19
Jul
Daga AISHA ASAS A Najeriya, addini ba kawai wata alaƙa ce tsakanin mutum da Ubangijinsa ba. Wani ɓangare ne da ke da tasiri a rayuwar al'umma, zamantakewa da al'adu. Saboda haka, duk lokacin da fitaccen mutum ya sanar da sauya addininsa, lamarin kan ɗauki hankalin jama'a, ya haifar da ce-ce-ku-ce tare da jan ra'ayoyi mabambanta. A shekarun baya-bayan nan, an samu wasu fitattun 'yan wasan Nollywood, mawaƙa da masu ƙirƙirar abubuwan da ake wallafawa a kafafen sada zumunta da suka bayyana cewa, sun rungumi addinin Musulunci bayan sun taso a gidajen Kirista ko kuma bayan sun daɗe suna bin addinin…
