Editor

9513 Posts
Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna ya gamu da cikas sa’a guda da fara aiki

Jirgin ƙasan Abuja-Kaduna ya gamu da cikas sa’a guda da fara aiki

A ranar Lahadi Jirgin kasan Kaduna zuwa Abuja ya gamu tsaiko a hanya a yankin Jere, Kaduna, sa’a guda da fara aiki. Jirgin mai dauke da gomman fasinjoji, ya baro Kaduna ne da misalin karfe 8:05 na safe da nufin zuwa Abuja inda ya gamu da cikas. Bayanai sun ce kafafuwan uku daga cikin taragon jirgin ne suka sauka a layi wanda hakan ya tilasta wa jirgin tsayawa. An ga jami’an tsaro daban-daban a wurin da lamarin ya faru don bai wa jama’a kariya. Hukumar Binciken Tabbatar da Kariya ta Nijeriya (NSIB) ta ce ta tura jami’anta yankin domin gudanar…
Read More
Hajjin Bana: Ɗaya daga cikin alhazan Nijeriya ya rasu a Makka

Hajjin Bana: Ɗaya daga cikin alhazan Nijeriya ya rasu a Makka

Rahotanni daga birnin Saudiyya sun ce, Allah Ya yi wa wani alhajin Najeriya, Alh. Muhammad Suleman rasuwa a Makka a ranar Lahadi. Majiyarmu ta ce marigayin wanda dan asalin Jihar Kebbi ne daga yankin Karamar Hukumar  Argungu, ya rasu ne sakamakon fama da rashin lafiya. Sakataren Hukumar Alhazai na Jihar Kebbi, Faruku Aliyu-Enabo, shi ne ya tabbatar da faruwar hakan ga manema Larabai a Makka. “Marigayin ya rasu ne a ranar Lahadi bayan fama da rashin lafiya, kuma an sallaci gawar a Masallacin Harami (Ka’aba), kana aka binne shi daidai da karantarwar Islama,” in ji Faruk. Jami’in ya yi amfani…
Read More
Sarkin Musulmi ya ƙaddamar da Cibiyar Ilimin Al-Ƙur’ani ta tsangaya a Zamfara

Sarkin Musulmi ya ƙaddamar da Cibiyar Ilimin Al-Ƙur’ani ta tsangaya a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD, a  Gusau Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Alh Sa'ad Abubakar III ya kaddamar da cibiyar koyar da Al-Kur'ani ta jihar Zamfara a ranar Lahadi a garin Gummi, hedikwatar karamar hukumar Gummi ta jihar. Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya sanya wa cibiyar sunan Sarkin Musulmi Sultan Muhammad Sa'ad Abubakar III cibiyar ilimin Kur'ani mai tsarki. Da yake jawabi a lokacin kaddamar da aikin, Sultan Sa’ad Abubakar ya yaba wa Gwamnatin Zamfara bisa wannan sabuwar dabara. A cewarsa, cibiyar za ta magance barace-barace a tsakanin almajirai da Kuma bai wa almajiran makarantun allo samun damar yin ilimin boko. Basaraken…
Read More
An maka gwamnonin Nijeriya a kotu kan rashin sakar wa ƙananan hukumomi mara

An maka gwamnonin Nijeriya a kotu kan rashin sakar wa ƙananan hukumomi mara

Gwamnatin Tarayya ta maka Gwamoni 36 na Jihohin Nijeriya a Kotun Ƙoli kan tauye haƙƙoƙin Shugabannin Ƙananan Hukumomi. Ministan Shari'a kuma Babban Lauyan Gwamnatin Tarayya, Lateef Fagbemi ne ya tabbatar da hakan. Lateef ya ce, Gwamnatin Tarayya ta ƙudiri aniyar ƙwato wa shugabannin ƙananan hukumomi 'yancinsu a hannun gwmanoni, tare da ba su cikakken ikon cin gashin kansu. Kazalika, Gwamnatin ta kuma buƙaci Kotu da ta bayar da umarnin haramta wa gwamnoni sauke zaɓaɓɓun shugabannin ƙananan hukumomi ba bisa ƙa'ida ba. Ta kuma buƙaci Kotun ta ba damar da za a tiƙa tura wa ƙananan hukumomin kuɗaɗen kai-tsaye daga asusun…
Read More
Ana fagarbar mutane da dama sun mutu sakamakon ruftawar masallaci a Legas

