Editor

9513 Posts
Yadda hayaƙin janareta ya kashe mutum bakwai a Bayelsa

Yadda hayaƙin janareta ya kashe mutum bakwai a Bayelsa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutum bakwai sun mutu sakamakon hayaƙin injin janareto da ya mamaye ɗakin da suke kwance a Yenagoa, babban birnin jihar Bayelsa. Jaridar Punch a Nijeriya ta ruwaito cewa an samu gawarwakin mutanen galibinsu ɗaliban Jami'ar Neja Delta a cikin ɗakin Kiɗe-kiɗe watau 'studio' ranar Talata da safe, bayan sun shaƙi hayaƙin injin. Jaridar ta ce sutudiyan na ɗaya daga cikin mutanen da suka mutun ne. An ce a ranar Litinin da daddare ne marigayan suka fara aiki a sutudiyan, sai barci ya ɗauke su sakamakon gajiyar da suka yi, ba tare da sun kashe…
Read More
Ɗan sanda ya bindige abokin aikinsa a ƙoƙarin razana masu zanga-zanga

Ɗan sanda ya bindige abokin aikinsa a ƙoƙarin razana masu zanga-zanga

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An tabbatar da mutuwar wani jami’in rundunar ’yan sandan Nijeriya tare da wasu mutane biyar da suka jikkata a wani rikici da ya varke a yayin aikin samar da zaman lafiya a kasuwar Jos da ke jihar Filato. Rahotanni sun nuna cewa rundunar hadin gwiwa da ta kunshi jami’an ’yan sanda, da ma’aikatan gwamnati, jami’an NSCDC, da jani'an hukumar shige da fice da Operation Rainbow da ke da alhakin tabbatar da tsafta a kasuwa, inda suka fuskanci turjiya mai tsanani daga jama'a. A ci gaba da aikin tabbatar da zaman lafiya wani jami'i ɗaya ya yi…
Read More
Kotu ta ƙi amincewa da tsawaita wa’adin shugabannin ƙananan hukumomi a Ribas

Kotu ta ƙi amincewa da tsawaita wa’adin shugabannin ƙananan hukumomi a Ribas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babbar Kotun Jihar Ribas da ke zamanta a Fatakwal ta bayyana tsawaita wa’adin shugabannin ƙananan hukumomin jihar na tsawon watanni shida da ’yan majalisar dokokin jihar ƙarƙashin jagorancin Martins Amaewhule suka bukata, wanda ya savawa Kundin Tsarin Mulkin ƙasar, kuma ba shi da wani tasiri. ’Yan majalisa 27 da ke sansanin Ministan Babban Birnin Tarayya, Cif Nyesom Wike, a bana, sun kafa dokar da ta tsawaita wa’adin shugabannin ƙananan hukumomi na tsawon shekaru uku da watanni uku.Sai dai a hukuncin da kotun ta yanke a ranar Talata, ta ce sabuwar dokar ta saba wa Kundin Tsarin…
Read More
Al’ummar duniya na ƙara nuna goyon bayansu ga Falastinawa – Abu Shawesh

Al’ummar duniya na ƙara nuna goyon bayansu ga Falastinawa – Abu Shawesh

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Jakadan Falastinu a Nijeriya, Abdullah Abu Shawesh ya bayyana cewa, al'ummar Falastinu suna kara samun goyon baya daga duniya, inda ya ce, a rana ta 230 da fara kisan ƙare dangi, an fara yaɗa irin munanan kisan kiyashi da ake yi wa al'umma Falastinu a gidajen talabijin na duniya. Abu Shawesh ya bayyana haka ne a cikin wata sanarwar manema labarai da ya fitar a ranar Alhamis. Ya ce, tun daga ranar Al Nakba zuwa kisan kiyashin da ake yi a yanzu, shekaru 76 kenan, Falastinawa na cigaba da fuskantar gallazawa da rashin adalci da rashin…
Read More
Hadi Siriki da ƙaninsa sun ƙi amsa laifin karkatar da dukiyar ƙasa

