Kasashen Waje

Tattaunawar Trump da Netanyahu kan Iran: Babu wata matsaya da muka tsaida – Trump 

Tattaunawar Trump da Netanyahu kan Iran: Babu wata matsaya da muka tsaida – Trump 

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa ganawarsa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ba ta haifar da wata yarjejeniya tabbatacciya ba dangane da batun Iran, sai dai an amince da ci gaba da tattaunawa. Wannan shi ne karo na bakwai da shugabannin biyu suka gana cikin watanni 13 da suka gabata. Trump ya jaddada cewa, duk wata yarjejeniya dole ta tabbatar da cewa Iran ba za ta mallaki makamin nukiliya ko makamai masu linzami ba. Isra’ila na son tattaunawar ta wuce batun nukiliya kadai ta hada da makaman ballistic da kuma goyon bayan ƙungiyoyin da take ɗauka a matsayin barazana.…
Read More
Dubban jama’a sun fito zaɓen raba gardama a Bangladesh

Dubban jama’a sun fito zaɓen raba gardama a Bangladesh

Dubban jama’a sun fito zaɓen raba gardama a Bangladesh, a zaɓen da ake kallon sa a matsayin makomar sabuwar siyasa bayan kifar da tsohuwar Firaminista Sheikh Hasina a 2024 sakamakon bore na matasa (Gen Z). Mutane kusan miliyan 128 ne ke da rajistar kaɗa ƙuri’a, kuma zuwa rana ta tsaka, kaso 32.88% sun riga sun kaɗa ƙuri’unsu a yawancin cibiyoyin zaɓe 42,651. Zaɓen na fuskantar hamayya tsakanin kawancen jam’iyyun BNP ƙarƙashin Tariƙue Rahman da kuma Jamaat-e-Islami ƙarƙashin Shafiƙur Rahman. Hasashen ra’ayin jama’a na nuna BNP na da rinjaye. A birnin Dhaka, masu kaɗa ƙuri’a sun fara taruwa tun kafin buɗe…
Read More
Kamfanin tsaro na Amurka na neman damar bayar da tsaro a Gaza 

Kamfanin tsaro na Amurka na neman damar bayar da tsaro a Gaza 

Wani kamfanin tsaro na Amurka, UG Solutions, wanda a baya ya tura tsoffin sojoji ɗauke da makamai domin tsaron cibiyoyin rabon tallafi a Gaza, na tattaunawa da kwamitin “Board of Peace” na Shugaba Donald Trump kan sabuwar rawar da zai taka a yankin. Kamfanin ya bayyana hakan ne bayan rahotanni sun nuna yana ɗaukar ma’aikata masu iya Larabci da ƙwarewar yaƙi domin aiki a wuraren da ba a bayyana ba. Wata majiya mai masaniya kan shirin kwamitin ta tabbatar da cewa tattaunawar na gudana, ko da yake ba a cimma yarjejeniya ba tukuna. UG Solutions ya taɓa samar da tsaro…
Read More
Sabbin takardun Epstein da girman abinda yake ƙunshe a ciki

Sabbin takardun Epstein da girman abinda yake ƙunshe a ciki

Daga AISHA ASAS Fitar da sabbin takardu sama da miliyan uku kan shari'ar Jeffrey Epstein ya sake zama batu mafi tattaunawa a kafafen sada zumunta tare da tayar da hankulan al'umma fiye da ƙima, wanda hakan ya sa ya kasance lamarin da ya fi komawane tashe a wannan makon. Haka muka ya zama abu da ya sanya ɗimbin tambayoyi a zukatan dubatan mutane daga koina a faɗin duniya. Duk da cewa, Ma'aikatar Shari'a ta Amurka ta bayyana wannan bankaɗo takardun da ta yi a matsayin babban mataki na yunƙurin bayyana gaskiya, saidai masana doka da kuma shahararrun 'yan jaridu da…
Read More
Guterres ya sake matsa wa Isra’ila lamba kan kai agaji Gaza

Guterres ya sake matsa wa Isra’ila lamba kan kai agaji Gaza

Babban sakataren Majalisar ɗinkin Duniya, Antonio Guterres, ya sake kiran Isra’ila da ta gaggauta ba da damar shigar da kayan agaji Gaza, yana mai cewa abin da ke faruwa a yankin ya wuce rikicin siyasa zuwa bala’i na rashin jinƙai na duniya. Duk da sake buɗe mashigar Rafah, alkaluma daga hukumomin jinƙai sun nuna cewa adadin mutanen da ke fita domin neman magani ya yi ƙasa sosai idan aka kwatanta da buƙatar da ke akwai. Dubban marasa lafiya, musamman yara da tsofaffi, na jiran damar fita yayin da lokaci ke kara kurewa. Manyan jaridun duniya sun ruwaito cewa kusan dukkan…
Read More
Sojojin Pakistan sun kashe ‘yan bindiga 145 bayan kai masu hari

