Adabi

Marubuta sun shirya taron taya Aminu Ala murnar naɗin sarautar Sarkin Adabin ƙasar Hausa 

Marubuta sun shirya taron taya Aminu Ala murnar naɗin sarautar Sarkin Adabin ƙasar Hausa 

Daga MUKHTAR YAKUBU  Gamayyar marubuta a ƙarƙashin ƙungiyar marubuta ta Kano Literary Space sun shirya Gagarumin Bikin Taya Murna ga Sarkin Adabin Harshen Hausa Dr. Aminu Alan Waƙa wanda a kwanakin baya Sarkin Daura Alhaji Umar Farouk ya naɗa shi sarautar Sarkin Adabin ƙasar Hausa. Taron mai taken ‘Adabi Mabuɗin Al'adu’, an gudanar da shine a ranar Asabar, 28 ga Maris, 2026, a da ɗakin taro na CITAD dake birnin Kano, inda manyan masana harshen Hausa da adabi suka gabatar da jawabai da waƙoƙi akan abubuwan da suka shafi tarihi da kuma al'adunmu na gargajiyar Hausa. Tun da farko da…
Read More

Duk Ramadan muna tafiya hutun labarai don ibada – Zainab Abdullahi

“Yadda ayyukan marubuta a cikin Ramadan ke kasancewa” Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A kowacce shekara a lokaci irin wannan na Ramadan, al’ummar Musulmi a ko'ina a cikin duniya suna shagaltuwa da ayyukan ibada da neman kusanci da Allah (SWT). Marubuta adabin Hausa su ma sukan jingine ayyukan rubuce-rubuce na nishaɗi da faɗakarwa da suke yi, zuwa ga tilawar Alƙur'ani, da faɗakarwa kan al'amuran addini, da koyar da girke-girke ga mata. A irin wannan lokaci mambobin ƙungiyar marubuta ta Jajirtattu Writers Association suna ware tsawon watan Ramadan don gudanar da shirye-shirye da suka shafi tambayoyin Musulunci da karatun Alƙur'ani. Wannan wani…
Read More
Ayyukan marubuta a cikin watan Ramadan 

Ayyukan marubuta a cikin watan Ramadan 

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Duk watan Ramadan mu kan tafi hutu daga fitar da labarai don yin ayyukan ibada - Zainab Abdullahi A kowacce shekara a lokaci irin wannan na Ramadan, musulmi a ko'ina a duniya na shagaltuwa da ayyukan ibada da neman kusanci da Allah, marubuta adabin Hausa su ma sukan jingine ayyukan rubuce-rubuce na nishaɗi da faɗakarwa da suke yi, zuwa ga tilawar Alƙur'ani, da faɗakarwa kan al'amuran addini, da koyar da girke-girke ga mata. A irin wannan lokaci mambobin ƙungiyar marubuta ta Jajirtattu Writers Association suna ware tsawon watan Ramadan don gudanar da shirye-shirye da suka shafi…
Read More
Aminu Alan Waƙa: Bikin naɗin Sarkin Adabi na farko a Daura ya yi armashi 

Aminu Alan Waƙa: Bikin naɗin Sarkin Adabi na farko a Daura ya yi armashi 

Daga KHALID IMAM Waƙoƙin Alan Waƙa tamkar wani madubi ne na duban harshen Hausa da adabi - Mai Martaba Sarkin Daura Masarautar Daura ta yi cikar kwari sakamakon dandazon dubban masoya da ɗaruruwan 'yan uwa da abokan arziki da suka halarci naɗin Dakta Aminu Ladan Abubakar Alan Waƙa a matsayin Sarkin Adabin Harshen Hausa na farko a tarihi. Wannan babban al’amari na tarihi a ƙasar Hausa  ya faru ne a Masarautar Daura a daidai lokacin bikin naɗi mai cike da ban ƙaye da armashi, Mai Martaba Sarkin Daura, Alhaji Dakta Umar Farouk Umar CON ya cicciɓa darajar Adabi da ma'abota…
Read More
Kishin harshen Hausa ya sa na ƙirƙire baƙaƙe da lambobi na Hausa – Sadar Musa

Kishin harshen Hausa ya sa na ƙirƙire baƙaƙe da lambobi na Hausa – Sadar Musa

"Na fuskanci ƙalubale musamman na sare min gwiwa da mutane ke yi" Daga AISHA ASAS  (Ci gaba daga makon jiya) MANHAJA: Kowanne abu yana da tsari da kuma matakalai da ake bi don ganin an kai ga nasara, musamman ma harkar irin wannan ta ilimi. Shin waɗanne matakai ne aka taka don ganin wannan aiki ya kai ga nasara? SADAR: Gaskiya ne shi ya sa tashin farko dana kammala wannan aikin na yi ƙoƙarin kauce wa 'media' ko yanar gizo, saboda a wannan lokacin bani da tabbacin me mutane za su faɗa akai, sai na fara haɗa kwamiti na mutane…
Read More
Arewa na fuskantar ƙalubalen karatu, musamman ta fuskar tsaro – Jamila Mu’azu Abubakar 

