Kasashen Waje

Sojojin juyin mulki a Nijar sun naɗa ministoci duk da gargaɗin ECOWAS

Sojojin juyin mulki a Nijar sun naɗa ministoci duk da gargaɗin ECOWAS

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Masu juyin mulkin jamhuriyar Nijar sun kafa sabuwar gwamnati duk da umarnin Ƙungiyar Ƙaya Tattalin Arzikin Ƙasashen Yammacin Afirka (ECOWAS). Shugabannin sojojin sun sanar da sabbin ministoci 21 a wata doka da aka karanta a gidan talabijin na ƙasar. Wannan dai na zuwa ne gabanin wani taron gaggawa da shugabannin ƙungiyar ECOWAS ta Yammacin Afirka suka yi kan juyin mulkin da aka yi a Nijar, bayan da hafsoshin sojin ƙasar suka bijirewa wa'adin da aka ba su na dawo da zavavven shugaban ƙasar. Janar Abdourahamane Tchiani ne ya sanar da sabuwar gwamnatin Nijar, wanda…
Read More
AU ta mara wa ECOWAS baya game da ƙudurorinta kan juyin mulkin Nijar

AU ta mara wa ECOWAS baya game da ƙudurorinta kan juyin mulkin Nijar

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Ƙasashen Afirka (AU) ƙarƙashin jagorancin Moussa Faki Mahamat, ta ce tana goyon bayan matakan da ECOWAS ta ɗauka kan Jamhuriyar Nijar ɗari bisa ɗari. AU ta bayyana goyon bayan nata ne ga ƙoƙarin da ECOWAS ke yi wajen maido da mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar Nijar wadda a yanzu take hannun sojojin juyin mulki. Faki Mahamat ya nuna damuwarsa dangane da rashin kulawar da hamɓararren shugaban Nijar, Mohamed Bazoum ke fuskanta a hannun sojojin da ke riƙe da shi. Cikin sanarwar bayan taron da AU ta fitar mai ɗauke da kwanan wata 10 ga Agusta, shugaban ƙungiyar…
Read More
Nijar ta yanke alaƙa da maƙwabciyarta Nijeriya

Nijar ta yanke alaƙa da maƙwabciyarta Nijeriya

Gwamnatin Jamhuriyar Nijar ƙarƙashin jagorancin sojijin juyin mulki, ta sanar da yanke alaƙa da Nijeriya bayan da ƙoƙarin ECOWAS na samar da maslaha a ƙasar ya ci tura. ECOWAS ta bai wa sojojin da suka yi juyin mulkin wa'adin mako guda a kan su maida Mohamed Bazoum kan kujerarsa ko kuma a yaƙe su da ƙarfin soji. A ranar Alhamis da ta gabata Shugaba Bola Tinubu a matsayinsa na Shugaban ƙungiyar ECOWAS, ya tura tawaga ta musamman ƙasar Nijar domin tattauna maslaha. Tawagar ta tafi Nijar ɗin ne ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya, Janar Abdulsalami Abubakar (rtd) inda ta gana…
Read More
Ruwan sama mafi ƙarfi cikin shekaru 140 ya haifar da mummunar ambaliya a ƙasar Sin

Ruwan sama mafi ƙarfi cikin shekaru 140 ya haifar da mummunar ambaliya a ƙasar Sin

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Chana sun ce, an samu ambaliya mai ƙarfi a wasu sassan ƙasar, musamman a yankunan Mentougou da Fangshan da ke birnin Beijing na kasar, sakamakon ruwan sama mai yawa da aka samu a yankunan da lamarin ya shafa. An ce ambaliyar ta yi sanadiyyar lalata matsugunnan al'ummar yankin da dama, ta kuma haifar da zaizayar ƙasa. Ɗan jarida daga ƙasar, Murtala Zhang, ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar Laraba cewa, "…mamakon ruwan sama da aka kwashe tsawon kwanaki ana yi, wanda ba a taɓa ganin irin ƙarfinsa ba a shekaru 140 da…
Read More
An cafke masu ƙoƙarin kitsa juyin mulki a Sierra Leone

