Nishadi

Fitattun taurarin da suka yi ridda: Mene ne alaƙar dake tsakanin fitattun mutanen da suka bar Musulunci?

Fitattun taurarin da suka yi ridda: Mene ne alaƙar dake tsakanin fitattun mutanen da suka bar Musulunci?

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A makon da ya gabata, mun kawo sunaye da bayanai na wasu fitattun taurari 'yan Nijeriya da suka fito daga gidajen Musulunci amma daga baya suka bayyana rungumar addinin Kiristanci. Sunayen da suka fito a rahoton sun haɗa da taurarin TikTok, mawaƙa, jaruman fina-finai da kuma wasu daga cikin mashahuran masu tasiri a kafafen sada zumunci. Kowane daga cikinsu ya bayar da nasa dalilin na barin addinin Musulunci, lamarin da ya haifar da ce-ce-kuce a tsakanin mabiya da masoyansu na daga addinan biyu. Saidai bayan hanayniyar ra'ayoyi da kuma martani, akwai tambayar…
Read More
Fitattun taurarin da suka yi ridda zuwa Kiristanci a Nijeriya

Fitattun taurarin da suka yi ridda zuwa Kiristanci a Nijeriya

Daga AISHA ASAS  A Najeriya, addini ba kawai wata al’ada ba ce ko wani ɓangare na rayuwar yau da kullum. Wani ginshiƙi ne da ke taka muhimmiyar rawa wajen gina mutumtaka, al’adu da yadda jama’a ke kallon mutum. Wannan dalili ne ya sa duk wani canjin addini da ya shafi fitattun mutane ke zama abin jan hankali da muhawara cikin al’umma. A masana’antar nishaɗi ta Najeriya, inda rayuwar fitattun mutane ke ƙarƙashin hasken jama’a a kowane lokaci, sauya addini na ɗaya daga cikin batutuwan da kan tayar da ƙura. Yayin da da dama daga cikin mashahuran mutane ke ci gaba…
Read More
Yadda shirin ‘Kannywood Abba Care’ ya buɗe ƙofar kula da lafiyar masu finafinan Hausa 

Yadda shirin ‘Kannywood Abba Care’ ya buɗe ƙofar kula da lafiyar masu finafinan Hausa 

Daga AISHA ASAS  A tsawon shekaru, ɗaya daga cikin manyan ƙalubalen da suka daɗe suna addabar masana'antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood shine yayata matsalar kula da lafiyar masu ruwa da tsaki a cikinta. Duk da irin gudunmawar da masana'antar ke bayarwa wajen nishaɗantarwa da bunƙasa al'adu, an sha ganin fitattun jarumai, mawaƙa da sauran masu sana'o'in da suke da alaƙa da sana’ar suna fuskantar matsalolin rashin lafiya ba tare da samun isasshen tallafi ba. Sai dai a wani sabon yanayi da ya jawo farin ciki a tsakanin zukatan masu harkar, an bayyana wani shiri da ake ganin zai kawo…
Read More
Rasuwar Tauraruwa Wasila ta kawo jimami da muhawara kan rayuwar aurenta da Jarumi Ciroma

Rasuwar Tauraruwa Wasila ta kawo jimami da muhawara kan rayuwar aurenta da Jarumi Ciroma

Daga AISHA ASAS  Masu hikima kan ce, “Allah Ya raba mu da ranar yabo.” Ba wai yabo ba ne ake gudu, illa dai saboda galibi ranar da mutum ya fi samun yabo ita ce ranar da ya riga ya bar duniya ko kuma ya bar wajen da maganar tasa ta taso. A lokacin da mutum yake raye, mutane kan yi saurin ganin kuskurensa, su yi masa hukunci, su zarge shi, ko ma su ɗora masa laifukan da ba a tabbatar da su ba. Amma da zarar mutuwa ta auku, zuciyoyi kan fara narkewa, harsuna su fara sassautawa, mutane kuma su…
Read More
An buƙaci gwamnati ta tallafa wa fannin kiɗa don bunƙasa tattalin arziki

An buƙaci gwamnati ta tallafa wa fannin kiɗa don bunƙasa tattalin arziki

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD An buƙaci Gwamnatin Tarayyar Nijeriya da ta ƙara zuba jari a fannin ƙirƙire-ƙirƙire da fasaha irin na kaɗe-kaɗe, domin ta iya bunƙasa tattalin arzikin ƙasar tare da samar da damar haɓaka baiwar matasa da suke tasowa. Daraktan Kiɗa na Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF), Kyaftin na Runduna Oludare Ayanbode, ne ya yi wannan kira yayin da yake ɗaya daga cikin alƙalan da suka jagoranci gasar kiɗa ta ƙasa a Abuja karo na takwas, wato Abuja National Music Competition (ANMC). A cewarsa, har yanzu akwai buƙatar gwamnati ta ƙara ƙoƙari wajen gano baiwar yara tun suna…
Read More
MOPPAN ta goyi bayan dakatar da Jaruman Kannywood biyu da Hukumar Tace Fina-finai ta yi

