Siyasa

Sanata Marafa ya amince da shan kaye, ya ce babu batun zuwa kotu

Sanata Marafa ya amince da shan kaye, ya ce babu batun zuwa kotu

Ɗan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Sanata Kabiru Garba Marafa, ya ce ya amince ya sha kaye a hannun takwaransa na PDP, Hon. Ikira Aliyu Bilbis. A jawabinsa da aka yaɗa ranar Litinin, Marafa ya yi alƙawarin ba zai tafi kotu don ƙalubalantar sakamakon zaɓen ba. Saboda a cewarsa, zuwa kotu zai karkatar da hankalin zaɓaɓɓen sanatan daga barin yin aikin da ya kamata, wanda hakan kuwa zai shafi shiyyarsu. Ɗan siyasar ya yi amfani da wannan dama wajen yaba wa al'ummar Zamfara ta Tsakiya dangane da damar da suka ba shi ta zame musu wakili a…
Read More
Sanata Binani ta garzaya kotu neman adalci

Sanata Binani ta garzaya kotu neman adalci

'Yar takarar gwamna ta Jam'iyyar APC a Jihar Adamawa, Sanata Aisha Binani Dahiru, ta garzaya kotu don neman a yi mata adalci a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamna a jihar. Aisha ta tafi Babbar Kotu a Abuja ne inda ta shigar da ƙarar neman kotu ta dakatar da matakin da Hukumar Zaɓe, INEC, ta ɗauka na soke bayyana ta a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamnan Adamawa bayan zaɓen da ya gudana ranar 18 ga Maris wanda aka kammala ran 15 ga Afrilu. Kazalika, Sanata Binani na neman kotu ta hana INEC ɗaukar wani mataki na gaba dangane da…
Read More
Nasiru Idris ya zama Gwamna mai jiran gado a Kebbi

Nasiru Idris ya zama Gwamna mai jiran gado a Kebbi

Ɗan takarar gwamna na Jam'iyyar APC a Jihar Kebbi, Nasiru Idris, ya zama sabon zaɓaɓɓen Gwamnan jihar. A ranar Lahadi INEC ta bayyana Idris a matsayin wanda ya lashen zaɓen gwamnan jihar bayan kammala zaɓen gwamnan jihar a ranar Asabar da ta gabata. Ya lashe zaɓen ne bayan da ya doke abokin hamayyarsa na Jam'iyyar PDP, Maj-Gen. Aminu Bande (mai ritaya).
Read More
Bilbis ya zama Sanatan Zamfara ta Tsakiya

Bilbis ya zama Sanatan Zamfara ta Tsakiya

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta bayyana ɗan takarar Sanatan Zamfara ta Tsakiya ƙarƙashin Jam'iyyar PDP, Ikra Aliyu Bilbis, a matsayin wanda ya lashe zaɓen sanata a yankin a zaɓen cike giɓin da da ya gudana Asabar da ta gabata. INEC ta ce Bilbis ya lashe zaɓen ne bayan da ya samu mafiyawan ƙuri'u 102, 866 wanda hakan ya ba shi damar doke abokin hamayyarsa na Jam'iyyar APC, Sanata Kabiru Garba Marafa, wandavya tsira da ƙuri'u 91, 216. Farfesa Kabiru Abdullahi na Jami'ar Tarayya da ke Gusau, shi ne ya kasance Baturen zaɓen da ya bayyana sakamakon zaɓen.
Read More
Sakkwato ta Arewa: Sanata Wamakko ya yi ta-zarce

Sakkwato ta Arewa: Sanata Wamakko ya yi ta-zarce

Sanata Aliyu Magatakarda Wamakko na Jam'iyyar APC ya sake lashe zaɓen sanatan Sakkwato ta Arewa. Wamakko ya samu nasarar ce a zaɓen cike giɓin da INEC ta gudanar a ranar Asabar inda ya samu ƙuri'u 141,468. Abokin hamayyarsa na Jam'iyyar PDP, Dan’iya Manir Muhammad ne ya zama na biyu da ƙuri'a 118,445. Farfesa Ibrahim Magawata shi ne Baturen Zaɓen da ya bayyana sakamakon zaɓen da aka gudanar a rumfunan zaɓe 185.
Read More
Tambuwal ya sha da ƙyar a takarar Sanatan Sakkwato ta Kudu

