Siyasa

Zan kawo wa Tinubu Kano kaf ɗinta a zaɓen 2027,  inji Minista Ata

Zan kawo wa Tinubu Kano kaf ɗinta a zaɓen 2027,  inji Minista Ata

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sabon ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi, ya sha alwashin tabbatar da nasarar jam’iyyar APC a zaɓen 2027. Ministan na wannan kalamai ne a yayin ganawarsa da manema labarai bayan dawowarsa Kano daga Abuja a ranar Lahadi. Ya yi alƙawarin jajircewa wajen yayata ayyukan da shugaba Tinubu ke yi na sabunta fatan ‘yan Nijeriya. Sannan ya jaddada aniyarsa ta cicciɓa aikin samar da gidajen da gwamnatin shugaba Tinubu ke yi tare da gode wa shugaban bisa karrama shi da wannan muƙami da ya yi. Ministan ya yi alƙawarin tabbatar da nasarar jami’iyyar…
Read More
Gawuna ya fi dacewa a bai wa muƙamin minista — Gwarzo

Gawuna ya fi dacewa a bai wa muƙamin minista — Gwarzo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Ministan Ma’aikatar Gidaje da Raya Birane, Abdullahi Gwarzo, ya ce ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaɓen 2023, Nasiru Yusuf Gawuna, ya fi dacewa a bai wa muƙamin minista maimakon Yusuf Ata. Gwarzo, ya ce kamata ya yi a bai wa ɗan takarar gwamnan Kano a zaɓen 2023, Nasiru Yusuf Gawuna matsayin nasa maimakon bai wa Yusuf Ata. “Idan an ware wannan muƙami ne don Kano ta Tsakiya ne, to Gawuna wanda ya yi takarar gwamna a 2023 wanda yake shugabanta a Kano ta Tsakiya, shi ya kamata a fara tunani. “Gawuna…
Read More
Zaɓen Ondo: Atiku ya gargaɗi INEC kan tafka maguɗin zaɓe

Zaɓen Ondo: Atiku ya gargaɗi INEC kan tafka maguɗin zaɓe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya buƙaci ‘ya’yan jam’iyyar PDP a Jihar Ondo, su haɗa kai don samun nasara a zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar a ranar Asabar. A wata sanarwa daga mai ba shi shawara kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, Atiku ya yaba wa ɗan takarar PDP, Agboola Ajayi, a matsayin gogaggen ɗan siyasa wanda zai iya jagorantar jam’iyyar zuwa ga nasara da kuma inganta rayuwar al’ummar jihar. Atiku, wanda ya tsaya takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya kuma gargaɗi Hukumar Zaɓe Mai Zaman…
Read More
Zaɓen ƙananan hukumomin Zamfara: An samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a

Zaɓen ƙananan hukumomin Zamfara: An samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Zaɓen kansilolin ƙananan hukumomin da ke gudana yau a Jihar Zamfara an samu ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a a Gusau babban birnin jihar. Matsalar ta faru ne yayin da aka samu jinkirin rarraba kayan zaɓe a sassa daban-daban na mazaɓu a babban birnin jihar. Wakilinmu ya ruwaito cewa wasu daga cikin rumfunan zaɓe da aka ziyarta ba kowa, yayin da jama’a suka fita harkokinsu na yau da kullum. Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar ZASIEC ta shirya da ƙarfe 8:00 na safe domin fara zaɓen amma har rumfar zaɓe da gwamna Dauda Lawal ya…
Read More
Shettima ya yi kira ga mutanen Ondo su sake zaɓen Aiyedatiwa

Shettima ya yi kira ga mutanen Ondo su sake zaɓen Aiyedatiwa

Daga USMAN KAROFI Mataimakin Shugaban Ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya yi kira ga mutanen Jihar Ondo da su sake zaɓen Gwamna Lucky Aiyedatiwa tare da mataimakinsa, Dr. Olayide Adelami a zaɓen gwamna da za a yi ranar Asabar mai zuwa. Shettima ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa, idan aka sake zaɓen Aiyedatiwa jihar za ta ƙara samun ci gaba, zaman lafiya da wadata. Sanata Shettima ya yi wannan kiran ne a wajen taron kammala yaƙin neman zaɓen jam'iyyar APC da aka yi a filin dimokraɗiyya na MKO Abiola a Akure inda ya ce zaɓen gwamna Aiyedatiwa ba kawai na neman…
Read More
Ƙungiyar Matasan APC sun yaba wa Tinubu kan sakin yara masu zanga-zanga

