Siyasa

Abin da ya sa ba a rantsar da shugaban ƙaramar Kumbotso na Kano ba

Abin da ya sa ba a rantsar da shugaban ƙaramar Kumbotso na Kano ba

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano A jihar Kano, har yanzu tsugune ba ta ƙare ba, duk da kammala zaɓen ƙananan hukumomi tare da rantsar da sabbin shugabannin, saboda rikicin shari’a. Hukumar zaɓen Kano ta ce jam’iyyar NNPP ce ta lashe duk shugannin ƙananan hukumomi 44 da kansiloli 484, to sai dai har yanzu ba a rantsar da shugaban ƙaramar hukumar Kumbotso ba. Daya daga cikin 'yan takarar kujerar ne ya garzaya babbar kotun jihar saboda sauya sunansa da wani, abin da ya sa kotu ta yi hukuncin da ake ganin shi ne ya hana rantsar da sabon shugaban. Ana gobe…
Read More
PRP reshen Katsina za ta maka Gwamnatin Tarayya a kotu kan matsalar lantarki a Arewa

PRP reshen Katsina za ta maka Gwamnatin Tarayya a kotu kan matsalar lantarki a Arewa

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Tsohon ɗan takarar gwamna a jam’iyar PRP, a Jihar Katsina, Alhaji Imrana Jabiru Jino ya ce zai maka Gwamnatin Tarayya a kotu kan tsawon kwanakin da aka ɗauka ba wutar lantarki a Arewacin Nijeriya. Ya ce ya shirya tattara bayanai tare da aika su ta yanar gizo ga duk iyalan mutanen da suka rasa rayukansu da dukiyoyinsu sanadiyyar ɗaukewar wutar lantarki. Jino ya koka kan yadda manyan kamfanoni da ƙananan 'yan kasuwa suka tafka asara sanadiyyar rashin wutar lantarki. “ƙananan 'yan kasuwa da suka haɗa da masu walda, aski, sayar da kayan sanyi da sauransu…
Read More
Akwai yiwuwar ƙulla gagarimar maja a zaɓen 2027 a Nijeriya – NNPP

Akwai yiwuwar ƙulla gagarimar maja a zaɓen 2027 a Nijeriya – NNPP

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Jam’iyyar NNPP na ƙasa, Ajuri Ahmed, ya nuna akwai yiwuwar ƙulla gagagrimar maja da wasu jam’iyyun siyasar Nijeriya domin tunkarar zaɓen 2027 domin kawo ƙarshen mulkin Shugaba Tinubu. Ahmad ya bayyana hakan ne a Akuren jihar Ondo a ranar Alhamis a yayin yaƙin neman zaɓen gwamnan jihar da za a yi a ranar 16 ga watan Nuwamba mai zuwa. Ya ce akwai tattaunawa game da yadda za a kawo ƙarshen mulkin jam’iyyar APC a zaɓen 2027. Sai dai bai bayyana sunayen jam’iyyun da ake kan tattauna da su, inda ya ce idan aka…
Read More
Lokacin da nake mulki na bai wa tsaro muhimmanci – Obasanjo

Lokacin da nake mulki na bai wa tsaro muhimmanci – Obasanjo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya nemi Gwamnatin Tarayya ta gaggauta magance matsalar rashin tsaro da ke ƙara yadɗuwa a faɗin ƙasar. Obasanjo ya yi magana a ranar Lahadi a fadar Rilwanu Suleiman-Adamu, Sarkin Bauchi. Tsohon janar na sojan ya je Bauchi ne domin ƙaddamar da ayyukan tituna da gwamnan jihar, Bala Mohammed, ya gina. Obasanjo ya ce yanayin tsaro a Nijeriya a yau yana da matuƙar “matsala”, yana mai cewa gwamnatinsa ta bai wa tsaron rayuka da dukiyoyi fifiko. "Irin tsaron da ya fi dacewa shi ne  na al'umma domin kowa ya san…
Read More
Samun mutum mai nagarta a yanzu yana matuƙar wahala – Osinbajo

Samun mutum mai nagarta a yanzu yana matuƙar wahala – Osinbajo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Mataimakin Shugaban ƙasa, Yemi Osinbajo, ya ce yanzu abu ne mai  wahala samun mutane masu nagarta. Farfesa Osinbajo ya bayyana hakan a wajen bikin ɗaukar sabbin ɗaliban shekarar 2024 na Jami’ar Miɓa Open a Abuja, a ranar Asabar. Yayin da yake kare Jami'ar, wanda ya bayyana a matsayin makomar kawo ingantacciyar ilimin gaba da sakandare a Afirka, ya ce ba za a iya isar da ingantaccen ilimi a Afirka ba ga yawancin masu sha'awar samun digirin jami’a idan za a ci gaba da gina jami’o’in gargajiya domin ɗaukar su. Ya ce: “Kowace shekara,…
Read More
Rikici ya kunno kai a cikin Jam’iyyar NNPP a Kano 