An cafke masu ƙoƙarin kitsa juyin mulki a Sierra Leone

Daga BASHIR ISAH 'Yan sanda a ƙasar Sierra Leonean sun ce sun tsare mutane da dama, ciki har da jami'an soji waɗanda ke shirin kai harin tada zaune tsaye a ƙasar. Wannan na zuwa ne shekara guda bayan mummunan rikicin da ya auku a ƙasar a watan Agustan 2022, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 30. 'Yan sandan sun ce “Ɓangaren tsaron ƙasar na bibiyar bayanan sirri dangane da ayyukan wasu ɗaiɗaikun 'yan ƙasar, ciki har da sojoji waɗanda suke ƙoƙarin daburta zaman lafiya a ƙasar. Jami'an sun ƙara da cewa, waɗanda ake zargin sun shirya yin amfani da…
Read More
Harin ƙunar-baƙin-wake ya kashe mutum 44 a Pakistan

Harin ƙunar-baƙin-wake ya kashe mutum 44 a Pakistan

Daga BASHIR ISAH Rahotanni daga ƙasar Pakistan sun ce, aƙalla mutum 44 mutu sannan sama da 100 sun jikkata a wani mummunan hari da aka kai wajen wani taron siyasa a ƙasar. Jami'an yankin sun ce, sun gano wasu abubuwa da ke tabbatar da cewar harin na ƙunar-baƙin-wake ne. Harin ya auku ne a Arewa maso Yammacin gundumar Bajaur kuma a daidai lokacin da mambobin jam'iyyar Jamiat Ulema-e-Islam-Fazl (JUI-F) ke tsaka da taro. Bayanai sun ce, an kammala aikin ceto a wurin da aka kai harin bayan da jami'ai suka samu nasarar kwashe dukkan waɗanda suka jikkata zuwa aisibiti. Sai…
Read More
Juyin mulkin Nijar: Bazoum ya sha alwashin gwagwarmayar kare dimukraɗiyya

Juyin mulkin Nijar: Bazoum ya sha alwashin gwagwarmayar kare dimukraɗiyya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Muhammad Bazoum, Shugaban Ƙasar Nijar, wanda sojoji suka yi wa juyin mulki a ranar Laraba, ya ce, ya sha alwashin kare ribar dimokraɗiyya da suka sha yin gwagwarmaya a kai wajen nema wa al'ummar ƙasar 'yanci. Rahotanni sun ce, Mohamed Bazoum na tsare a hannun waɗanda suka shirya maƙarƙashiyar yi masa juyin mulki, waɗanda tun farko suka sanar da dakatar da duk wasu cibiyoyin gwamnati a ƙasar. Ita ma rundunar sojojin Nijar ta yi watsi da juyin mulkin da aka yi wa shugaban ƙasar. Babban hafsan sojin qasar ya ce, yana buƙatar "kiyaye mutuncin…
Read More
Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Sojoji sun kifar da gwamnatin Bazoum

Daga BASHIR ISAH Sojoji a ƙasar Nijar sun yi wa Shugaban Ƙasar, Mohamed Bazoum, juyin mulki ranar Laraba da daddare sa'o'i bayan da masu tsaronsa suka tsare shi a fadarsa. A jawabin da ya yi wa 'yan ƙasa kai tsaye a tashar talabijin ta ƙasar, Colonel-Major Amadou Abdramane ya bayyana cewa, “sojoji da sauran hukumomin tsaro sun yanke shawarar jawo ƙarshen gwamnatin da kuka sani. “Wannan ya biyo bayan ci gaba da taɓarɓarewar tsaron ƙasar da kuma rashin walwala da ingancin tattalin arziki," in ji shi. Sojojin sun ce an rufe iyakokin ƙsar, sannan an kafa dokar hana zirga-zirga a…
Read More

Yunƙurin juyin mulki: Fadar Shugaban Ƙasar Nijar ta yi ƙarin haske

Fadar Shugaban Ƙasar Jamhuriyar Nijar ta fitar da sanarwa dangane da halin da ake ciki na fargabar yiwuwar shirin juyin mulki a ƙasar inda ta tabbatar da cewa lallai an samu wasu sojoji da ke tsaron fadar shugaban ƙasar da suka ɗauki matakin da ya saɓa wa doka. A cewar sanarwar, sojojin da suka yi wannan yunƙuri ba su samu haɗin kan takwarorinsu da ke tsaron fadar ba, kuma a halin da ake ciki Shugaba Bazoum Mohamed da iyalinsa na cikin ƙoshin lafiya. Rundunar sojin Nijar ta ce a shirye take ta ɗauki matakin murƙushe dukkanin waɗanda suke da hannu…
Read More