01
Jun
Daga USMAN KAROFI Yaƙi tsakanin Amurka da Iran ya sake ɗaukar wani sabon salo bayan Amurka ta kai hare-hare kan wasu wuraren sojin Iran a ƙarshen mako, yayin da Iran ta mayar da martani da kai hare-hare kan sansanonin sojin Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya. Rundunar Amurka ta ce hare-haren nata sun biyo bayan zargin cewa Iran ta harbo jirgin leƙen asirin Amurka mara matuƙi da ke shawagi a sararin samaniyar ƙasa da ƙasa. A cewar CENTCOM, jiragen yaƙin Amurka sun lalata wasu cibiyoyin kariyar sararin samaniyar Iran, cibiyar sarrafa hare-hare da kuma wasu jirage marasa matuƙi da ake…
