Editor

9513 Posts
SERAP ta sake maka gwamnonin jihohi 36 da ministan Abuja a kotu

SERAP ta sake maka gwamnonin jihohi 36 da ministan Abuja a kotu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙungiyar Fafutukar Yaƙi da Cin Hanci a Nijeriya, SERAP, ta kai ƙarar gwamnonin jihohin ƙasar 36 da Ministan Birnin Tarayya, Abuja, saboda zarginsu da gaza yin bayanin yadda suka kashe maqudan kuɗaɗen da suka samu daga kason Asusun Tarayya na FAAC, tun daga shekarar 1999. Cikin wata sanarwar manema labarai da mataimakin daraktan ƙungiyar, Kolawole Oluwadare ya fitar ranar Lahadi, ya ce qungiyar ta ɗauki matakin ne sakamakon rahoton da ta samu cewa a cikin watan Maris FAAC ta raba Naira Tiriliyan 1.123 tsakanin gwamnatin tarayya da na jihohi da ƙananan hukumomi. Ƙunhiyar ta ce, haka…
Read More
Abubuwan da suke nuna ka samu sana’a mai kyau – Likitan Sana’a

Abubuwan da suke nuna ka samu sana’a mai kyau – Likitan Sana’a

Daga AMINA YUSUF ALI A tattaunawarmu da Badamasi Aliyu Abdullahi wanda aka fi sani da likitan sana'a, wanda ƙwararre ne a kan sanin madafa da mafita a game da sana'o'i da dabarun bunƙasa tattalin arziki. Ya bayyana mana wasu hanyoyi da mai sana'a zai gane cewa sana'ar da yake ciki ko aikin da yake yi sana'a ce ko aiki ne mai kyau da ya dace da shi. A tattaunawar ga wasu dalilai da ya kawo. Idan kana shauƙin ta. Son sana'arka shi ne tubalin gina ta da yin haƙuri da juriya da kasuwanci ke buƙata. Idan ba soyayyar abinda ka…
Read More
Gwamnatin Kaduna za ta tallafi manoman citta a jihar

Gwamnatin Kaduna za ta tallafi manoman citta a jihar

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni sun bayyana cewa, Gwamnatin Kaduna tare da hukamar gwamnatin Tarayya za su tallafa wa manoman citta da suka tafka hasara a kakar bara Gwamnatin Kaduna tare da hukamar gwamnatin Tarayya za su tallafa wa manoman citta da suka tafka hasara a kakar baraBiyo bayan ibtila’in da ya afka wa manoman Citta da ya yi sanadiyyar tafka gagarumar asara a kakar noman bara da wasu manoman suka rasa ilahirin amfanin gonarsu, jin ƙai da tallafi na tafe cikin gaggawa daga mahukunta daga Kaduna da gwamnatin Tarayya. Asusun tallafa wa manoma na gwamnatin tarayya NADF da hukumar…
Read More
Ana sa ran ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar za su janye ficewa daga ECOWAS – Ndume

Ana sa ran ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar za su janye ficewa daga ECOWAS – Ndume

Daga AMINA YUSUF ALI Rahotanni dai sun bayyana cewa, ƙasashen Mali, Burkina Faso da Nijar na shirin janye matakinsu na ficewa daga ƙungiyar Ecowas mai raya tattalin arzikin qƙasashen Afirka ta Yamma. Sanata Ali Ndume - wanda ɗan majalisar ƙungiyar Ecowas ɗin ne ya bayyana haka yayin zantawa da manema labarai a Kano, a yayin da majalisar ƙungiyar ke ci gaba da gudanar da taronta a jihar. Dan majalisar ya ce an cimma duk wani abu da ake buƙata domin maido da ƙasashen cikin ƙungiyar ta Ecowas. "An riga an warware saɓanin da ya kai ga ɗaukar matakin fita daga…
Read More
Mafi ƙarancin albashi: NLC ta ƙara matsa lamba a kan gwamnatin Tarayya

Mafi ƙarancin albashi: NLC ta ƙara matsa lamba a kan gwamnatin Tarayya

Daga AMINA YUSUF ALI Ƙungiyoyin 'yan ƙwadago ta NLC da TUC sun nemi gwamnatin Bola Ahmad Tinubu da ta biya Naira 497,000 maimakon Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi. A taqaice dai ma wato sun sassauta abin da suke buƙata gwamnati ta biya a matsayin mafi ƙarancin albashi a ƙasar zuwa naira 497,000. A baya dai ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce dage a kan Naira 615,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi da suke son gwamnatin ƙasar ta amince da shi. Yayin cigaba da tattaunawar a ranar Talatar da ta gabata, ƙungiyoyin sun kuma yi watsi da sabon ƙudirin da gwamnati…
Read More
Kotu ta ba wa ‘yan sandan Kano umarnin fitar da Aminu Ado daga Gidan Sarki na Nasarawa