Tambuwal ya sha da ƙyar a takarar Sanatan Sakkwato ta Kudu

Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Gwamnan Jihar Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal, ya yi nasarar lashe kujerar Sanatan Sakkwato ta Kudu da ya nema. Baturen zaɓen yankin, Farfesa Abubakar Abdullahi Bagudo, shi ne ya sanar da nasarar Tambuwal inda ya ce ya samu ƙuri'u 100,860 wanda hakan ya ba shi damar doke abokin karawarsa na APC, Sanata Ibrahim Abdullahi Danbaba wanda ya tsira da ƙuri'u 97,884. Nasarar Tambuwal ɗin dai na zuwa ne bayan da zaɓen kujerar ya kasance wanda bai kammalu ba a zaɓen yayin zaɓen 'yan Majalisar Tarayya da aka gudanar ran 18 ga watan Maris ɗin da ya…
Read More
Hedikwatar INEC ta ƙi amincewa da bayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamnan Adamawa

Hedikwatar INEC ta ƙi amincewa da bayyana Binani a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamnan Adamawa

*Ta ba da umarnin dakatar da ci gaba da tattara sakamakon zaɓe Babban Ofishin Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ya dakatar ta ci gaba da tattara sakamakon zaɓen cike giɓi na Gwamnan Jihar Adamawa da ya gudana ranar Asabar. Ofishin ya ɗauki wannan mataki ne bayan da labarin ayyana 'yar takarar Jam'iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru (Binani) a matsayin wadda ta lashe zaɓe da Kwamishinan Zaɓe na jihar, Farfesa Hudu Yunus Ari, ya yi a ranar Lahadi ya isa gare shi. Cikin sanarwar da INEC ta wallafa a shafinta na Tiwita mai ɗauke da sa hannun Kwamishinan hukumar, Barista Festus…
Read More
Sanata Binani ta ɗaɗa Gwamna Fintiri da ƙasa a Adamawa

Sanata Binani ta ɗaɗa Gwamna Fintiri da ƙasa a Adamawa

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, ta ayyana Sanata Aisha Dahiru (Binani) a matsayin wadda ta lashe zaɓen Gwamnan Jihar Adamawa. Kwamshinan Zaɓe na Jihar Adamwa, Farfesa Hudu Yunus Ari, shi ne ya bayyana nasarar Binani wadda ta kasance 'yar takarar Jam'iyyar APC. Da fari, Gwamna Ahmadu Fintiri na Jam'iyyar PDP ne ke gaba da yawan ƙuri'u kafin daga bisani Binani ta shige gabansa. Magoya bayan jam'iyyar PDP sun nuna rashin jin daɗinsu ganin Kwamishinan Zaɓe na jihar ne ya bayyana sakamakon zaɓen maimakon Baturen Zaɓe. Da wannan nasarar da ta samu, a iya cewa Sanata Aisha ta zamo mace ta…
Read More
Zaɓen cike giɓi: NNPP ta lallasa APC a Fagge

Zaɓen cike giɓi: NNPP ta lallasa APC a Fagge

Daga BASHIR ISAH Ɗan takarar Jam'iyyar NNPP, Barista MB. Shehu, ya lashe zaɓen ɗan Majalisar Wakilai na ƙaramar hukumar Fagge a Jihar Kano. Nasarar da MB Shehu ya samu ta kawo ƙarshen ɗan majalisa mai wakiltar shiyyar a Majalisar Wakilai, Aminu Sulaiman Goro na Jam'iyyar APC wanda ke kan wa'adinsa na uku a Majalisar. Da yake bayyana sakamakon zaɓen, Baturen zaɓen Ibrahim Tajo Suraj, ya ce MB Shehu ya samu ƙuri'u 19,024 daga jimillar ƙuri'un da aka kaɗa, yayin da ɗan takarar Jam'iyyar Labour, Shuaibu Abubakar ya rufa masa baya da ƙuri'u 12,789. Sakamakon zaɓen ya nuna Aminu Sulaiman Goro…
Read More