Kasashen Waje

Biden ya jinjina wa Tinubu kan kare martabar dimokuraɗiyya

Biden ya jinjina wa Tinubu kan kare martabar dimokuraɗiyya

Shugaba Joe Biden na ƙasar Amurka, ya yaba da shugabancin da Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu, ke yi wa ƙungiyar raya tattalin arzikin ƙasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS). Biden ya jinjina wa Tinubun ne la'akari da ƙoƙarin da ke ECOWAS ke yi wajen maido da tsarin mulkin dimokraɗiyya a ƙasar Nijar. Biden ya ce jajircewar da Tinubu ke yi wajen kare tsarin dimokuraɗiyya a Nijar da ma yankin Afirka ta Yamma baki ɗaya abin a yaba ne. Ya byyana haka ne yayin ganawarsu da Tinubu a wajen taron G20 da ya gudana a Delhi, Kasar Indiya. Cikin sanarwar da ta fitar…
Read More
Juyin mulkin Burkina Faso: Reshe ya nemi juyawa da mujiya

Juyin mulkin Burkina Faso: Reshe ya nemi juyawa da mujiya

Daga BASHIR ISAH An cafke wasu manyan jami'an soji a ƙasar Burkina Faso bisa yunƙurin yin juyin mulki ga sojojin da suka hamɓarar da mulkin dimokraɗiyya a ƙasar. Mai gabatar da ƙara na mulkin sojin ƙasar, Manjo Alphonse Zorma ne ya bayyana haka a ranar Juma'a. Ya ce a makon da ya gabata masu bincike suka samu rahoto kan shirin da wasu sojoji da tsoffin sojojin ƙasar ke yi na neman kifar da sosjojin da ke riƙe da ƙasar a halin yanzu. Sanarwar ta ce cikin hasfsoshin da lamarin ya shafa har da Kyaftin Ibrahim Traore wanda jigo ne a…
Read More
Girgizar ƙasa ta kashe sama da mutum 296 a Moroko

Girgizar ƙasa ta kashe sama da mutum 296 a Moroko

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Moroko sun ce, sama da mutum 296 sun mutu sakamakon girgizar ƙasa mai karfin maginitud 6.8 da ya auku a ƙasar. Jami'ai sun ce galibin waɗanda suka mutu mutanen da suka maƙale ne a ɓuraguzan gine-gine wanda kai wa gare ya yi wahala balle a cece su a yankunan Kudancin Marrakech. Iftilain girgizar ƙasar ya auku ne da sanyin safiyar wannan Asabar ɗin, lamarin da ya haifar da zubewar gine-gine a wasu manyan biranen ƙasar. A ƙalla mutum 153 aka rawaito sun jikkata kuma ana yi musu magani a asibiti. An ga jami'ai a…
Read More
An rantsar da Janar Nguema shugaban ƙasa na riƙon ƙwarya a Gabon

An rantsar da Janar Nguema shugaban ƙasa na riƙon ƙwarya a Gabon

A ranar Ltinin aka rantsar da Janar ɗinda ya jagoranci juyin mulki a ƙasar Gabon, Brice Oligui Nguema, a matsayin shugaban riƙon ƙwarya bayan hamɓarar da Shugaba Bongo. Janar Nguema, ya jagoranci juyin mulkin da sojoji suka yi a ranar Larabar da ta gabata kan shugaban ƙasar Ali Bongo Ondimba, wanda ya fito daga gidan iyalan da suka mulki ƙasar sama da shekaru hamsin. Sojoji sun kifar da gwamnatin Bongo ne bayan da aka bayyana na shi a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar a watan da ya gabata bayan da ‘yan adawa suka…
Read More
Erdogan zai gana da Putin kan samar da hatsi a duniya

Erdogan zai gana da Putin kan samar da hatsi a duniya

Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan na shirin ziyartar Rasha domin tattaunawa da takwaransa na ƙasar, Vladimir Putin game da farfaɗo da yarjejeniyar fitar da hatsi daga tekun Black Sea. Ana sa ran tattaunawar tsakanin Erdogan da Putin ta yi armashi ta yadda za a iya amfani da ita wajen faɗaɗa yarjejeniyar zaman lafiyar Ukraine. Jam’iyyar Erdogan mai mulki ta shaida wa manema labarai cewa, za a gudanar da wannan tattaunawar ce a wurin shaƙatawa da ke gavar Tekun Black Sea a birnin Sochi, inda za su mayar da hankali kan kawar da matsalar ƙarancin abinci da ke tunkarowa. Watakila shugaba…
Read More
Ɗumamar yanayi za ta fara laƙume rayuka a duniya – IMF

