Nishadi

A da ba na sha’awar Kannywood saboda zargin da ake masu – Jaruma Samira Sani

A da ba na sha’awar Kannywood saboda zargin da ake masu – Jaruma Samira Sani

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Samira Sani ƴar asalin garin Kano ce da ta shigo Masanartar Kannywood a shekarar 2022, a tattaunarta da wakilinmu a Kano Ibrahim Hamisu, za ku ji tarihinta da kuma yadda ta daɗe tana mu'amala da ƴan Kannywood kafin ta fara fitowa a fim: MANHAJA:Za mu so ki gabatar da kanki? SAMIRA: Sunana Samira Sani, jaruma a masanartar fim ta Kannywood. Mene ne tarihinki a taƙaice? To ni ƴar asalin garin Kano ce, an haife ni a garin Dakatsalle da ke ƙaramar Hukumar Bebeji ta Jihar Kano, na yi primary da secondary duk a Dakatsalle, bayan…
Read More
Disney zai fitar da ‘Descendants’ na biyar

Disney zai fitar da ‘Descendants’ na biyar

Daga AISHA ASAS  Kamfanin fina-finai na Disney ya tabbatar da cewa, fim na biyar cikin shahararren jerin Descendants zai fito da suna 'Wicked Wonderland' a shekarar 2026. Wannan sabon fim zai bayyana a tashar Disney Channel da kuma dandamalin Disney+, inda za a ci gaba da labarin ‘ya’yan manyan azzaluman da suka fito daga tatsuniyoyin Disney.  A cikin wannan gawurtaccen fim mai fitowa za a ga fitattun jarumai da suka yi fice a fim ɗin da suka gabata, ciki har da: Brandy Norwood a matsayin Cinderella, Paolo Montalban a matsayin Sarki Charming, Rita Ora a matsayin Sarauniyar Zuciya (ƙueen of…
Read More
EFCC ta gayyaci jaruma Iyabo Ojo da AY Makun kan wulaƙanta Naira 

EFCC ta gayyaci jaruma Iyabo Ojo da AY Makun kan wulaƙanta Naira 

Daga AISHA ASAS  Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kasa (EFCC) ta gayyaci fitacciyar jarumar fina-finan Nollywood, Iyabo Ojo, da kuma shahararren jarumin barkwanci Ayo Makun (AY) domin yi musu tambayoyi kan yadda aka watsa takardun Naira a fili yayin wasu bukukuwa da suka halarta — abin da ya saɓa wa dokar Najeriya. Iyabo Ojo ta bayyana cewa, EFCC ta gayyace ta bayan bikin ɗiyarta, Priscilla, inda baƙi suka watsa Naira da kuɗaɗen ƙasashen waje. Ta ce tana ƙasar Ingila lokacin gayyatar ta zo, kuma da ta dawo a ranar 5 ga Mayu, 2025, ta halarci ofishin hukumar…
Read More
Da yawan mawaƙan Arewa ba su san yadda za su amfana da basirarsu ba – Haidar Blog

Da yawan mawaƙan Arewa ba su san yadda za su amfana da basirarsu ba – Haidar Blog

"'Diwani' ce bakandamiya a waƙoƙin da na yi" Daga: ADAMU YUSUF INDABO, Kano Fasihin mawaƙin Hausa, kuma ɗan kasuwar da ke dillancin waƙoƙin Hausa a yanar gizo, mai suna Aliyu Abubakar, da ake wa laƙabi da Haidar Blog, ya bayyana wannan kyakkyawan fata da buri da yake da shi ne a kan mawaƙa da dukkan waɗanda Allah Ya yi wa baiwar basirar na suna amfanuwa da basirar tasu don ƙara samun kwarin gwiwa gare su. Tare kuma da yin kira ga matasa da su ƙara ƙaimi wajen neman ilimi, wanda da shi ne rayuwar bawa take yin haske kuma komai…
Read More
Shugaban MOPPAN na Abuja, Auwal Falala, ya samu ƙaruwar ɗa namiji

Shugaban MOPPAN na Abuja, Auwal Falala, ya samu ƙaruwar ɗa namiji

Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja Allah Ubangiji ya albarkaci Shugaban Babbar Haɗaɗɗiyar ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Kannywood (MOPPAN) reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Hon. Auwal Sharif Falala, da samun ƙaruwar ɗa namiji a ranar Lagadi, 6 ga Afrilu, 2025, inda aka raɗa masa suna Muhammad Ashraf Falala ranar da aka yi taron suna bayan mako guda, wato Lahadi, 13 ga Afrilu, 2025. Auwal Falala ya nuna farin cikinsa da samun wannan ƙaruwa, musamman ma kasancewar, jaririn da mahaifiyarsa suna cikin ƙoshin lafiya. Baba Falala yana fitowa a finafinan Hausa masu ƙayatawar, wanda ya kasance ɗaya daga cikin jaruman…
Read More
An yi taron Tarihi da Waƙoƙin Kassu Zurmi a Sakkwato 

