Yunƙurin juyin mulki: Fadar Shugaban Ƙasar Nijar ta yi ƙarin haske

Spread the love

Fadar Shugaban Ƙasar Jamhuriyar Nijar ta fitar da sanarwa dangane da halin da ake ciki na fargabar yiwuwar shirin juyin mulki a ƙasar inda ta tabbatar da cewa lallai an samu wasu sojoji da ke tsaron fadar shugaban ƙasar da suka ɗauki matakin da ya saɓa wa doka.

A cewar sanarwar, sojojin da suka yi wannan yunƙuri ba su samu haɗin kan takwarorinsu da ke tsaron fadar ba, kuma a halin da ake ciki Shugaba Bazoum Mohamed da iyalinsa na cikin ƙoshin lafiya.

Rundunar sojin Nijar ta ce a shirye take ta ɗauki matakin murƙushe dukkanin waɗanda suke da hannu a yunƙurin saɓa wa dokar da aka yi a baya-bayan nan, muddin ba su gaggauta tuba ba.

Da safiyar ranar Laraba jami’an tsaron da lamarin ya shafa suka ɗauki matakin datse hanyar da ke kaiwa Fadar Shugaban Ƙasar a cikin wani yanayi da ake fargabar mai yiwuwa na barazanar juyin mulki ne.

By Editor