Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo ta sake tsintar kanta a tashin hankali sakamakon annoba mai tayar da hankali ta sake bayyana a gabashin Kongo bayan wata jaririya mai suna Buswaza ta rasa ranta sakamakon cutar Ebola, lamarin da ya sake fito da irin haɗarin da yara ƙanana da jarirai ke fuskanta a yayin barkewar wannan muguwar cuta.
Rahotanni sun bayyana cewa bayan rasuwar mahaifiyarta a karshen watan Mayu, an kai Buswaza zuwa wani gidan marayu da Cocin Kirista ke gudanarwa a garin Bunia. Sai dai ba da jimawa ba limaman mata masu kula da gidan suka lura cewa jaririyar na fama da zazzaɓi. Cikin ‘yan kwanaki kadan kuwa ta rasu, daga bisani aka tabbatar cewa cutar Ebola ce ta yi sanadin mutuwarta.
Masu kula da gidan marayun da jami’an lafiya sun bayyana cewa bayan mutuwar Buswaza, an gano karin wasu jarirai shida a cikin gidan marayu mai dauke da yara 69 da ake zargin suna ɗauke da cutar Ebola. Gidan yana cikin garin Bunia na lardin Ituri, wanda a halin yanzu shi ne cibiyar da annobar ta fi ƙamari a Kongo.
An garzaya da jariran zuwa asibiti domin gudanar da gwaje-gwaje da kula ta musamman. Daga bisani an tabbatar cewa biyar daga cikinsu ba su dauke da cutar, inda aka sallame su daga tantin killace masu zargin kamuwa da Ebola a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Eɓangelical Medical Centre (CME). Jami’an lafiya sanye da kayan kariya na musamman ne suka sallame su cikin farin ciki, yayin da limaman mata suka bayyana godiyarsu.
