Siyasa

Atiku da Obi sun musanta ganawa don yin takara tare a 2027

Atiku da Obi sun musanta ganawa don yin takara tare a 2027

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a 2023, Peter Obi, sun musanta jita-jitar cewa suna tattaunawa kan haɗa kai don tsayawa takara a zaɓen 2027. Wannan ya biyo bayan hotunan Atiku da Obi da aka gani suna tare yayin karin kumallo a gidan Atiku da ke Jihar Adamawa, wanda ya yaɗu a shafukan sada zumunta. Atiku ya wallafa bidiyon ganawar a shafinsa na X ranar Asabar, inda aka nuna su tare da wasu mutane suna zaune a teburin cin abinci. Mai magana da yawun Atiku, Paul Ibe, ya bayyana cewa…
Read More
Duk da shawarar Ganduje, Gwamnan Edo ya kafa kwamitin da zai binciki gwamnatin Obaseki

Duk da shawarar Ganduje, Gwamnan Edo ya kafa kwamitin da zai binciki gwamnatin Obaseki

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Edo, Sanata Monday Okpebolo, ya amince da kafa kwamitin tantance kadarorin jihar mai mutane 14, domin binciken gwamnatin tsohon gwamnan jihar Godwin Obaseki. Babban Sakataren Yaɗa Labarai na Gwamnan, Fred Itua ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi. Ya ce kwamitin wanda za a ƙaddamar da shi a ranar Talata 26 ga watan Nuwamba, 2024, a gidan gwamnati da ke birnin Benin, Dr Ernest Afolabi Umakhihe ne zai jagoranta. Sanarwar ta ƙara da cewa, "A ci gaba da shirin da gwamnan ya yi na ɗora jihar kan…
Read More
‘Yan majalisar wakilai na NNPP sun tsige Ali Madaki a matsayin mataimakin shugaban marasa rinjaye

‘Yan majalisar wakilai na NNPP sun tsige Ali Madaki a matsayin mataimakin shugaban marasa rinjaye

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja 'Yan majalisar wakilai 15 cikin 18 da aka zaɓa a Jam’iyyar NNPP a jihar Kano sun amince da tsige ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Dala, Ali Madaki, a matsayin mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar. A cikin wata takarda da Manhaja ta gani a ranar Litinin, 'yan majalisar da ba su amince da cire Madakin Gini ɗin ba su ne Alhassan Rurum na Rano/Kibiya/Bunkure da Abdullahi Sani na ƙaraye/Rogo. A cikin wata wasiƙa da aka aika zuwa ga shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajudeen, tare da haɗin gwiwar shugaban jam’iyyar NNPP da sakataren…
Read More
Abin dariya ne waɗanda ba ‘yan jam’iyya ba su sauke ni daga muƙamina – Madakin Gini

Abin dariya ne waɗanda ba ‘yan jam’iyya ba su sauke ni daga muƙamina – Madakin Gini

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar wakilai, Ali Madakin Gini ya bayyana cewa abin dariya ne a ce waɗanda ba 'yan jam'iyyar NNPP ba su yi yunƙurin cire shi daga muƙaminsa. A wata tattaunawa da jaridar Daily Nigerian, Madaki ya zargi jagoran NNPP na ƙasa, Rabi'u Kwankwaso da kitsa yunƙurin tsige shi da ga muƙamin na sa. A cewarsa, ya za a yi waɗanda shugabancin jam'iyya na ƙasa ya kora su samu ikon cire wani daga muƙaminsa, inda ya ƙara da cewa wani yunƙuri ne na wasu da su ke rawa da bazar Kwankwaso…
Read More
Ba ma goyon bayan Kawu Sumaila kan munanan kalamai wa shugaban jam’iyyar NNPP – KYD

Ba ma goyon bayan Kawu Sumaila kan munanan kalamai wa shugaban jam’iyyar NNPP – KYD

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Shugaban ƙungiyar Cigaban Matasa a Siyasar Kano, wato Kano Youth Democrat, Malam Aliyu  Sumaila ya yi tir da matakin rashin biyayya da Sanatan Kano ta Kudu ya ɗauka kan Shugaban Jam'iyyar NNPP na Kano, Hashimu Suleiman Dungurawa duk da cewa jagorancin jam'iyyar gaba yake da duk wani me riƙe da kujerar siyasa a ƙasa. Sumaila ya ce sun yi mamaki mutuƙar gaske ganin yadda Sanata Kawu Sumaila ya ke aibata shugaban jamiiyar NNPP a kafafen yaɗa labarai ganin cewa jam'iyya tana da damar ladabtar da duk wani ɗan ta da ya kauce daga manofofin tafiyarta.…
Read More
Tinubu da Buhari ne suka jefa Nijeriya cikin tsananin fatara da rashin tsaro – Obasanjo