Ƙungiyar Matasan APC sun yaba wa Tinubu kan sakin yara masu zanga-zanga

Daga IBRAHIM MUHAMMAD Wata ƙungiyar ta matasa mai suna 'APC Arewa Youths Merger Group' ta yaba wa shugaban ƙasa Ahmad Bola Tunubu bisa karɓar  ƙorafinsu da kira da suka yi masa akan ya sa a saki yara da aka tsare akan zanga-zanga cikin awa 48. A cikin wata takardar sanarwa dake ɗauke da sa hannun jagoran Matasa na APC Arewa merger group  Hon Musa Mujahid Zantawa aka raba wa manema labarai yace sun yi matuƙar jin daɗi da  farin ciki da yafe wa yaran da shugaban ƙasa ya yi bayan amsa kira da sukayi masa ya kuma miƙa su hannun…
Read More
PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi a Kuros Riba, ta garzaya kotu

PDP ta yi watsi da sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi a Kuros Riba, ta garzaya kotu

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam’iyyar PDP reshen Kuros Riba, ta ce zaɓukan ƙananan hukumomin da aka gudanar a ranar Asabar a jihar ya gaza kan kowane ma’auni da za a kira zaɓe. Daga bisani jam'iyyar ta yi watsi da sakamakon sannan ta ce za ta ƙalubalanci sakamakon a gaban kotun da ta dace. Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da shugaban jam’iyyar PDP na jihar, ɓenatius Ikem ya fitar a birnin Kalaba ranar Litinin. Mista Ikem ya bayyana abin da ya faru a matsayin wani shiri na maguɗin da aka tsara wanda ya haɗa da karkatar da…
Read More
Rikici na neman ɓarkewa tsakanin Kwankwaso da Abba bayan da gwamnan ya daina ɗaga wayar maigidansa

Rikici na neman ɓarkewa tsakanin Kwankwaso da Abba bayan da gwamnan ya daina ɗaga wayar maigidansa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Rikicin da ke cikin Jam'iyyar NNPP mai mulki a Kano na neman ƙazancewa, inda gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya fara ƙin daga wayar mai gidansa Rabi'u Musa Kwankwaso sannan ya ƙi halartar tarukan da jagoran NNPP din na ƙasa ya shirya. Da alama dai wannan taken na "Abba tsaya da ƙafar ka" ya fara tasiri a gurin gwamnan bayan da wasu ke ta motsa yadda zai karɓe iko da jam'iyyar da kuma Kwankwasiyya daga hannun Kwankwaso. Wasu majiyoyi sun shaidawa Manhaja cewa tuni Abba ya fara amsa kira bayan da "aka nusar da…
Read More
APC ta dakatar da tsohon Ministan Buhari Aregbesola

APC ta dakatar da tsohon Ministan Buhari Aregbesola

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jam'iyyar APC, reshen jihar Osun ya dakatar da Rauf Aregbesola, tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, saboda zargin ayyukan da suka saɓa wa jam’iyya. Dakatarwar ta na ɗauke ne a cikin wata wasiƙa da Tajudeen Lawal da Alao Kamoru, shugaban jam’iyyar da sakatarensa, suka sanya wa hannu. An aika wasiƙar zuwa ga shugaban jam'iyyar na ƙasa, Abdullahi Ganduje, tare da kwafin ta da aka bai wa manema labarai ranar Talata a birnin Osogbo. A cewar wasiƙar, dakatarwar Aregbesola ta biyo bayan zargin ayyukan da suka saɓa wa jam’iyya da kwamitin zartarwa na jam’iyyar na ƙaramar…
Read More
Muna farin cikin zaɓen Shugaban ƙaramar Hukumar Fagge da kansiloli cikin kwanciyar hankali – Sule Chamba

Muna farin cikin zaɓen Shugaban ƙaramar Hukumar Fagge da kansiloli cikin kwanciyar hankali – Sule Chamba

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Shugaban Jam'iyyar NNPP na ƙaramar Hukumar Fagge, Hon. Sulaiman Muhammad Chamba ya bayyana cewa sun yi matuƙar farin cikin da zaɓen Shugaban ƙaramar Hukumar Fagge da kansilolin da ya gudanar Asabar ɗin da ta gabata a Kano. Sulaiman Chamba ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da 'yan jarida a yayin rantsar da mataimakin shugaban ƙaramar hukumar Fagge da zaɓɓaɓɓun kansilolin yankin da aka zaɓa. Ya ce suna yi wa jama'a da suka taimaka wajen samun wannan nasara su kuma waɗanda Allah ya bai wa nasara na muƙamai Allah ya ba su dama da…
Read More