Kotu ta ba wa ‘yan sandan Kano umarnin fitar da Aminu Ado daga Gidan Sarki na Nasarawa

Babbar Kotu a Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alƙali Amina Adamu Aliyu, ta bai wa Kwamishinan 'Yan Sandan Kano umarni a kan su gaggauta fitar da Aminu Bayero daga Fadar Sarkin Nasarawa inda yake da zama a halin yanzu. Haka nan, Kotun ta ba da umarnin haramta wa Alhaji Aminu Ado Bayero da sauran sarakuna huɗun da aka tuɓe, ɗaukar kansu a matsayin sarakai har sai ta surari ƙarar da ke gabanta. Sauran da hanin ya shafa su ne tuɓaɓɓun sarakunan Bichi da Rano da Gaya da kuma Karaye. Wannan umarni ya biyo bayan ƙararar da lauyan mai ƙara, Ibrahim Isa…
Read More
Za a yi wa yara 6000 gwajin cutar Tarin Fuka a Kano — Dr Labaran

Za a yi wa yara 6000 gwajin cutar Tarin Fuka a Kano — Dr Labaran

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da yin aiki tukuru wajen ganin an kawar da cutar Tarin Fuka (TB) a jihar, Kwamishinan Lafiya na jihar Kano, Dr. Abubakar Labaran Yusuf ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da ya gudana a ranar Litinin, a wani ɓangare na tunawa da ranar gwajin tarin TB na duniya da yake gudana a duk ranar 27-5-2024. Dakta ya ce, za a yi sati guda ana aiwatar da wannan gwaje-gwaje, wanda baya ga gwajin cutar Tarin Fuka za a kuma yi gwajin cutar ƙanjamau da cutar cutar yunwa (Tamowa)…
Read More
Gwamnati ta dakatar da jirgin Air Nigeria har sai baba-ta-gani

Gwamnati ta dakatar da jirgin Air Nigeria har sai baba-ta-gani

Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar cewa, ta dakatar da aikin kamfanin jirgin saman Nijeriya, wato Air Nigeria. Sanarwar wadda aka fitar a ranar Litinin ta ce, dakatarwar ta har baba-ta-gani ce. Ministan Sufurin Jirgin Sama, Festus Keyamo, shi ne ya bayyana haka yayin da yake ba da bayani kan ayyukan ma'aikatarsa a matsayin ɓangare na cika Shuga Bola Tinubu shekara guda a ofis. Da yake ƙarin haske kan dalilin dakatarwar, Keyamo ya ce, jirgin da aka nuna cewa ta Nijeriya ne ba gaskiya, rufa-rufa ce kawai aka yi wa lyan ƙasa a wancan lokaci.
Read More
Kotu ta tabbatar da nasarar da Ododo, Diri suka samu a zaɓukan Kogi da Bayelsa

Kotu ta tabbatar da nasarar da Ododo, Diri suka samu a zaɓukan Kogi da Bayelsa

Kotun Sauraren Ƙararrakin Gwamna a Jihar Kogi mai zamanta a Abuja, ta tabbatar da nasarar da Usman Ododo na jam'iyyar APC ya samu a zaɓen gwamnan jiharda ya gudana a ranar 11 ga Nuwamban 2023. Kwamitin alƙalan ƙarƙashin jagorancin Mai Shari'a Ado Birnin-Kudu, ƙarar da aka shigar kan nasarar da Ododo ya samu ba ta da tushe, a don haka aka yi watsi da ita. Kazalika, Kotun ta ce masu ƙarar, Jam'iyyar SDP da ɗan takararta Murtala Ajaka, zun gaza kare zargin da suke yi da hujjoji masu gamsarwa. A wata mai kama da wannan, Kotun Sauraren Ƙorafe-ƙorafen Zaɓen Gwamnan…
Read More
Namiji mai duka

Namiji mai duka

Daga AISHA ASAS Idan an yi zancen namiji mai dukan matarsa a Arewacin Najeriya, ko ma ince a Ƙasar Najeriya bakiɗaya, ba a cika ɗaga kai a dube ta ba, kasancewar ta zama ruwan dare, kuma iyaye da kakani sun mata gurbi a zamantakewar aure, don haka matar da ba ta jure dukan mijinta ana sanya ta a layin marasa haƙuri. Yayin da ka ce duka ba kyau a addinin Musulunci, to fa ka janyo wa kanka abinda za a iya kiranka ɗan tawayen addini, saboda ya yi wa masu yin sa rana. Mazaje da dama suna kafa hujja da…
Read More