Ɗumamar yanayi za ta fara laƙume rayuka a duniya – IMF

Asusun Bada Lamuni na Duniya IMF ya yi gargaɗin cewa, matsalar ɗumamar yanayi na barazana ga matalautan ƙasashe, wanda idan har ba a ɗauki matakan gaggawa ba, za ta fara haifar da hasarar rayuka nan da shekarar 2060. IMF ya ce, za a samu ƙaruwar kaso 8.5 na adadin rayukan da za a yi asara, musamman a yankunan da ke fama da matsalar sauyin yanayi, kuma kaso 14 na waɗannan ƙasashe za su fuskanci qaruwar tsananin zafi. Daga cikin ƙasashe 39, wanɗanda ke ɗauke da kusan mutane biliyan guda na al’ummar duniya, rabi daga cikinsu da ke fama da wannan…
Read More
Juyin mulki: Sojoji sun naɗa Kanal Brice Nguema a matsayin sabon shugaban Ƙasar Gabon

Juyin mulki: Sojoji sun naɗa Kanal Brice Nguema a matsayin sabon shugaban Ƙasar Gabon

Sojojin da suka yi juyin mulki a ƙasar Gabon sun sanar cewa Kanal Brice Clotaire Oligui Nguema ne sabon shugaban ƙasar wanda hakan ya kawo ƙarshen mulki na shekara 55 da zuri'ar Bongo suka shafe suna yi a ƙasar. Manhaja ta rawaito a ranar Laraba sojojin ƙasar suka hamɓarar da Ali Bongo Ondimba daga karagar mulki tare da soke zaɓen da aka ce Odimba ne ya lashe. Sun ce zaɓen da ya gudana a ƙasar cike yake da maguɗi. A ranar Talata da daddare Hukumar Zaɓe ta ƙasa ta bada sanarwar sakamakon zaɓen inda Ali Bongo ya samu ƙuri'u kashi…
Read More
Sojoji sun karɓe mulki a Gabon

Sojoji sun karɓe mulki a Gabon

Sojojin ƙasar Gabon sun sanar da ƙwace iko daga gwamnati mai ci tare da rushe sakamakon zaɓen da aka bayyana Ali Bongo Ondimba a matsayin wanda ya lashe. Kafin sanarwar sojojin, bayanai sun ce an shafe tsawon sa’o’i ana jin ƙarar harbin bindiga a sassan Libreville babban birnin ƙasar kodayake babu tabbacin ko musayar wuta ce ko kuma kawai sojojin na harbin iska ne. Cikin jawabin kai tsayen da suka yi ta gidan talabijin ɗin ƙasar da safiyar Laraba, sojojin sun sanar da rushe dukkanin sassan gwamnati ciki har da majalisun dokoki da kuma kotun kundin tsarin mulki. A cewar…
Read More
Shugaban Ƙasar Zimbabwe ya nemi yin tazarce

Shugaban Ƙasar Zimbabwe ya nemi yin tazarce

Shugaban Ƙasar Zimbabwe mai shekaru 80, Emmerson Mnangagwa, ya nuna ra'ayinsa na sake maimara wasu shekaru a kujerar shugabancin ƙasar. Shugaba wanda ya kasance shugaban Ƙasar Zimbabwe na biyu tun bayan dogon mulkin shugaba Robert Mugabe da ya shafe shekaru kusan 40 a mulki. Emmerson Mnangagwa, shi ne tsohon mataimakin shugaban ƙasa Mugabe, ya karɓi ragamar shugabancin ƙasar bayan juyin mulkin, ya kuma yi alƙawarin bunƙasa tattalin arziki ƙasar, da bayar da 'yancin faɗin albarkacin baki, da sassauta takurawar da ake yi wa 'yan adawar da ke magantuwa kan wa'adin mulkin Mugabe, da kuma taɓarɓarewar dangantaka da ƙasashen yammacin duniya.…
Read More
Ƙungiyar AU ta dakatar da Jamhuriyar Nijar daga dukkan sha’aninsu

Ƙungiyar AU ta dakatar da Jamhuriyar Nijar daga dukkan sha’aninsu

Ƙungiyar Tarayyar Afrika, AU, ta fitar da Nijar daga cikinta, tare da umurtar sojojin da suka yi juyin mulki su koma barikinsu don yin abin da aka san su da shi, wato tsare ƙasa. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne a wata takarda da ta fitar a ranar Talatar da ta gabata, sannan ta ƙara kira da babbar murya ga sojojin da su saki hamɓararen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum. Bayan wannan, ƙungiyar ta AU ta ɗau alwashin sake bibiyar irin matakan da ƙungiyar ECOWAS ta ɗauka kan Jamhuriyar Nijar don ganin ta inda ya kamata ta qara kutsa kai da nufin…
Read More