Kasashen Waje

Al Green ya ƙalubalance Trump kan bidiyon Obama

Al Green ya ƙalubalance Trump kan bidiyon Obama

Dan majalisar Democrat Al Green ya bayyana cewa ya ƙalubalance Shugaban Amurka, Donald Trump, a jawabin State of the Union kan bidiyo “mai tsananin rashin kunya” da aka wallafa a kafafen sada zumunta na Trump, wanda ke nuna tsohon Shugaba Barack Obama da matarsa a matsayin apes. Green, daga Teɗas, ya nuna takarda mai rubutu: “Black people aren’t apes,” yayin da Trump ke shiga ɗakin Majalisar. White House ta cire bidiyon daga kafafen sada zumunta, Trump ya ce wani ma’aikaci ne ya wallafa shi. “Ina so ya san cewa nuna Shugaba Obama da matar sa a matsayin apes ba abu…
Read More
Wani kamfanin Gaza zai gina gidaje a yankin da Isra’ila ta ƙwace

Wani kamfanin Gaza zai gina gidaje a yankin da Isra’ila ta ƙwace

Kamfanin Masoud & Ali Contracting Co na Gaza ya samu kwangilar gina sansanin yan gudun hijira wanda United Arab Emirates ta ɗauki nauyin kuɗi, domin dubban ‘yan gudun hijira a yankin da Isra’ila ke ƙarƙashin ikon soja. Shirin yana nufin fara sake ginawa ba tare da jiran Isra’ila ta janye ba, mataki da ake ganin zai haɗu da wanzar da zaman lafiya da kuma kawar da makamai daga hannun ‘yan Hamas a mataki na gaba na tsagaita wuta karkashin tsarin Trump. Masu sha’awar aikin sun bayyana cewa amfani da ma’aikata na cikin gida zai iya rage rashin jin daɗi ga…
Read More
DSS ta kama mutum na shida da ake zargi da kitsa harin Owo

DSS ta kama mutum na shida da ake zargi da kitsa harin Owo

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hukumar Tsaro ta Farin Kaya DSS ta sanar da cafke wani mutum da ake zargi yana da hannu a harin da aka kai cocin Katolika na St. Francis da ke Owo a Jihar Edo a shekarar 2022. Mutumin nan bayan nan wanda aka bayyana da suna Sani Yusuf, shi ne cikon na shida da ake zargi da kitsa harin wanda ya yi sanadiyar mutuwar fiye da masu ibada 40 tare da jikkata wasu da dama. Tuni dai hukumar DSS ta riga ta kama mutum biyar waɗanda suke fuskantar shari’ar aikata laifukan ta’addanci. Gidan Talabijin…
Read More
Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya taya Musulmi murnar azumin Ramadana

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya ya taya Musulmi murnar azumin Ramadana

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, ya fitar da saƙo mai taɓa zuciya domin murnar fara watan Ramadan na Shekarar 2026 a inda ya yi kira ga duniya baki ɗaya da ta rungumi ruhin zaman lafiya, tausayi da haɗin kai da wannan wata mai tsarki ke ɗauke da shi. A cikin saƙon nasa, Guterres ya jaddada cewa Ramadan ba lokaci ne na ibada da tunani kawai ba, wata ne na ƙarfafa bege da zaman lafiya a tsakanin al’umma. Ya yi kira ga kowa da kowa da ya yi amfani da wannan lokaci wajen ƙarfafa haɗin kai da kuma…
Read More
Amurka na shirin bai wa jama’a damar kallon abubuwan da aka haramta

Amurka na shirin bai wa jama’a damar kallon abubuwan da aka haramta

Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka na shirin ƙaddamar da wani sabon shafin intanet mai taken “Freedom.gov”, wanda manufarsa ita ce bai wa jama’a, musamman mazauna Turai damar shiga da kallon abubuwan da gwamnatocinsu suka takaita ko suka haramta. Rahoton da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fitar ya nuna cewa shirin na ƙarƙashin jagorancin Mataimakiyar Sakataren Hulɗa da Jama’a ta Amurka, Sarah Rogers, kuma an yi niyyar sanar da shi a wani taron tsaro da aka gudanar a birnin Munich na Jamus, sai dai aka dakatar ba tare da bayyana dalili ba. Majiyoyi sun ce an tattauna yiwuwar sanya wata fasaha…
Read More
Gwamnati Kanada ta fara shirin rage dogaro da Amurka a ɓangaren tsaro

