Editor

9328 Posts
Ranar Ma’aikata: Gwamnan Zamfara ya jaddada ƙudurinsa na kyautata rayuwar ma’aikatan jihar

Ranar Ma’aikata: Gwamnan Zamfara ya jaddada ƙudurinsa na kyautata rayuwar ma’aikatan jihar

Daga BASHIR ISAH Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada ƙudurin gwamnatinsa na kyautata wa rayuwar ma'aikatan jihar. Ya bayyana haka ne a wajen taron bikin Ranar Ma'aikata na bana wanda aka saba gudunarwa ran 1 ga Mayun kowace shekara. Bikin bana a jihar ya gudana ne a ranar Laraba a Sakatariyar JB Yakubu, Gusau, babban birnin jihar. Cikin sanarwar da ta fitar, Kakakin Gwamna, Sulaiman Bala Idris, ya ce gwamnatin jihar ba za ta baro ma'aikatan jihar a baya wajen gudanar da harkokinta. Sulaiman ya rawaito Lawal na cewa, “Gwamnatina na sane da muhimmiyar rawar da ma'aikata ke…
Read More
A saka hankali yayin zaɓin aure

A saka hankali yayin zaɓin aure

Assalam alaikum. Da fatan kowa ya yi sallah lafiya? Allah ya albarkaci Jaridar Blueprint Mahaja. A yau zan yi wasiƙa ne a kan zaɓin ma'aurata, domin shi ne babban abin da ke ci wa kowa tuwo a ƙwarya a halin yanzu. Wanda kuma hakan ke jawo yawan mace-macen aure, domin ana auren ne kawai barkatai ba tare da sanin wa ya kamata a aura ba. Babban hadafin da ya ke sanya mu zaɓar wanda zamu rayuwa da shi ko wacce zamu rayu da ita a matsayin rayuwar aure shi ne samun nutsuwar rayuwa, shi kuwa samun nutsuwar ruhi da abokiyar…
Read More
1 ga Mayu sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki – Gwamnati

1 ga Mayu sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki – Gwamnati

*Ba mu amince da ƙarin albashin kashi 35 ba — NLC Daga BSHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta ba da tabbacin cewa sabon albashi mafi ƙaranci zai fara aiki daga 1 ga Mayu. Kodayake, Gwamnatin ta ce kwamitin da ke da ruwa da tsaki kan batin ƙarin albashin bai kammala aikinsa ba tukuna. Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Nkeiruka Onyejeocha, ita ce ta yi wannan babayin a wajen taron bikin Ranar Ma'aikata da aka shirya ranar Laraba a Abuja. Ta ce abin takaici ne ƙarin albashin bai kammalu ba zuwa wannan lokaci, amma cewa ana ci gaba da tattaunawa domin tabbatar dukkanin bayanai…
Read More
Shawara ga ‘yan uwa mata

Shawara ga ‘yan uwa mata

Daga SALIHA ABUBAKAR ABDULLAHI Assalamu alaikum. 'Yan uwa mata barkanmu da wannan lokaci. Allah Ya shirya mana zuri'a bakiɗaya. Zan yi amfani da wannan damar da na samu wurin yi mana tuni da kuma lurar da mu kan muhimmancin tarbiyya musamman a wannan zamanin da muka samu kanmu. Shawarata gare mu 'yan uwa mata dukka, duba da irin yanayin da muke ciki yanzun na taɓarɓarewar tarbiyya, 'yan uwa mu farka daga barci, mu san ƙima da darajojin da Allah SWT yai mana ba kaɗan ba ne, mu san ciwon kanmu, mu tashi tsaye wajen ganin ɗiyanmu sun samu tarbiyya ta…
Read More
Ki kame kanki ’yar uwa!

Ki kame kanki ’yar uwa!

A wannan zamani da muka tsinci kawunanmu ciki, mace wacce ta kame kanta daga aikata alfasha da nesantar shiga ta bayyana tsiraici, da ƙin kula samarin banza bisa hanya, ita ake wa kallon mace mai girman kai. To duk irin abinda al'ummah za su ce a kanki matuƙar kin kiyaye dokokin Allah, da yin koyi da mata salihan bayi na zamanin Manzon Allah (SAWW), kar ki tava damuwa, duk mai ƙaunarki da gaskiya, to ya bi tsarin neman aure yadda addini ya shar'anta domin ke ma'abociyar tsadace. Bayyana tsiraici alamu ne na fushin Allah, shi ya sa lokacin da Allah…
Read More
Wanne darasi karatun littattafai ke koyarwa?

