Nishadi

Manyan ’yan siyasa sun kira ni sanadin maganata, inji Adam Zango

Manyan ’yan siyasa sun kira ni sanadin maganata, inji Adam Zango

Daga AISHA ASAS A satuka buyu da suka gabata, fitaccen jarumi a Masa’antar Kannywood, Adam A. Zango ya bayyana a kafar sada zumunta na TikTok da bayyanai da za mu iya kira da tura ta kai bango, duk da cewa wasu da yawa na kallon faifan bidiyon na Zango a matsayin ishara ga abinda zai iya faruwa da shi nan gaba idan ba a ɗauki mataki ba, wanda wannan tunanin ne ya sa hankullan masoyan jarumin suka ta shi, yayin da suka shiga aika masa da saƙon nuna soyayya da goyon baya gare shi. Jarumi Adam ya nuna takaicinsa ta…
Read More
Me ya jawo mutuwar auren G-Fresh da Sadiya Haruna? 

Me ya jawo mutuwar auren G-Fresh da Sadiya Haruna? 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Tun bayan da jarumar Tiktok ɗin nan, kuma tsohuwar matar G-Fresh Al-Ameen, Sayyida Sadiya Haruna ta fitar da sanarwar cewa, aurenta da tsohon mijinta Abubakar Ibrahim (G-Fresh Al-Ameen) ya zo ƙarshe, sakamakon biyansa kuɗi Naira dubu 500 da ta yi, mutane ke ta tofa albarkacin bakinsu. Daga masu cewa dama mun san a rina, wai an saci zanin mahaukaciya, sai masu cewa gara ma haka, an sayar da gonar rago an saya mai fura!  Za ku iya tunawa tun da sanyin safiyar wata ranar 16 ga Yuni na shekarar 2023 ne zaurukan sada zumunta suka wayi…
Read More
Kotu ta umurci Jaruma Halima Abubakar da ta biya Apostle Suleman tarar miliyan 10

Kotu ta umurci Jaruma Halima Abubakar da ta biya Apostle Suleman tarar miliyan 10

Daga AISHA ASAS Babbar Kotun Tarayya ta umurci jaruma a masana’antar Nollywood Halima Abubakar da ta biya tarar Naira miliyan 10 ga Apostle Johnson Suleman kan kalaman ɓata suna da ta yi a shafinta na Instagram. Baya ga haka, kotun ta haramtawa jarumar yin kowanne irin kalamai kan faston. Suleman ya zargi jarumar da wallafa kalaman cin zarafi gare shi ciki kuwa har da kiransa da mutumin banza da kuma mabiɗi mata. Duk da cewa kotun ta ba wa jaruma Halima damar kare kanta tare da bayar da hujjar da za ta wanke ta daga zargin na limamin Cocin, sai…
Read More
Ƙungiyar matasa ta naɗa Ado Ahmad muƙamin ‘Sarkin Mawallafan Arewa’

Ƙungiyar matasa ta naɗa Ado Ahmad muƙamin ‘Sarkin Mawallafan Arewa’

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Arewa Youth And Women For Change ta naɗa shahararren marubucin nan, Alhaji Ado Ahmad Gidan Dabino MON, daga Jihar Kano a matsayin 'Sarkin Mawallafan Arewa na Farko' kuma 'Jakadan Zaman Lafiyar Arewa'. Bayanin naɗin na ƙunshe ne cikin sanarwar da ƙungiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun Babbar Sakatariyar Ƙungiyar, Ambasada Sadiya Ahmed Birniwa. Ƙungiyar ta ce ta naɗa Ado wannan muƙamin ne duba da irin gudunmawar da yake bayarwa ga cigaban al'umma, musamman ga rayuwar mata da matasa. Ta ƙara da cewa, sai da ta yi nazari mai zurfi tare da tantance wasu ɗaiɗaikun…
Read More
Sau uku ina kama matata da aikata baɗala — Zango

Sau uku ina kama matata da aikata baɗala — Zango

Daga BASHIR ISAH Jarumi a masana'antar Kannywood, Adam A. Zango, ya bayyana cewa sau uku yana kama matarsa da aikata baɗala, amma duk da haka ya yi haƙuri ya ci gaba da zama da ita. An ji jarumin ya bayyana haka ne a cikin wani faifan bidiyo.mai tsawo da aka yaɗa a soshiyal midiya. A cikin bidiyon, jarumin ya taɓo batutuwa da dama, daga ciki har da yadda wasu abokan sana'arsa waɗanda ya taɓa bai wa gudunmawa a rayuwa ba sa ba shi kariya ga mutuncinsa da kuma irin rashin haɗin kan da ke Kannywood. Haka nan, Jarumin ya taɓo…
Read More
‘….Mu taimaka wa Adam Zango da soyayya a halin da yake ciki’