An yi taron Tarihi da Waƙoƙin Kassu Zurmi a Sakkwato 

Daga DAHIRU SAMA'ILA a Sokoto Sashen Harsunan Nijeriya na Jami'ar Jihar Sakkwato da ke Birnin Sakkwato ya shirya Taron ƙasa da ƙasa akan tarihin rayuwa da waƙoƙin makaɗa Abubakar Kassu Zurmi.  Taron na kwana huɗu ya gudana ne tsakanin Ranakun Jumu'a 18 zuwa Litinin 21 ga watan Afrilun 2025 a harabar jami'ar da ke Madorawa a birnin Sakkwato. An buɗe bikin mai taken 'Wawa Mugunyar Tsirfa' Tarihin Rayuwa da Waƙoƙin Makaɗa Abubakar Kassu Zurmi a Ranar Asabar 19 /04 2025 tare da samun halartar masana da manazarta daga ciki da kuma wajen Nijeriya. ɗan majalisar Wakilai ta Tarayya mai wakiltar…
Read More
Bikin auren ‘yar jaruma Zulai Babeji: ‘Yan fim sun mata kara

Bikin auren ‘yar jaruma Zulai Babeji: ‘Yan fim sun mata kara

Daga MUKHTAR YAKUBU Fitacciyar jaruma a masana'antar finafinai ta Kannywood Hajiya Zulai Babeji ta yi bikin auren 'yar autarta, wato Maryam M. Usman Nunu wadda aka fi sani da Maryam 'Yar autar Mama.  Bikin auren dai an fara gudanar da shi ne a ranar Asabar 5 ga Afrilun 2025 inda aka fara da taron liyafa a ɗakin taro na Gidauniyar Jihar Kano da ke kan titin BUK Kano da misalin ƙarfe biyar na yamma. Taron bikin dai ya samu harkar 'yan fim da dama da suka halarci wajen domin taya jaruma Zulai Babeji murna. A wajen taron an sha shagali…
Read More
Kallon finafinai ne ya zaburar da ni na shiga harkar fim – Sayyadi

Kallon finafinai ne ya zaburar da ni na shiga harkar fim – Sayyadi

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Faruk Sayyadi na ɗaya daga cikin zaƙakurai a masanantar Kannywood; ƙwararre ne a fannin zane-zane da tasirin gani (ɓFɗ). Shi darakta ne, kuma marubucin fim ne kuma jarumi ne a masana'antar Kannywood. A wannan hira ta musamman da wakilinmu Ibrahim Hamisu ya yi da shi a Kano, za ku ji tarihinsa da ma wasu muhimman bayanai.  MANHAJA: Za mu so ka gabatar mana da kanka? SAYYADI: Da fari dai, sunana Faruk Sayyadi. An haife ni a unguwar Dandago, kusa da ƴar Maishinkafi. Na yi makarantar firamare a Mawgan, sannan na tafi makarantar sakandare ta Kawaji,…
Read More
Tabbas makomar Kannywood mai kyau ce – Momoh 

Tabbas makomar Kannywood mai kyau ce – Momoh 

"Bayar da gudunmawa ga haɓakar adabin Hausa abu ne da na yi alfahari da shi" Daga IBRAHIM HAMISU a Kano  Aminu Aliyu Shariff Momoh, wanda da aka fi sani da Aminu Momoh na ɗaya daga cikin manyan jarumai kuma fitattu da suka bayar da gagarumar gudunmawa a masana'antar fim ta Kannywood, domin Momoh ya kasance a Kannywood tun shekaru 24 da suka gabata. Don haka za mu iya cewa, ya kasance daga cikin ɗaiɗaikun jaruman da ba sa tsufa a masana'antar Kannywood.  A wannan makon, shafin Nishaɗi na jaridar Blueprint Manhaja ya tattauna da jarumin don samar wa masu karatu…
Read More
Labarin fim ɗin ‘Faliha & Falisha’ ya faru da gaske – Mansurah Isah

Labarin fim ɗin ‘Faliha & Falisha’ ya faru da gaske – Mansurah Isah

DAGA MUKHTAR YAKUBU a Kano A yanzu haka dai shirye-shirye sun yi nisa na fara haska gawurtaccen fim ɗin nan mai suna 'Faliha & Falisha' wanda tsohuwar jaruma kuma furodusa Mansurah Isah ta ɗauki nauyin shiryawa. Fim ɗin wanda ake sa ran za a fara haska shi a sinima a ranar 2 ga Afrilun nan za a nuna shi ne a manyan sinimomi kamar Platinum da ke Kano, Silverbird Kaduna, Silverbird Jabi, Dex View Kano, DexView Katsina, Mees Palace Jos (TBC) Alinco Cinema Ijaye Lagus, Bridge Park Cinema Kaduna, da sauran sinimomi da ke faɗin tarayyar Nijeriya. Domin ganin yadda…
Read More