Gwamnati Kanada ta fara shirin rage dogaro da Amurka a ɓangaren tsaro

Gwamnatin Kanada ta sanar da sabbin sauye-sauye a tsarin karɓar baƙin haure masu ƙwarewa, inda za a fara bai wa wasu rukunai na musamman fifiko domin cike giɓin ƙwararru a sassa masu muhimmanci. Ministar Shige da Fice ta ƙasar ta ce sauye-sauyen na shekarar 2026 za su jawo ƙwararru da za su iya fara ba da gudunmawa nan take, musamman a ɓangaren kiwon lafiya, bincike, sufuri da kuma tsaro. Firayim Minista Mark Carney ya jaddada cewa maƙasudin shirin shi ne rage yawan mazauna na dindindin da ake karɓa a ƙasar, tare da mayar da hankali kan hazikai da za su…
Read More
Shugaban Jamus na goyon bayan taƙaita wa yara amfani da kafofin sadarwa 

Shugaban Jamus na goyon bayan taƙaita wa yara amfani da kafofin sadarwa 

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya bayyana goyon bayansa ga matakan da za su taƙaita damar yara shiga kafafen sada zumunta, yana mai cewa illar bayanan ƙarya da ake kirkira ta hanyar fasahar zamani ta sa ya sake duba matsayinsa. Ya ce ba za a bar al’umma ta rushe sakamakon yaɗuwar bayanan bogi da aka ƙirƙira domin yaudarar jama’a ba, musamman idan yara ne ke yawan shafe sa’o’i masu yawa a kan intanet. Jam’iyyarsa ta nemi a hana yara ƙasa da shekara 16 shiga wasu manhajoji, yayin da ake sa ran jihohin ƙasar za su tattauna yadda za a kafa…
Read More
Iran na ci gaba da gyara da ƙarfafa wasu muhimman wuraren soja da aka kai wa hari a shekarar baya

Iran na ci gaba da gyara da ƙarfafa wasu muhimman wuraren soja da aka kai wa hari a shekarar baya

An gina garkuwar kankare a wani muhimmin sansani An rufe hanyoyin shiga ramuka a wuraren nukiliya Matakin na zuwa ne yayin da rikici da Amurka ke ci gaba Sabbin hotunan tauraron dan adam da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya gani sun nuna cewa Iran na ci gaba da gyara da ƙarfafa wasu muhimman wuraren soja da aka kai wa hari a shekarar da ta gabata. Masana sun ce an gina garkuwar kankare mai kauri tare da lullube ta da ƙasa domin kare wani sabon gini a wani sansanin soja, tare da rufe mashiga zuwa wasu ramuka a wuraren da…
Read More
Birtaniya ta daina manna biza a fasfon ’yan Nijeriya bayan rungumar tsarin fasahar zamani

Birtaniya ta daina manna biza a fasfon ’yan Nijeriya bayan rungumar tsarin fasahar zamani

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Gwamnatin ƙasar Birtaniya ta sanar da cewa daga ranar 25 ga Fabrairu 2026 za ta daina manna alamar biza a cikin fasfo ga matafiya ’yan Nijeriya, inda za ta maye gurbinsa da cikakken tsarin visa na fasahar zamani, wato eVisa.  Hukumomi sun bayyana matakin a matsayin wani babban sauyi a tsarin shige da ficen ƙasar. Sanarwar da Ofishin Bayar Da Biza Na Hukumar Shige Fice Ta Birtaniya (UKVI) ya fitar a Abuja ta ce duk sabbin bizar ziyara (Visit visas) da za a bai wa ’yan Nijeriya za su kasance na fasahar zamani ne kacokan. Wannan…
Read More
An kama matashiya ‘yar 18 da zargin kai hari wata makaranta a Kanada 

An kama matashiya ‘yar 18 da zargin kai hari wata makaranta a Kanada 

Jami’an ‘yan sanda a Kanada sun bayyana cewa, wata matashiya mai shekaru 18, Jesse Van Rootselaar, ce ta kai harin bindiga a wata makaranta a yankin British Columbia, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane tara ciki har da ita kanta. Da farko an ruwaito mutuwar mutum goma, amma daga bisani aka gyara adadin zuwa tara. Lamarin ya faru ne a wata ƙaramar alƙarya mai mutane kusan 2,400 a Tumbler Ridge. ‘Yan sanda sun ce ana zargin ta fara kashe mahaifiyarta mai shekaru 39 da kuma ɗan uwanta ɗan shekara 11 a gida kafin ta nufi tsohuwar makarantar da ta…
Read More