Za mu gudanar da ayyukan cigaban al’ummar ƙaramar Hukumar Doguwa – Abdulrashid Rilwan

Spread the love

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano

Zaɓaɓɓen Shugaban ƙaramar Hukumar Doguwa a Jihar Kano, Hon. Abdulrashid Rilwan ya bayyana cewa  abinda suka sa a gaba  a  yanzu a shugabancin ƙaramar hukumar shine su tabbatar da haƙƙin  al’ummar Doguwar yana zuwa  gare su ana yi musu ayyukan bunƙasa cigabansu.

Ya bayyana haka ne da yake zantawa da manema labarai a Kano ya yi nuni da cewa akwai  ƙalubale da yawa da suke fuskanta a Doguwa  na  rashin ayyukan  cigaba  da ake fama dasu  a yankin sakamakon ana  turo tarin  haƙƙoƙinsu na  ƙaramar hukumar amma saboda azzalumai da Allah ya  ya haɗa su dasu sun mallake suna  riƙewa  a matsayin nasu ba sa ayyuka da za su inganta rayuwar al’umma. 

Hon. Abdulraahid Rilwan ya ce a tsawon lokacin nan da aka dawo na mulkin Damakwaraɗiyya a ƙasar nan  an turo da abubuwa na kason arziƙi masu ɗinbin yawa   da  yakamata a raya cigaban yankin amma waɗannan mutane da ke ci da gumin  yan yankin  basa hidimtawa al”umma dasu.

Ya ce zuwan su yanzu  da yardar Allah gwargwadon hali da iko za su saka ɗan ba na kyautata cigaban yankin ta farawa  da bunƙasa harkar ilmi da raya ƙasa suna kuma da yaƙinin na  sanin zaɓaɓɓen  Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf  zai basu  dukkan goyon baya da gudunmuwa da zasu  tabbatar sun yi aiki na raya ƙasa da raya cigaban al’ummar karamar hukumar Doguwa domin  duk mutumin da ka taimake shi ka raya shi da al’ummar sa shima akwai kyakkyawan zato zai rama alkhairi da alkhairi.

Hon. Abdulrashid Rilwan ya ce za su   tabbatar dukkan tsare- tsare na kwankwasiyya sun yi aiki da tabbatar dasu domin in an bi tsarin al”ummar Doguwa za su ji daɗi da farin ciki.Duk da cewa sun zo sun sami tarin matsaloli a ƙaramar hukuma sakamakon Allah ya tara musu wasu da basa kishin al’umma da son cigaban su sakamakon  ƙaramar hukumar ta yi nisa  da cikin birni 

Ya ce domin a da al”ummar Doguwa  basa samun dama  da za su bayyana ra’ayinsu  domin a ɗauki mataki na gaggawa shi yasa mutane marasa kishin da suke kwace musu zaɓe in sun yi  suka sami dama suke danne  haƙƙin al’umma a Doguwa

Shugaban ƙaramar Hukumar Doguwa, Hon. Abdulrashid  Rilwan ya  godewe jagoran Kwankwasiyya Dakta Rabiu Musa Kwankwaso da  Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf da ya girmama dan asalin yankin su Umar Haruna Doguwa na   bashi dama yake  hidimtawa a Gwamnatinsa 

 Hon. Abdulrashid Rilwan Doguwa ya ce wannan dama da ake basu  amana ce tasa domin duk dan ƙaramar hukumar Doguwa in dai ba mara daraja ba zaka sane shi mai amana da halacci  suna saka alkhairi da alkhairi , duk wanda ya yi musu babban burinsu su saka masa  shi yasa suke jinjina ga  jagoransu na kasa a  siyasa  Dakta Rabiu Musa  Kwankwaso domin wannan  irin tarbiyya da ya basu kenan suke nunawa a koyaushe.

By ukarofi