Arewa na fuskantar ƙalubalen karatu, musamman ta fuskar tsaro – Jamila Mu’azu Abubakar 

"Babban ƙalubalen dake akwai dama bai wuce salon da ake amfani da shi wajen koyarwa ba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  (Ci gaba daga makon jiya) Jajirtattun mata masu ƙwazo da himma kan duk abin da suka sa a gaba, su ne ake kira da Kallabi Tsakanin Rawwuna. Ba domin komai ba kuwa, sai don ƙoƙarin su da rawar ganin da suke takawa, wanda ko a cikin maza ma sai an tona kafin a dace da mai jarumtarsu. Hajiya Jamila Mu’azu Abubakar ɗaya ce daga cikin irin waɗannan matan da ake yi wa laƙabi da Giwar Mata. ƙwararriya ce kuma jajirtacciya…
Read More
Hausa babbar harshe ce da ke da rinjayen masu amfani da ita a Afrika – Sadar Musa

Hausa babbar harshe ce da ke da rinjayen masu amfani da ita a Afrika – Sadar Musa

"Shekaru shida na kwashe Ina aikin samar da baƙaƙen Hausa da lambobi" Daga AISHA ASAS Idan ana zancen baiwa ta rubutu,  ba na jin a faɗin Nijeriya akwai inda ya kai Arewa yawaitar marubuta da za a iya buga ƙirji a kira su da gwanaye, watakila namijin ƙoƙarin da suke yi ne ya haifar da wanzuwa da kuma raya yaren Hausa ga masu tasowa duk da irin horo da ruɗin da yaren Ingilishi ke yi a ƙwaƙwalensu. A cikin irin wannan ƙoƙari, aka samu wani matashi da ya yi kishin ƙirƙirar baƙaƙe da kuma lambobi da malam bahaushe zai buge…
Read More
Na fara tunanin kafa makaranta ne lokacin da zan sa ‘yata karatu – Jamila Mu’azu Abubakar 

Na fara tunanin kafa makaranta ne lokacin da zan sa ‘yata karatu – Jamila Mu’azu Abubakar 

"Nasarorin da na samu na da nasaba da jajircewar da mahaifinmu ya yi kan ilimi" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Jajirtattun mata masu ƙwazo da himma kan duk abin da suka sa a gaba, su ne ake kira da Kallabi Tsakanin Rawwuna. Ba domin komai ba kuwa, sai don ƙoƙarin su da rawar ganin da suke takawa, wanda ko a cikin maza ma sai an tona kafin a dace da mai jarumtarsu. Hajiya Jamila Mu’azu Abubakar ɗaya ce daga cikin irin waɗannan matan da ake yi wa laƙabi da Giwar Mata. ƙwararriya ce kuma jajirtacciya kan fagen da aka fi saninta…
Read More
Nasarata a Gasar Tsangayar Gusau ce ta ba ni lasisin amsa sunan marubuciya  – Ummi Abba

Nasarata a Gasar Tsangayar Gusau ce ta ba ni lasisin amsa sunan marubuciya  – Ummi Abba

"Ko yau na ajiye alƙalami zan iya cewa kwalliya ta biya kuɗin sabulu" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Akwai marubutan Hausa da dama dake bayar da gudunmawa sosai ga cigaban rubutun Adabi, sai dai ba kasafai ka ke jin amon su daga Jihar Borno ba, duk kuwa da kasancewar akwai marubuta da dama da suka shahara daga wannan yankin. Fatima Abba Muhammad, ba sunanta ne kawai ya bayyana ba, ta kasance ma a cikin gwarazan da suka yi fice a Gasar Tsangayar Gusau, ɗaya daga cikin manyan gasannin marubutan Hausa da ake sa su a Arewacin Nijeriya, inda ta samu nasara…
Read More
Alaƙar da ke tsakanin rubutun adabi da aikin jarida alaƙa ce irin ta Ɗanjuma da Ɗanjummai – Umar Yunus Jos

Alaƙar da ke tsakanin rubutun adabi da aikin jarida alaƙa ce irin ta Ɗanjuma da Ɗanjummai – Umar Yunus Jos

"Dlilin da ya ja hankalin maza suka duƙufa rubuce a baya nake fatan ya dawo nan gaba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Harkar rubutun adabin Hausa, harka ce mai faɗin gaske wacce ta tattaro mutane daban-daban, daga ɓangarorin ilimi da rayuwa mabambanta. Ba mamaki ba ne ka ga malamin makaranta marubuci, ko jami'in tsaro, ɗan siyasa, injiniya, lauya ko likita da sauransu, suna ba da gagarumar gudunmawa cikin harkar rubutun adabi. Umar Yunus na daga cikin irin waɗannan fasihan mutane waɗanda ke bai wa adabi gudunmawa a ɓoye da zahiri, duk da kasancewar sa ɗanjarida, kuma malamin makaranta, mai sha'awar harkokin…
Read More