06
Feb
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Alhassan Dantata, fitaccen attajiri a fadin nahiyar Afirika ta yamma, wanda tushen arzikinsa ya samo asali daga sayar da Goro da Gyada. Haihuwa da nasaba; Alhassan Dantata ya fito ne daga cikin zuri’ar Agalawa, iyayensa fatake ne masu yawon kasuwanci daga wannan gari zuwa wancan. An haife shi a shekarar 1877, a wani qaramin qauye da ake kira Danshayi a garin Bebeji, wanda ke da tazarar aqalla kilomita goma sha-biyar daga garin Kano. Alhasan daya ne daga cikin ’ya’yan Abdullahi wanda matarsa Fatima da ake kira Amarya ta haifa. Shi Abdullahi da ne ga wani mutum…