Sojojin Pakistan sun kashe ‘yan bindiga 145 bayan kai masu hari

Sojojin Pakistan sun ce sun kashe ’yan bindiga 145 bayan hare-haren da suka kashe kusan mutane 50. Wannan na daga cikin mafi girman hare-haren ramuwar gayya da gwamnati ta taɓa kaiwa a yankin. Jaridun duniya sun bayyana cewa rikicin Balochistan ya samo asali ne daga korafin rashin adalci, rabon arziki da siyasar tsakiya, wanda ke kara rikitar da matakan soja. Pakistan ta sake zargin Indiya da Afghanistan, yayin da kasashen ke musanta hannu a cikin kowanne irin rikici da ƙasar ke fuskanta.  Saidai duk da hakan lamarin na kara tsananta rikicin diflomasiyya a yankin Kudancin Asiya.
Read More
Uwa ba tare da hannuwa ba: Fuskar da ke bayyana irin matsanancin halin da mata da yara ke ciki a Gaza

Uwa ba tare da hannuwa ba: Fuskar da ke bayyana irin matsanancin halin da mata da yara ke ciki a Gaza

Nebal al-Hessi, wadda aka yanke hannuwanta, ta zama fuskar da ke bayyana irin matsanancin halin da mata da yara ke ciki a Gaza.  Labarinta ya fito a manyan kafafen yada labarai na duniya a matsayin misalin illar yaƙi ga fararen hula. Nebal ta bayyana yadda take kallon yaronta na girma ba tare da ta iya rungumarsa ba, ba tare da ta samu damar hidimta masa ba kamar yadda iya ke wa 'ya'yansu na daga al'ada. Lamarin wannan baiwar Allah na ƙara nuni da irin raunin kayan aƙaji da ake kai wa cikin Gaza da kuma girman bala’in da yankin yake…
Read More
‘Yan bindiga sun halaka ɗan Marigayi Gaddafi, Saif al-Islam a Libiya

‘Yan bindiga sun halaka ɗan Marigayi Gaddafi, Saif al-Islam a Libiya

Rahotanni daga ƙasar Libiya sun nuna cewa wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne, sun halaka Saif al-Islam Gaddafi, wanda ɗan tsohon shugaban ƙasar Marigayi Muammar Gaddafi ne. A cewar Al Jazeera ana ganin an harbe Saif al-Islam ne a yankin Zintan da ke Yammacin Libiya inda a nan yake zaune tsawon shekaru da dama. Kawo yanzu dai ba a san musabbabin kashe Saif al-Islam ba. Wata ‘yar uwarsa ta shaida wa gidan talabijin na ƙasar cewa ya mutu ne a kusa da iyakar ƙasar da Aljeriya, ba tare da bayyana ta yadda ya mutu ba. An daɗe ana ɗaukarsa…
Read More
Shugaban KAROTA ya nemi haɗin kan jama’a don inganta tsarin zirga-zirga a Kano

Shugaban KAROTA ya nemi haɗin kan jama’a don inganta tsarin zirga-zirga a Kano

Daga RABIU SANUSI a Kano Darakta Janar na Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) Injiniya Faisal Mahmud ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba hukumar cikakken haɗin kai domin ta samu damar aiwatar da ayyukanta yadda ya kamata wajen tabbatar da tsari da tsaro a kan hanyoyi. Injiniya Faisal Mahmud ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da manema labarai a ofishinsa da ke Kano, inda ya jaddada ƙudirin KAROTA na kare rayuka da dukiyoyin jama’a ta hanyar tabbatar da bin dokokin zirga-zirga a faɗin jihar. Ya ce haɗin kan direbobi, masu motocin haya…
Read More
Indiya ta tabbatar da samuwar cutar Nipah

Indiya ta tabbatar da samuwar cutar Nipah

*Kasar ta bayyana sabbin mutane biyu masu ɗauke da cutar Nipah a West Bengal Gwamnatin Indiya ta tabbatar da ɓullar sabbin cututtukan Nipah guda biyu a Jihar West Bengal da ke gabashin ƙasar, lamarin da ya janyo ƙarin tsauraran matakan binciken lafiyar matafiya a wasu ƙasashen kudu maso gabashin Asiya, musamman Thailand da Malaysia. Ma’aikatar Lafiya ta Indiya ta bayyana hakan ne a ranar 28 ga Janairu, 2026, inda ta ce an gano cututtukan tun daga watan Disamba, kuma ana ci gaba da sanya ido sosai domin hana yaɗuwar cutar. A cikin wata sanarwa, ma’aikatar ta gargadi jama’a da su…
Read More