Kasashen Waje

Rikicin soja a Sudan ta Kudu: Sojojin gwamnati sun umurci farar hula da ma’aikatan agaji su fice daga yankunan

Rikicin soja a Sudan ta Kudu: Sojojin gwamnati sun umurci farar hula da ma’aikatan agaji su fice daga yankunan

Sudan ta Kudu na fuskantar rikici mai tsanani yayin da sojojin gwamnati suka bayar da umurnin gaggawa ga farar hula da ma’aikatan Majalisar ɗinkin Duniya (UNMISS) da NGOs su fice daga yankunan Jonglei. Wannan mataki ya biyo bayan ƙara tsananta rikicin sojojin gwamnati da ‘yan adawar SPLA‑IO, inda hare-hare suka fi yawa a Nyirol, Akobo da Uror. Gwamnatin ta bayyana cewa matakin na da nufin kare rayuka da dukiyoyin jama’a, tare da dawowa da oda a yankuna masu rikici. Sai dai Majalisar ɗinkin Duniya ta yi gargadin cewa wannan mataki zai iya jefa dubban farar hula cikin haɗari, yayin da…
Read More
Ranar International Holocaust Remembrance: Duniya ta tuna mummunan kisan da aka yi a yammacin Turai

Ranar International Holocaust Remembrance: Duniya ta tuna mummunan kisan da aka yi a yammacin Turai

International Holocaust Remembrance Day, rana ce da ake tuna wa da kisan kiyashi da aka yi wa miliyoyin mutane a lokacin Yaƙin Duniya na II, musamman a sansanin Auschwitz da sauran wurare. Ana gudanar da taron addu’a, ƙona kyandir, da karatun tarihi a birane kamar Berlin, London, New York da Warsaw. Masana tarihi da shugabanni suna jaddada darussan baya a matsayin hanyar ƙarfafa zaman lafiya, mutunta bambance-bambance da hana faruwar irin wannan ɓarna a nan gaba. “Tarihi ya koya mana cewa rashin mutunta juna da wariya na haifar da ɓarna; duniya na buƙatar zaman lafiya da adalci,” inji wani malami…
Read More
Aƙalla Mutane 5,777 sun rasa rayukansu a Iran – Rahoton Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam

Aƙalla Mutane 5,777 sun rasa rayukansu a Iran – Rahoton Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam

Kungiyar masu rajin kare haƙƙin ɗan adam mai suna Human Rights Activists News Agency ta fitar da rahoto cewa “jami’an tsaro na Iran sun kashe aƙalla mutane 5,777, ciki har da yara ƙanana 86, yayin da ake ƙoƙarin murƙushe zanga‑zangar lumana da ƙaruwar adawa da gwamnati.” Wannan rahoto ya kuma nuna cewa aƙalla mutane kusan 42,000 an kama su yayin rikicin da ya ɗauki hankali a cikin 'yan watanni.  Rahoton ya jawo cece‑kuce sosai, inda ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan adam ke bayyana cewa ana amfani da makamai da ƙarfi fiye da kima wajen murƙushe ‘yan adawa, lamarin da ya jawo…
Read More
An tilasta Falasɗinawa fiye 37,000 barin gidajensu a 2025 – Majalisar Dinkin Duniya 

An tilasta Falasɗinawa fiye 37,000 barin gidajensu a 2025 – Majalisar Dinkin Duniya 

A cikin wani rahoton da ƙungiyar Majalisar ɗinkin Duniya ta fitar a ranar Talata, an bayyana cewa fiye da 37,000 Falasɗinawa ne aka tilasta su barin gidajensu a shekarar 2025 a Yammacin Banki (West Bank), yawanci dalilin irin aayyukan ɓarna da sojojin Isra’ila ke aikatawa da sunan matakan tsaro waɗanda suka shafi sansanonin ‘yan gudun hijira. Wannan adadi ya jawo ƙarin damuwa daga ƙasashen duniya, waɗanda ke kira ga ɗaukar matakin rage tashin hankali da tallafa wa waɗanda rikicin ya shafa.  Rahoton ya ce wannan ƙaura ta tilastawa ta faru ne a lokacin da ake ƙoƙarin sake ƙoƙarin kwaɗaita zaman…
Read More
Tsohon Shugaban Philippines na fuskantar tuhume-tuhumen laifukan yaƙi

Tsohon Shugaban Philippines na fuskantar tuhume-tuhumen laifukan yaƙi

Kotun Harkokin Laifuka ta Duniya (ICC) ta yanke hukuncin cewa tsohon shugaban ƙasar Philippines, Rodrigo Duterte, yana da lafiya da hankali da zai iya halartar zaman tabbatar da tuhuma da ake yi masa a kotun, dangane da zargin aikata laifukan yaƙi da tu'ammali da muyaggun kwayoyi tare da cin zarafin ɗan adam.  Wannan hukunci ya tabbatar da cewa da yiwar a ɗage zaman tabbatar da tuhuma da aka shirya a ranar 23 Fabrairu 2026, domin isa kai tsaye a shari’a kan laifukan da ake zargin ya aikata.  Masu rajin kare haƙƙin ɗan adam da masu sharhi sun bayyana wannan mataki a matsayin…
Read More
Yaƙi da raguwar haihuwa: Chana ta kakaɓa haraji kan kondon da magungunan hana ɗaukar ciki 