Ana fagarbar mutane da dama sun mutu sakamakon ruftawar masallaci a Legas

Ana fargabar mutane da dama sun mutu sanan wasu da ya yawa sun jikkata sakamakon ruftawar ginin masallaci wanda ya auku Papa Ajao, Jihar Legas. Bayanai sun ce ruftawar da auku ne ranar Lahadi yayin da masallata ke tsaka da sallar Azahar. Manhaja ta kalato cewar, an gano wasu gawarwaki da ma waɗanda suka suka jikkata a ƙarƙashin ɓuguzan ginin, kuma ana fargabar akwai wasu da dama da suka maƙale. Ya zuwa kammala haɗa wannan labari, babu wani bayani a hukumance a kan lamarin.
Read More
Gwamnatin Tinubu na goyon bayan bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai – Akume

Gwamnatin Tinubu na goyon bayan bai wa ƙananan hukumomi ‘yancin cin gashin kai – Akume

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, ya bayyana cewa gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ta na goyon bayan a bai wa ƙananan hukumomi 774 na faɗin ƙasar nan ‘yancin cin gashin kan su, kai-tsaye daga asusun gwamnatin tarayya. Akume ya bayyana haka lokacin da yake wa manema labarai jawabi bayan kammala taron Majalisar Zartaswa a ranar Laraba, a Abuja. An yi taron domin tattauna cikar Gwamnatin Tinubu shekara ɗaya da kafuwa. Akume ya ce Shugaba Tinubu ya maida hankali sosai wajen bin doka da oda da tsarin mulkin ƙasa tun da ya hau mulki. Ya…
Read More
CISLAC ta yi kira a wanzar da zaman lafiya a Kano

CISLAC ta yi kira a wanzar da zaman lafiya a Kano

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Cibiyar Rajin Kyautata Ayyukan Majalisun Dokokin da Yaƙi da Rashawa a Nijeriya (CISLAC), ta bayyana damuwarta game da abubuwan da ke faruwa a Kano dangane da batun sauya sarki a jihar. CISLAC ta yi gargaɗin cewa irin abubuwan da ke faruwa a jihar ta Kano na barazana ga zaman lafiyar jihar. Babban Darakta a cibiyar, Auwal Musa Rafsanjani, ya fitar da tsattsauran gargaɗi a kan duk wani yunƙuri na amfani da yanayin da ake ciki a jihar domin ayyana dokar ta ɓaci, Ya ce, ” Irin waɗannan ayyuka ana kallonsu ne a matsayin ganganci da…
Read More
Shekara guda: Ku nuna wa ’yan Nijeriya ayyukanku – Tinubu ga ministocinsa

Shekara guda: Ku nuna wa ’yan Nijeriya ayyukanku – Tinubu ga ministocinsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja A taron tunawa da cikarsa shekara ta farko kan karagar mulki, Shugaba Bola Tinubu ya umurci ministocinsa da su gabatar da rahoton ayyukansu ga ‘yan Nijeriya. Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na kasa, Mohammed Idris, yayin da ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Laraba, ya ce za a gudanar da bukukuwan murnar zagayowar ranar haihuwar qananan yara tare da gabatar da jawabai a ɓangarori da dama na ministocin tarayya 47 daga ranar Alhamis (jiya). Idris ya samu halartar taron manema labarai na ranar Laraba da sakataren…
Read More
Tsohon Shugaban EFCC, Ibrahim Lamorde ya kwanta dama

Tsohon Shugaban EFCC, Ibrahim Lamorde ya kwanta dama

Bayanan da suka cim mana na nuni da cewa, tsohon Shugaban Hukunar EFCC, Ibrahim Lamorde, ya kwanta dama. Majiyarmu ta ce marigayin ya rasu ne a ƙasar Masar inda ya tafi jinya, kuma ya bar duniya yana da shekara 61. An haifi marigayin ne a ranar 20 ga Disamban 1962, sannan ya shiga aikin ɗan sanda a 1986 inda ya yi ritaya a matsayin Mataimakin Sufeto Janar na 'Yan Sanda 2021. A halin rayuwarsa, ya riƙe muƙamin Shugaban EFCC daga 2011 zuwa 2015 bayan da Shugaba Goodluck Jonathan ya tsige Farida Waziri a muƙamin shugabancin hukumar.
Read More
‘Yan majalisa sun amince da dokar komawa ga tsohon Taken Ƙasa

‘Yan majalisa sun amince da dokar komawa ga tsohon Taken Ƙasa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar wakilai ta zartar da wani ƙudirin doka da ya bukaci al’ummar ƙasar su koma rera tsohuwar waƙar taken Nijeriya. Kafin a fara zaman majalisar, majalisar ta shiga wani zama na zartaswa wanda ya kwashe kusan mintuna 40 ana tattaunawa a kan batutuwan da suka wajaba kuma ana kyautata zaton cewa dokar ta taken ƙasar ce ta haifar da batutuwan da aka tattauna. An gabatar da ƙudirin dokar da shugaban majalisar Julius Ihonvbare ya gabatar a karo na farko da kuma karatu na biyu a ranar Alhamis, wanda kwamitin baki ɗaya ya amince da…
Read More