Tinubu da Buhari ne suka jefa Nijeriya cikin tsananin fatara da rashin tsaro – Obasanjo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya bayyana Nijeriya a matsayin ƙasar da ta gaza sakamakon shugabancin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari da kuma Shugaba Bola Tinubu. Obasanjo ya ce, Tinubu da Buhari ne suka jefa Nijeriya cikin halin yunwa da rashin tsaro da rashin cigaba. Obasanjo na waɗannan kalamai ne a yayin taron tunawa da marigayi, Chinua Achebe da ake duk shekara domin tun wa da shi wanda aka yi a jami’ar Yale da ke Amurka. Tsohon shugaban ƙasar ya gabatar da wanj jawabi wanda aka naɗa, sannan aka kunna a wurin taron. Haka…
Read More
Babu rashin jituwa tsakani na da Badaru – Gwamna Namadi

Babu rashin jituwa tsakani na da Badaru – Gwamna Namadi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, a ranar Litinin, ya ce, ba zai bari shaci-faɗin mutane da ake yaɗawa cewa ba sa ga maciji da ministan tsaro, Muhammad Badaru, ya shafe shi ba. Badaru shi ne tsohon gwamnan jihar Jigawa wanda ya gama ya miƙa wa Namadi a shekarar 2023. Gwamnan Namadi ya ce ya yi mamakin yadda aka samu wasu -wasu bayan ya tafi hutun na ƙarshen shekara na kwanaki 18 – suna ƙoƙarin ƙulla gaba a jam’iyyarsu ta APC. Mai magana da yawun gwamnan, Hamisu Gumel, ne ya bayyana hakan, inda gwamnan ya…
Read More
Babu abin da zai girgiza tafiyar Kwankwasiyya a Dala – Alhaji Sani Baba 

Babu abin da zai girgiza tafiyar Kwankwasiyya a Dala – Alhaji Sani Baba 

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Alhaji Sani Baba, shugaban masu sayar da taki da sauran kayan amfanin gona na gidan Aminu ɗantatta a kasuwar Galadima, kuma shugaban NNPP na mazaɓar Dala, ya bayyana shugaban ƙaramar hukumar Dala, Hon. Suraj Imam da cewa mutum ne mai ƙoƙari da kowa ya san shi a haka. Ya bayyana hakan ne da yake zantawa da 'yan jarida a taron rantsar da kansiloli masu gafara da aka yi a sakatariyar mulki ta Dala. Ya ce kuma Allah ya taimaka ya kawo waɗanda za su yi aiki da shi jajirtattu matasa da aka ɗora kwarya a…
Read More
Ina gargaɗin Kwankwaso kan tsoma baki a rikicin masarautar Kano — Ata

Ina gargaɗin Kwankwaso kan tsoma baki a rikicin masarautar Kano — Ata

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sabon ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya gargaɗi jagoran Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso, da ya guji yin magana kan rikicin masarautar Kano. Ya yi gargaɗin cewa tsoma baki kan lamarin na iya ƙara rura wutar rabuwar kawuna a ƙasar nan. Hadimin ministan, Adamu Aminu Fagge, yunƙuri ne na “mulkin mallaka” a yankin Arewa. Ya ce, “Yanzu Legas ba za ta bari mu zaɓi sarki ba. Legas ta shiga tsakiyar Kano don kafa nasu sarkin.” A martaninsa, Minista Yusuf Abdullahi Ata ya yi nuni da cewa batun masarautar Kano yana gaban…
Read More
Zaɓen Ondo: Ɗan takarar PDP ya garzaya kotu

Zaɓen Ondo: Ɗan takarar PDP ya garzaya kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Ɗan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Jihar Ondo, Agboola Ajayi, ya yi watsi da sakamakon zaɓen da aka gudanar, inda ya ce zai ƙalubalanci sakamakon a kotu. Lucky Aiyedatiwa na jam’iyyar APC, aka ayyana a matsayin wanda ya lashe zaɓen da ƙuri’u 366,781, yayin da Ajayi ya samu ƙuri’u 117,845. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Ayo Fadaka, ya fitar, Ajayi ya ce zai tafi kotu domin ƙalubalantar rashin adalci a zaɓen. “Mun yi watsi da sakamakon zaɓen ranar 16 ga watan Nuwamba, kuma za mu ɗauki matakin shari’a don…
Read More