Nishadi

Da Ɗumi-ɗumi: Jaruma a Kannywood, Saratu Giɗaɗo ta riga mu gidan gaskiya

Da Ɗumi-ɗumi: Jaruma a Kannywood, Saratu Giɗaɗo ta riga mu gidan gaskiya

Daga BASHIR ISAH da RABI'U SANUSI Allah Ya yi wa fitacciyar jaruma a masana'antar shirya fina-finai ta Kannywood, Saratu Giɗaɗo wadda aka di sani da Daso, rasuwa. Jarumar ta rasu ne a ranar Talata kamar yadda wani makusancinta ya bayyanawa MANHAJA. Da yake amsa tambayar wakilinmu, makusancin marigayiyar ya ce lafiya ƙalau Saratu ta wayi gari a wannan rana. Ya ƙara da cewa, hasali ma Mmarigayiyar ta ɗauki azumi a wannan rana. Har wa yau, wata majiyar ta sheda ma wakilinmu cewa, "Saratu Gidado tana fama da rashin lafiya a tsaitsaye ne, wanda a yau kuma ta yi mutuwar Fuj'a".…
Read More
Abin da Shugaban NFC, Ali Nuhu suka tattauna da Jakadan Spaniya a Nijeriya

Abin da Shugaban NFC, Ali Nuhu suka tattauna da Jakadan Spaniya a Nijeriya

Daga BASHIR ISAH A ranar Litinin ta wannan makon Shugaban Hukumar Shirya Fina-finai ta Ƙasa (NFC), Dokta Ali Nuhu, ya yi ganawa ta musamman a Abuja tare da Jakadan Ƙasar Spaniya a Nijeriya, Juan Ignscio Sell, inda suka tattauna kan muhimman batutuwa. Tattaunawar tasu ta shafi samar da ƙawance tsakanin NFC da Spaniya domin bunƙasa harkokin masana'antar ƙirƙire-ƙirƙire a Nijeriya. Da yake jawabi, Ali Nuhu ya yaba wa Jakada Sell bisa goyon bayan da ofishinsa kan bai wa masana'antar, tare da neman ya faɗaɗa goyon bayan nasa zuwa ga hukumar NFC don bunƙasa harkar shirya fina-finai da sauransu a Nijeriya.…
Read More
Mun haramta shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a Kano — El-mustapha

Mun haramta shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a Kano — El-mustapha

Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ta ce dag yanzu ta haramta shirya fina-finai masu nuna faɗan 'yan daba da harkokin 'yan daudu a jihar. Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da hukumar ta fitar mai ɗauke da sa hannun Jami'in Yaɗa Labarai na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman da kuma kwanan wata 3 ga Afrilun da ake ciki. Sanarwar ta ce: "Biyo bayan ƙorafe-ƙorafen da al'umma ke yi a kan shirya fina-finan da ke nuna faɗan daba da harkar daudu a jihar Kano, Shugaban Hukumar tace fina-finai da Ɗab'i ta Jihar Kano, Abba El-mustapha, ya bada umarnin dakatarwa tare…
Read More
Sarari ya ɗaukaka darajar MOPPAN zuwa ƙololuwa, inji Habibu Barde

Sarari ya ɗaukaka darajar MOPPAN zuwa ƙololuwa, inji Habibu Barde

“Muna son samar da tsarin shugabancin da zai saita masana'antar Kannywood” Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Alhaji Habibu Barde Muhammad shi ne sabon shugaban haɗaɗiyar ƙungiyar kwararru ta masu shirya fim ta ƙasa, wato MOPPAN, da ya kama mulki bayan saukar da tsohon shugaban Dakta Ahmad Muhammad Sarari ya yi a ƙarshen watan Janairun da ya gabata, wanda kafin hakan shi ne mataimaki na Arewa ta Tsakiya . Domin jin wanene Habibu Barde Muhammad da kuma irin gudunmawar da ya bayar a harkar fim, jaridar Blueprint Manhaja ta tattauna da shi, don haka sai ku biyo mu ku ji yadda ta…
Read More
’Yan sanda sun yi karar Jaruma Amal kotu bayan kotu ta wanke ta

’Yan sanda sun yi karar Jaruma Amal kotu bayan kotu ta wanke ta

Daga AISHA ASAS  Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya Shiyya ta Ɗaya (wato Zone 1) ta kai ƙarar fitacciyar jaruma a Kannywood, Amal Umar, gaban kotu kan zargin bayar da toshiyar baki ga wani ɗan sanda da ke binciken ta kan zargin aikata wata almundahanar kuɗi da ake zargin da sa hannunta a ciki, duk da cewa, kotu ta wanke jarumar tun a watannin baya. A jiya Alhamis ne aka gurfanar da jarumar a kotun Majistare mai lamba 24 da ke Jihar Kano.  Da yake jawabi a gaban manema labarai, Kakakin Rundunar 'Yan Sanda Na Shiyya Ta Ɗaya, CSP Bashir Muhammad, ya…
Read More
‘Ban fuskanci wata matsala ba wajen sauya jinsina’ – Bobrisky

