01
May
Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kyautata wa rayuwar ma'aikatan jihar. Ya bayyana haka ne a wajen taron bikin Ranar Ma'aikata na bana wanda aka saba gudunarwa ran 1 ga Mayun kowace shekara. Bikin bana a jihar ya gudana ne a ranar Laraba a Sakatariyar JB Yakubu, Gusau, babban birnin jihar. Cikin sanarwar da ta fitar, Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce gwamnatin jihar ba za ta baro ma'aikatan jihar a baya wajen gudanar da harkokinta. Sulaiman ya rawaito Lawal na cewa, “Gwamnatina na sane da muhimmiyar rawar da ma'aikata ke…