MOPPAN ta goyi bayan dakatar da Jaruman Kannywood biyu da Hukumar Tace Fina-finai ta yi

Daga AISHA ASAS  MOPPAN ta bayyana cikakken goyon bayanta ga matakin da Hukumar Tace Fina-finai ta Kano ta ɗauka na dakatar da wasu jaruman Kannywood na tsawon shekara guda, tana mai cewa hukuncin ya dace da abin da suka aikata. A cikin wata sanarwa ta musamman da shugaban ƙungiyar na ƙasa Shehu Hassan Kano ya fitar, ƙungiyar ta nuna rashin jin daɗinta tare da yin Allah wadai da halayen da suka janyo ɗaukar matakin, tana mai bayyana cewa irin waɗannan ɗabi’u ba su dace da kyawawan halayen Hausawa da kuma koyarwar addinin Musulunci ba. Sanarwar ta bayyana cewa, abin da…
Read More
Seyi Tinubu ya ba wa Cubana Chief Priest baki bayan shan kaye a zaɓen fidda gwani

Seyi Tinubu ya ba wa Cubana Chief Priest baki bayan shan kaye a zaɓen fidda gwani

Daga AISHA ASAS  Seyi Tinubu ya aike wa fitaccen ɗan kasuwa kuma jigo a harkar nishadi Cubana Chief Priest saƙon ƙarfafa gwiwa bayan ya gaza samun tikitin Jam’iyyar All Progressives Congress domin tsayawa takarar kujerar Majalisar Wakilai ta Tarayya daga mazabar Orsu/Orlu/Oru East da ke Jihar Imo. An gudanar da zaɓen fidda gwani na jam’iyyar APC ne a ranar Asabar a wani ɓangare na shirye-shiryen babban zaɓen shekarar 2027, inda ‘yan takara daga sassa daban-daban suka fafata domin neman amincewar jam’iyya. Cubana Chief Priest, wanda ke matsayin mai kula da tafiyar ƙungiyar City Boy Moɓement a Jihar Imo, ya shiga…
Read More
Da gaske jarumi Alex Ekubo ya rasu?

Da gaske jarumi Alex Ekubo ya rasu?

Daga AISHA ASAS  Rahotanni da suka bazu cikin gaggawa a kafafen sada zumunta sun jefa dubban masoya fina-finai cikin ruɗani da jimami bayan wasu bayanai sun yi iƙirarin cewa fitaccen jarumin fina-finan Nollywood, Alex Ekubo, ya rasu yana da shekaru 40 a duniya. Jita-jitar ta fara ɗaukar hankali ne bayan wani saƙo da fitaccen jarumi Godwin Nnadiekwe ya wallafa a shafinsa na Instagram, inda ya bayyana matuƙar kaɗuwa da alhini kan wani “mummunan labari” da ya ce ya samu. A cikin saƙon, ya bayyana Ekubo a matsayin baiwar da ba kasafai ake samu irinta ba a masana’antar Nollywood, yana mai…
Read More
Daga tarihin karramawa zuwa sabuwar alƙiblar Nollywood: Cikakken nazari kan manyan nasarorin AMVCA 2026

Daga tarihin karramawa zuwa sabuwar alƙiblar Nollywood: Cikakken nazari kan manyan nasarorin AMVCA 2026

Daga AISHA ASAS  Da yammacin ranar Asabar ne titunan yankin Victoria Island da ke Jihar Iko suka fara cunkoso tun kafin a isa lokacin fara bikin karramawa mafi girma a masana’antar fina-finai ta Afirka, wato Africa Magic Viewers’ Choice Awards 2026. Motoci masu tsada suna jerawa a kofar Eko Hotel & Suites yayin da dubban masoya nishadi, ‘yan jarida, masu ɗaukar hoto da masu sharhi daga sassa daban-daban na duniya suka mamaye wajen domin shaida abin da mutane da dama suka kira “daren da zai tantance sabbin sarakunan Nollywood.” Tun daga wajen jan kafet, ana iya fahimtar cewa AMVCA ta…
Read More
Muhawarar soyayyar Ross da Rachel a fim ɗin ‘Friends’ ta sake dawowa sabuwa bayan shekaru kusan talatin 

Muhawarar soyayyar Ross da Rachel a fim ɗin ‘Friends’ ta sake dawowa sabuwa bayan shekaru kusan talatin 

Daga AISHA ASAS  A duniyar fina-finan akwai labaran da lokaci ba ya iya share su. Daya daga cikin su shi ne rikicin soyayya tsakanin Ross da Rachel a cikin shahararren shirin barkwanci nan da duniya ta yi amo da shi, wato 'Friends' rikicin da ya haifar da sanannen  mai cike da ce-ce-ku-ce, wato “We were on a break.” Shekaru kusan talatin kenan, amma har yanzu waɗannan kalmomi guda uku na ci gaba da raba kan masoya shirin, inda wasu ke ganin hujja ce, wasu kuwa na ganin uzuri ne. Tsayin shekaru ana ja-ni-in-ja ka kan wannan muhawarar ta ko hujja…
Read More