‘….Mu taimaka wa Adam Zango da soyayya a halin da yake ciki’

Daga FAUZIYYA D. SULAMAIN Ban taɓa magana a kan wani ɗan fim ba, amma halin da Adam Zango ke ciki yana buƙatar mu nuna masa soyayya irin ta addini. Yana buƙatar mu ja shi a jiki, abubuwan da ya ke yi a yanzu akwai damuwa. Don Allah a samu waɗanda za su je kusa da shi don Allah, komai zai iya faruwa da shi, domin a yanzu yana ruguza gidansa da rayuwar yaransa da danginsa da 'yan'uwansa. Amma don Allah mu ja shi a jiki, kar mu ji haushinsa yana buƙatar kulawar duk wani musulmi hakan zai dawo da shi…
Read More
Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Tinubu ya nuna alhini kan rasuwar Saratu Giɗaɗo

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya nuna alhininsa dangane da rasuwar jaruma a masana'antar shirya finafinai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi dani da Daso. Hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Afrilu da kuma sa hannun mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Ajuri Ngelale. Tinubu ya yi amfani da wannan dama wajen miƙa ta'aziyya ga 'yan uwan da abobakan aiki da masoyan marigayiyar da ke sassa daban-daban. Tinubu ya bayyana rasuwar jarumar mai shekara 56 a matsayin babban rashi ga ƙasa baki ɗaya. Ya…
Read More
Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Na samu rufin asiri a sana’ar rubuta finafinai – Yahaya S. Kaya

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Yahaya S. Kaya fasihin marubucin labarin fim ne, da ya rubuta finafinai fiye da 20 a masana'antar fim ta Kannywood. A tattaunawasa da Ibrahim Hamisu a Kano za ku ji cikakken tarihinsa da kuma irin nasarorin da ya samu cikin shekaru 8 da shigar sa Kannywood, ku biyo mu: MANHAJA: Ka gabatar mana da kanka? YAHAYA S. KAYA: Sunana Yahaya S Kaya. Ni marubuci ne, ina rubutun littafi, ina na film. Ko za ka ba mu taƙaitaccen tarihinka? An haife ni a Garin Zariya, a shekarar 1996, na ta so a garin Zariya, anan na…
Read More
Sani Muazu ya nuna kaɗuwarsa kan rasuwar Daso

Sani Muazu ya nuna kaɗuwarsa kan rasuwar Daso

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kwamitin Amintattu na Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Nijeriya (MOPPAN), Sani Muazu, ya bayyana alhini da kaɗuwarsa dangane da rasuwar jarumar Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka fi sani da Daso. Ya bayyana haka ne cikin bayanin da ya fitar dangane da rasuwar marigayiyar a ranar Talata. Ya ce, “Cike da alhini na bi sahun ‘yan uwa wajen sanar da rasuwar ɗaya daga cikin fitattun jaruman Kannywood, Hajiya Saratu Giɗaɗo, wacce masoyanta suka fi kira da Daso. “Rasuwarta ta zo da kaɗuwa saboda ƙalau take ba ta fama da wani rashin lafiya. Cikin ƙoshin lafiya ta…
Read More
Masu harkar DJ sun koka kan haramta musu sana’a a Katsina

Masu harkar DJ sun koka kan haramta musu sana’a a Katsina

Daga UMAR GARBA a Katsina Ƙungiyar masu kiɗan DJ reshen jihar Katsina, ta koka dangane da hana sana'ar a faɗin jihar. Shugaban ƙungiyar a jihar, Hassan Mamman, ya bayyana irin halin da mambobin ƙungiyar za su shiga bayan da hukumar Hisba ta jihar Katsina ta hana gudanar da sana'ar. Ƙungiyar ta bayyana damuwwarta a wani taro da ta kira don wayar wa al'umma da kuma hukumar Hisba ta jihar kai game da yadda mambobinta suke tafiyar da sana'ar DJ a jihar. A cewar shugaban ƙungiyar sun ɗauki harkar DJ a matsayin sana'a, ba suna yi ba ne don ɓata tarbiyyar…
Read More