27
May
A ranar Lahadi Jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya gamu tsaiko a hanya a yankin Jere, Kaduna, sa’a guda da fara aiki. Jirgin mai dauke da gomman fasinjoji, ya baro Kaduna ne da misalin karfe 8:05 na safe da nufin zuwa Abuja inda ya gamu da cikas. Bayanai sun ce kafafuwan uku daga cikin taragon jirgin ne suka sauka a layi wanda hakan ya tilasta wa jirgin tsayawa. An ga jami’an tsaro daban-daban a wurin da lamarin ya faru don bai wa jama’a kariya. Hukumar Binciken Tabbatar da Kariya ta Nijeriya (NSIB) ta ce ta tura jami’anta yankin domin gudanar…