Rikici ya kunno kai a cikin Jam’iyyar NNPP a Kano 

Daga RABIU SANUSI a Kano Jam’iyyar NNPP ta Jihar Kano ta faɗa cikin rikici, inda har ta kai ga dakatar da Sakataren Gwamnatin Jihar Dakta Abdullahi Baffa Bichi, da Kwamishinan Sufuri na jihar Kano Muhammad Diggwal, daga cikin jam’iyyar. Shugaban Jam’iyyar NNPP a Kano Dakta Hashim Sulaiman Dungurawa ne ya bayyana hakan ta cikin wani saƙon murya da aka aikowa Dala FM Kano, a cikin daren Litinin. Hashim Dungurawa, ya ce dakatar da ƙusoshin gwamnatin jihar Kanon su biyu,ya biyo bayan zargin keta alfarmar jagoranci, da ta Jam’iyya, da kuma keta alfarmar gwamnati, a don haka ne suka ɗauki matakin…
Read More
Me ya sa ‘yan siyasa ke sauya sheƙa tun zaɓe bai ƙarato ba?

Me ya sa ‘yan siyasa ke sauya sheƙa tun zaɓe bai ƙarato ba?

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Kasa da shekara ɗaya da rabi da kama aikin sabuwar gwamnati, sauya sheƙa da 'yan siyasa ke yi daga wannan jam'iyya zuwa waccan ya zama ruwan dare. Al'amarin dai ya fi ƙamari tsakanin jam'iyya mai mulki ta APC da na adawa musamman PDP da NNPP da kuma LP. Ko a ƙarshen makon nan sai da wasu ɗaruruwan 'yan jam'iyyar APC a jihar Kano suka sanar da ficewa daga jam'iyyar zuwa jam'iyya mai mulki ta NNPP. Sai dai kafin nan sai da wasu 'ya'yan jam'iyyar ta NNPP suka fice zuwa jam'iyyar APC. Ko a jihar…
Read More
Haɗakar NNPP da LP: Ba a fahimci maganganun Kwankwaso ba – Buba Galadima

Haɗakar NNPP da LP: Ba a fahimci maganganun Kwankwaso ba – Buba Galadima

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tun bayan fitar wani bidiyo da aka ga tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, yana hira da 'yan jarida a jihar kafafen sada zumunta da ma jaridun Nijeriya suka fara rawaito cewa tsohon gwamnan ya amince ya zama mataimakin Peter Obi a takarar shugaban ƙasa ta 2027. A 2023 Peter Obi, wanda tsohon gwamnan jihar Anambra ne da ke kudancin ƙasar, ya yi takarar shugaban ƙasa ƙarƙashin jam'iyyar Labour Party (LP), bayan da ya fice daga jam'iyyar PDP inda ya yi wa Atiku Abubakar na jam'iyyar adawa ta PDP mataimakin ɗantakara a…
Read More
Tsagin jam’iyyar PDP sun naɗa Yayari Ahmed a matsayin shugaban riƙon ƙwarya

Tsagin jam’iyyar PDP sun naɗa Yayari Ahmed a matsayin shugaban riƙon ƙwarya

Jam'iyyar PDP ta naɗa Ahmed Yayari wanda shine ma'ajin jam'iyyar a matsayin sabon shugaban ta na riƙon ƙwarya bayan dakatar da Umar Damagun da wani tsagin kwamitin gudnarwar jam'iyyar ya yi. Sanarwa ta fito a wata takarda wadda sakataren jam'iyyar Hon. Debo Ologunagba ya sanya wa hannu a ranar Juma’a a Abuja. Sanarwar ta bayyana Yayari Ahmed a matsayin sabon shugaban riƙon ƙwarya kamar yadda kundin tsarin mulkin jam'iyyar ya bada damar yin hakan. Kwamitin ya roƙi mambobi da su haɗe kansu kuma su maida hankali ga taron kwamitin gudanarwa da ake sa ran za ayi 24 ga watan Oktoba…
Read More
Atiku ya yaba wa mutanen Ribas da Fubara kan yadda suka bijire wa barazana

Atiku ya yaba wa mutanen Ribas da Fubara kan yadda suka bijire wa barazana

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya yabawa mutanen Jihar Ribas da gwamna Similaye Fubara bisa jajircewa da kuma bijire wa tsangwama a zaɓen ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar Asabar. Atikun yayi wannan jawabin ne a shafin sada zumunta na X. Ya bayyana gamsuwarsa da yanayin yadda aka gudanar da zaɓen. Yayi matuƙar farin ciki da kyara da tsangwama bai hana mutane fitowa su yi zaɓe ba. Ya ƙara yabawa da irin jajircewa da mutanen Ribas su ka yi na ganin zalunci da siyasar uban gida bai yi tasiri ba. Daga ƙarshe ya sake yabawa gwamna Fubara yadda…
Read More