‘Ban fuskanci wata matsala ba wajen sauya jinsina’ – Bobrisky

Daga BASHIR ISAH Matashin ɗan Nijeriyar nan da ya sauya jinsinsa zuwa mace, wato Bobrisky, ya ce komai ya tafi daidai na aikin sauya masa jinsi da aka yi daga namiji zuwa mace. A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Instagram, Bobrisky ya bayyana farin cikinsa kan yadda aka yi masa aiki cikin nasara, yana mai cewa babu wata matsala da ya fuskanta a yayin aikin. A cikin saƙon nasa, ya bayyana godiyarsa ga likitocinsa na gida da ƙetare bisa ƙoƙarin da suka yi wajen sauya masa jinsi zuwa mace. Majiyarmu ta rawaito Bobrisky na cewa, “Komai na…
Read More
Yadda jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Yadda jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Daga AISHA ASAS A ranar Talata da ta gabata ne, shahararren jarumi a masana’antar Kannywood Dakta Ali Nuhu ya kama aiki a hukumance a matsayin Shugaban Hukumar Finafinai ta Qasa (NFC) tare da alƙawarin hanzarta kawo cigaba a masana’antar finafinan Nijeriya. Bayanin wanda ya fito daga wurin Daraktan Ya daa Labarai na hukumar, Mista Brian Etuk. A sanarwar wadda ya gabatar ga ‘yan jarida, Mista Brian ya ce, a ƙwarya-ƙwaryar bikin miqa mulki da aka gudanar a shelkwatar hukumar da ke Jos ta Jihar Filatu, wanda ya samu halartar manyan baqi, da suka haɗa da jiga-jigan masana’antar fim, ma’aikatan hukumar…
Read More
Hukumar tace finafinai ta bada umurnin rufe dukkan gidajen gala da ke Kano

Hukumar tace finafinai ta bada umurnin rufe dukkan gidajen gala da ke Kano

Daga AISHA ASAS Hukumar tace finafinai ta Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Abba El-Mustapha ta bayar da umurnin kulle duk wani gidan gala da ke faɗin Jihar Kano. Wannan na daga cikin shirye-shiryen da hukumar ke yi na tarbon wata mai tsarki, watan Ramadana. Sanarwar wadda ta fito ta hannun jami’in hulɗa da jama'a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman. A cewar sanarwar, hukuncin na zuwa ne bayan wata ganawa da shugaban hukumar ya yi da jagororin koungiyar ta masu gidajen gala a ofishinsa. Kamar yadda ya bayyana, shugaban hukumar Abba El-Mustapha, ya ce, dokar za ta fara aiki ne a ranar…
Read More
Jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Ya sha alwashin bunƙasa harkokin finafinai Daga BASHIR ISAH Jarumi a masana'antar Kannywood, Dokta Ali Nuhu, ya kama aiki a hukumance a matsayin Shugaban Hukumar Fina-finai ta Ƙasa (NFC). Sanarwa mai ɗauke da sa hannun Daraktan Hulɗa da Jama'a na hukumar, Brian Etuk, ta nuna a ranar Talata Ali Nuhu ya shiga ofis a matsayin shugaban hukumar na bakwai. Ta ƙara da cewa, jarumin ya sha alwashin yin aiki tukuru don bunƙasa masana'antar fina-finai ta Nijeriya. Da yake jawabi a wajen bikin karɓar ragamar aiki wanda aka shirya a hedikwatar hukumar da ke Jos, babban birnin Jihar Filato, Ali Nuhu…
Read More
El-mustapha ya nuna alhini kan rasuwar mahaifiyar Afakallah

El-mustapha ya nuna alhini kan rasuwar mahaifiyar Afakallah

Daga BASHIR ISAH Sakataren Hukumar Tace Finafinai na Jihar Kano, Alh. Abba El-mustapha, ya nuna alhininsa kan rasuwar mahaifiyar tsohon sakataren hukumar, Malam Na'abba Afakallah. Sanarwar da hukumar ta fitar ranar Juma'a ta bakin Jami'in Yaɗa Labarai, Abdullahi Sani Sulaiman, ta ce Hajiya Gwaggo ta rasu ne bayan fama da rashin lafiya. Abba El-mustapha ya bayyana marigayiyar a matsayin uwa tagari, kuma abar koyi wadda rasuwarta ta haifar da wagegen giɓi a cikin al'umma. Ya ƙara da cewa, mutuwarta babban rashi ne ba ga ahalinta kaɗai ba har ma da al'ummar Musulmi baki ɗaya. Daga nan, El-Mustapha ya yi addu'ar…
Read More