Hadi Siriki da ƙaninsa sun ƙi amsa laifin karkatar da dukiyar ƙasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Zagon Ƙasa, EFCC, ta gurfanar da Hadi Sirika, tsohon ministan sufurin jiragen sama a gaban kotu bisa zargin almundahanar kwangila. EFCC ta gurfanar da Sirika ne tare da ɗan uwansa, Ahmad Abubakar Sirika kamfanin da Enginos Nigeria Limited, wani kamfani mallakin Abubakar, a gaban mai shari’a Suleman Belgore na babban kotun babban birnin tarayya Abuja da ke zaune a Garki, Abuja. An gurfanar da su a gaban kotu kan tuhume-tuhume 10 da aka gyara ranar 13 ga Mayu kuma aka shigar da su ranar 14 ga Mayu,…
Read More
Hedkwatar tsaro ta ƙalubalanci Gwamna Raɗɗa bisa zargin sojoji da cin gajiyar ta’addanci

Hedkwatar tsaro ta ƙalubalanci Gwamna Raɗɗa bisa zargin sojoji da cin gajiyar ta’addanci

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Hedkwatar Tsaro ta Nijeriya ta ƙalubalanci Gwamnan Jihar Katsina, malam Umar Dikko Raɗɗa, kan zargin sojojin Nijeriya da ya yi da hannu wajen cin gajiyar ayyukan ta'addanci a Katsina cikin wata hira da ya yi da gidan talabijin na Channels a shirin 'Politics Today' a ranar 5 ga Afrilu, 2024. AFN ta bayyana cewa babu shakka tana biyayya ga dukkan zaɓaɓɓun wakilan gwamnati don haka tana mutunta dangantakar.  Dangane da furucin da Maigirma Gwamnan Jihar Katsina ya yi a baya, AFN ta zaɓe shi kada ya haɗa baki da Gwamnan Jihar, maimakon ya ƙara…
Read More
Mahaifi ya kai ɗansa kotu domin ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai a Kano

Mahaifi ya kai ɗansa kotu domin ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai a Kano

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani fusataccen mahaifi ya yi karar dan cikinsa a gaban Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Fagge ’Yan Alluna a Jihar Kano. Mahaifin ya koka da cewa ɗan nasa ya addabe shi da sace-sace da kuma shaye-shaye. Mahaifin, wanda aka ɓoye sunansa ya nemi kotun ta ɗaure ɗan nasa har illah ma sha Allah. Mai gabatar da ƙara, Abdul Wada, ya karanta wa wanda ake ƙarar tuhume-tuhumen da ake masa, inda nan take ya amsa laifinsa. Alƙalin kotun, Mai Shari’a Malam Umar l Lawan Abubakar, ya ɗage sauraren shari’ar zuwa ranar 6 ga…
Read More
Badaƙalar Sarauta: Za mu bi umarnin Kotu wajen hana maido da Sanusi a matsayin Sarkin Kano — ‘Yan Sanda

Badaƙalar Sarauta: Za mu bi umarnin Kotu wajen hana maido da Sanusi a matsayin Sarkin Kano — ‘Yan Sanda

Rundunar 'Yan Sanda ta Jihar Kano ta lashi takobin yi wa umarnin kotu biyayya wajen dakatar da naɗa Muhammadu Sunusi II a natsayin Sarkin Kano, da kuma hana Gwamnatin Jihar rushe sabbin masarautu biyar da aka ƙirƙiro a jihar. Kwamishinan'Yan Sandan Jihar, Muhammad Hussain Gumel ne ya bayyana hakan ga manema labarai a ranar Asabar a Babban Ofishin Rundunar da ke Bompai, Kano. Ya ce, “Za mu yi biyayya ga umarnin Kotu na bar komai yadda yake har sai kotu ta yanke hukunci." A ranar Alhamis ne dai Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta ba da umarnin wucin-gadi na…
Read More
Yanzu-yanzu: Abba ya ba da umarnin kama tuɓaɓɓen Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero

Yanzu-yanzu: Abba ya ba da umarnin kama tuɓaɓɓen Sarkin Kano, Aminu Ado Bayero

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ba da umarnin gaggawa kan a tsare tuɓaɓɓen Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero. News Point Nigeria ta rawaito cewar, Mai magana da yawun Gwamna, Sanusi Bature Dawakin Tofa, shi ne ya shaida wa manema labarai hakan da safiyar Asabar. A cewar Yusuf, ‘Komawar Aminu Ado Bayero Kano ba komai ba ne face haddasa rashin lumana a jihar'. “Don haka na bai wa Kwamishinan 'Yan Sanda na Jihar umarnin ya kama Alhaji Aminu Ado Bayero, a duk inda ya gan shi a jihar," in ji sanarwar.
Read More