18
Apr
Ɗan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Sanata Kabiru Garba Marafa, ya ce ya amince ya sha kaye a hannun takwaransa na PDP, Hon. Ikira Aliyu Bilbis. A jawabinsa da aka yaɗa ranar Litinin, Marafa ya yi alƙawarin ba zai tafi kotu don ƙalubalantar sakamakon zaɓen ba. Saboda a cewarsa, zuwa kotu zai karkatar da hankalin zaɓaɓɓen sanatan daga barin yin aikin da ya kamata, wanda hakan kuwa zai shafi shiyyarsu. Ɗan siyasar ya yi amfani da wannan dama wajen yaba wa al'ummar Zamfara ta Tsakiya dangane da damar da suka ba shi ta zame musu wakili a…