Yaƙi da raguwar haihuwa: Chana ta kakaɓa haraji kan kondon da magungunan hana ɗaukar ciki 

A wani sabon mataki da ya ɗauki hankulan duniya, gwamnatin ƙasar Chana ta kakaɓa harajin kashi 13 cikin 100 kan kayayyakin hana ɗaukar ciki kamar kondon da kwayoyin hana ɗaukar ciki, a wani yunƙuri na daƙile raguwar haihuwa da ke ƙara tsananta a ƙasar. Sabon tsarin, wanda ya fara aiki tun 1 ga Janairu, ya kawo ƙarshen rangwamen haraji da aka shafe kusan shekaru 30 ana amfani da shi, tun daga shekarar 1994, lokacin da Chana ke tsaurara manufofinta na rage yawan jama’a ta hanyar tsarin haihuwa ɗaya. Yanzu haka, duk wani magani ko wata hanya ta hana ɗaukar ciki…
Read More
Kama Shugaban Venezuela: Rasha da Iran sun yi Allah-wadai, EU Ta nemi a mutunta dokokin ƙasa da ƙasa

Kama Shugaban Venezuela: Rasha da Iran sun yi Allah-wadai, EU Ta nemi a mutunta dokokin ƙasa da ƙasa

Gwamnatin Amurka ta bayyana cewa ta kama Shugaban Venezuela, Nicolás Maduro, a wani mataki da ya ƙara tayar da ƙura a siyasar duniya, musamman a yankin Latin Amurka. Hukumomin Amurka sun ce an kai Maduro New York domin fuskantar shari’a a kotun tarayya bisa zargin safarar miyagun ƙwayoyi da ta’addanci. Shugaban Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da kama Maduro, inda ya ce an gudanar da aikin ne cikin tsari mai tsauri, ba tare da asarar rayuka ba. A cewarsa, jami’an tsaro sun fuskanci ƙalubale masu yawa kafin samun nasarar kama shugaban. A cewar Ma’aikatar Shari’ar Amurka, tuhumar da ake yi…
Read More
Duk da Allah-wadai, Chana na kallon harin Amurka a Venezuela a matsayin dama a rikicin ta da Taiwan 

Duk da Allah-wadai, Chana na kallon harin Amurka a Venezuela a matsayin dama a rikicin ta da Taiwan 

Masana harkokin tsaro da siyasar duniya sun bayyana cewa matakin da Shugaban Amurka Donald Trump ya ɗauka na kai farmaki a Venezuela tare da kama Shugaba Nicolás Maduro na iya zama babban darasi kuma wata dama ga ƙasar Chana, duk da cewa Beijing ta yi kakkausar suka kan harin. A cewar masana, irin wannan mataki da Amurka ta ɗauka zai iya ƙarfafa Chana ta sake duba dabarunta na tsoma baki ta ƙarfi a yankinta, musamman game da Taiwan da kuma Tekun Kudancin Chana, inda ake ta fama da rikice-rikicen ikon mallaka. Rahotanni sun nuna cewa duk da furucin Chana a…
Read More
Netanyahu zai gana da Trump kan mataki na biyu a shirin Gaza

Netanyahu zai gana da Trump kan mataki na biyu a shirin Gaza

Firaminista Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa mataki na biyu na shirin Amurka na kawo ƙarshen yaƙin Gaza ya kusan kaiwa ga aiwatarwa, duk da cewa akwai muhimman batutuwa da ba su warware ba — musamman batun ko za a tura sojojin ƙasashen duniya a matsayin dakarun tsaro a Gaza. Netanyahu ya faɗi haka ne yayin taronsa da Shugaban gwamnatin Jamus, Friedrich Merz, a birnin Urushalima. Ya ce zai gudanar da muhimmiyar tattaunawa da Shugaban Amurka Donald Trump a ƙarshen wata domin tabbatar da yadda mataki na biyu zai tabbata. Fadar Firaminista Isra’ila ta tabbatar a ranar 1 ga Disamba…
Read More
Shuwagabanni masu goyon bayan Ukraine za su yi taro ta yanar gizo

Shuwagabanni masu goyon bayan Ukraine za su yi taro ta yanar gizo

Fadar shugaban ƙasar Faransa ta tabbatar cewa gungun ƙasashen da ake kira Coalition of the Willing — ƙungiyar da ke ba Ukraine cikakken goyon baya — za su gudanar da wani taro a ranar Alhamis mai zuwa ta hanyar bidiyo. Taron, wanda Birtaniya da Faransa ke jagoranta, zai samu hallarar shugaban gwamnati na Birtaniya Keir Starmer, da Shugaban Ukraine Volodymyr Zelenskiy. Downing Street ta tabbatar da shiga taron. Zelenskiy ya ce Ukraine na shirin gudanar da tattaunawa da jami’an Amurka kan batun sake gina ƙasar da ci gaban tattalin arziki, a wani ɓangare na shirin zaman lafiya da Rasha.
Read More