Wanne darasi karatun littattafai ke koyarwa?

Tare da ABBA ABUBAKAR YAKUBU Littafi abu ne mai muhimmanci ga rayuwar ɗan adam, duba da yadda littafi ke taimakawa wajen adana muhimman bayanai da labarai da suka jiɓanci harkokin rayuwa daban-daban, kama daga tarihi, bayanan da suka shafi harkokin kimiyya da fasaha da tattalin arziki, tarihin ƙasa da muhimman mutane da al'adu da sauransu. Ranar littafi da kare 'yancin mallakar fasaha ta duniya ta samo asali ne tun a shekarar 1616 lokacin da aka yi rashin wasu fitattun marubuta irinsu Cervants, da Sharkspare da Inca Garcilaso de La vega. Kana a shekarar ce kuma aka samu wanzuwar wasu fitattun…
Read More
Ranar Ma’aikata: Gwamnati ta ayyana 1 ga Mayu, ranar hutu ga ma’aikata

Ranar Ma’aikata: Gwamnati ta ayyana 1 ga Mayu, ranar hutu ga ma’aikata

Daga BASHIR ISAH Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranar Laraba, 1 ga watan Mayu, a matsayin ranar hutun gama-gari albarkacin Bikin Ranar Ma'aikata na bana. Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin sanarwar da Babban Sakataren Ma'aikatar Cikin Gida, Dr Aishetu Ndayako, ta fitar ranar Talata a Abuja. Aishetu ta ce, Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr Olubunmi Tunji-Ojo ne ya ayyana ranar hutun a madadin Gwamnatin Tarayya. Tunji-Ojo ya jaddada buƙatar aiki da ƙwazo a ɗaukacin ɓangarorin ƙwadago, kana ya ƙara haskaka ƙudurin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na ƙoƙarin samar da walwala ha ma'aika da kuma son ganin ma'aikata sun zamo masu…
Read More
Ta ya za ku iya ƙara wa ƙwaƙwalwarku kaifi?

Ta ya za ku iya ƙara wa ƙwaƙwalwarku kaifi?

Daga AISHA ASAS Mai karatu barkanmu da sake kasancewa tare. A wannan makon shafin kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja zai yi duba ne kan muhimmin abu da lafiyar jikinmu ke buƙata ko in ce jiki ke buƙata don tabbatar da gudanar da ayyukan yau da kullum ba tare da matsala ba. Ba komai nake magana kai ba face kaifin ƙwaƙwalwa. Ƙwaƙwalwar ɗan adam wata halitta ce mai cike da abin ban mamaki, kuma muhimmancinta ga jikin mutum lamari ne mai gima. Duba da cewa kusan kowacce gava ta jikin ɗan adam tana da hedikwata a ƙwaƙwalwa, wadda daga can ne…
Read More
Za mu gurgunta samar da fetur muddin ba a biya mu bashin N200bn ba — IPMAN

Za mu gurgunta samar da fetur muddin ba a biya mu bashin N200bn ba — IPMAN

Daga BASHIR ISAH Ƙungiyar Masu Dakon Fetur ta Nijeriya (IPMAN), ta yi barazanar gurgunta samar da fetur afaɗin ƙasa muddin ba a biya ta bashin Naira biliyan 200 da take bi ba. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ƙarancin fetur ke ci gaba da ta'azzara lamarin da ya yi sanadiyar ƙarin farashin fetur a sassan ƙasa, inda a yanzu ake sayar da fetur tsakanin N610 da N800 kan lita guda a wasu wurare, sannan N1000 zuwa N1200 a kasuwar bayan fage. Jigo a IPMAN, Mazi Oliver Okolo ne ya yi wannan barazanar, kuma cewa da goyon bayan shugabancin…
Read More
Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Emefiele ba ya bayar da kwangila sai da cin hanci, in ji shaida

Daga BASHIR ISAH Mutum na biyu da ke ba da shaida a kan shari'ar da tsohon Gwamnan CBN, Godwin Emefiele ke fuskanta, ya bayyana wa Kotu ƙarara cewa lallai Emefiele ba ya ba da kwangila ba tare da ya karɓi cin hanci ba. John Ayo wanda ya kasance tsohon Darakta na Sashen Labarai na CBN, ya bayyana haka ne ga Babban Kotun da ke zamanta a Ikeja, Jihar Legas. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake ba da shaida a gaban Alƙali Rahman Oshodi yayin zaman da kotun ta yi a ranar Litinin. Emefiele na fuskantar shari'a ne kan…
Read More