Editor

9513 Posts
Yaƙi da ta’addanci: Gwamnan Zamfara ya jaddada ƙudirinsa na bai wa sojoji cikakken haɗin kai

Yaƙi da ta’addanci: Gwamnan Zamfara ya jaddada ƙudirinsa na bai wa sojoji cikakken haɗin kai

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya jaddada ƙudirin gwamnatinsa na bai wa jami'an tsaro cikakken haɗin kai da goyon baya wajen yaƙi da ɓarayin daji a faɗin jihar. Ya bayyana hakan ne yayin da ya jagoranci taron majalisar tsaron jihar Zamfara a Fadar Gwamnati da ke Gusau, babban birnin jihar. Sanarwa mai ɗauke da sa hannun Kakakin Gwmanan, Sulaiman Bala Idris, taron ya mai da hankali ne kan sha'anin tsaron jihar da kuma yaƙi da ɓarayin daji da ke gudana a jihar. Sanarwar ta rawaito Lawal na cewa, “Taron yau zai auna sha'anin tsaron jihar ne don sanin nasarorin…
Read More
Tinubu ya bai wa fasinjoji alakoron wata biyu a sabon jirgin ƙasan Abuja

Tinubu ya bai wa fasinjoji alakoron wata biyu a sabon jirgin ƙasan Abuja

Daga WAKILINMU A yayin da aka kammala shirye-shiryen buɗe tashar sabon jirgin ƙasan Abuja a ranar 29 ga watan Mayu, Ministan babban birnin, Nyesom Wike, ya shaida wa manema labarai cewa tuni Shugaba Tinubu ya buƙaci da a ɗebi fasinjoji kyauta na tsayin wata biyu a jirgin ba tare da an karɓi ko sisinsu ba. Hakan na zuwa ne a yayin da Gwamnatin Tarayya ta ce ta sami ragin Dala Milyan 53 a aikin wanda a ka kammala shi a kan kuɗi Dala milyan 75 maimakon Dala milyan 128 da gwamnatin baya ta ce za a yi aikin. Ministan ya…
Read More
Tinubu ba zai iya magance matsalolin Nijeriya a shekara ɗaya ba — Sanusi II

Tinubu ba zai iya magance matsalolin Nijeriya a shekara ɗaya ba — Sanusi II

Daga WAKILINMU An bayyana cewa, da kamar wuya Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya iya magance matsalolin Nijeriya a cikin shekara guda da kama mulki. Sarkin Kano na 14, Muhammad Sunusi II, shi ne ya bayyana haka a ranar Alhamis sa'ilin da yake jawabi a taron ƙoli na tattalin arziki da zuba jari wanda jihar Rivers ta shirya a Fatakwal, babban birnin jihar. Sunusi ya ce, "A irin wannan yanayin ya kamata mu fuskanci zahiri a matsayinmu na 'yan ƙasa, ɓarnar da aka tafka a Nijeriya cikin shekaru 10 wadda ta gurgunta duk wani sashin gudanarwar ƙasar ba za a iya…
Read More
Sanusi ya dawo!

Sanusi ya dawo!

…kan karagar Sarkin Kano…Mun ba tsoffafin sarakuna kwanaki biyu su kwashe komatsansu – Gwamna Abba Daga RABIU SANUSI a Kano Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya bayyana Muhammadu Sanusi ll, wanda aka fi sani da Sanusi Lamiɗo Sanusi, a matsayin sabon Sarkin Kano na 16 da zai cigaba da zama karagar mulkin Masarautar Kano. Gwamna ya bayyana haka ne a jiya Alhamis yayin da ya ke rattaɓa hannu kan dokar da Majalisar Dokokin Jihar Kano a ƙarƙashin jagorancin Kakakin Majalisar, Rt. Hon. Jibril Isma'il Falgore, ta yi wa gyara ta shekarar 2019. Haka kuma Abba Kabir ya ce,…
Read More
Yadda Tinubu ya rufe ƙofa da Aminu Ɗantata

Yadda Tinubu ya rufe ƙofa da Aminu Ɗantata

Daga MAHDI M. MUHAMAMAD Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi baƙuncin hamshaƙin ɗan kasuwa, shugaban rukunin kamfanonin Dantata, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, a fadar shugaban aasa da ke Abuja a ranar Talata. Lokaci na ƙarshe da aka ga mutanen biyu tare a bainar jama'a shi ne a shirye-shiryen zaɓen 2023, Tinubu ya ziyarci fitaccen ɗan kasuwan a Kano. Ba a bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar ta ranar Talata ga jama'a ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
Read More
Toni Kroos: Ɗan wasan Real Madrid da Jamus zai yi ritaya bayan kammala gasar Euro 2024

Toni Kroos: Ɗan wasan Real Madrid da Jamus zai yi ritaya bayan kammala gasar Euro 2024

Daga MAHDI M. MUH'D Ɗan wasan tsakiya na Real Madrid da Jamus, Toni Kroos zai rajaye takalmansa daga buga wasan ƙwallon ƙafa bayan gasar Euro 2024 da za ta gudana a Jamus ɗin. Ɗan wasan mai shekaru 34, ya yi fice a ƙwallon ƙafa, inda ya lashe kofuna da dama tare da Real Madrid tun bayan da ya koma ƙungiyar daga Bayern Munich a watan Yulin shekarar 2014, inda ya lashe kofin La Liga da na zakarun Turai sau 4 kowanne. Kroos na cikin tawagar ƙwallon ƙafar Jamus da ta lashe gasar kofin duniya a shekarar 2014. A watan Yulin…
Read More
An bai wa tsofaffin sarakunan Kano sa’o’i 48 su fice daga masarautu

An bai wa tsofaffin sarakunan Kano sa’o’i 48 su fice daga masarautu

Daga IBRAHIM HAMISU, a Kano Gwamnatin jihar Kano ta bai wa tsofaffin sarakunan masarautun Kano; Rano da Gaya da Bichi da Ƙaraye wa’adin sa’o’i 48 su fice daga fada bayan rushe masarautun da gwamnatin ta yi a ranar Alhamis. Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ne ya sanar da haka lokacin da ya yi jawabi jim kaɗan bayan sanya hannu kan dokar da ta rushe dokar da ta assasa masarautun a shekara ta 2019. A ranar Alhamis ne Gwamnan ya sanya hannu kan sabuwar dokar masarautar Kano, wadda ta rushe ƙarin masarautu huɗu da aka samar a 2019, wanda hakan ya…
Read More
Babu sarki a Kano a halin yanzu — Majalisa

Babu sarki a Kano a halin yanzu — Majalisa

Biyo bayan soke masarautun da tsohuwar gwamnatin Ganduje ta ƙirƙiro a Kano a zaman da ta yi ranar Alhamis, Majalisar Dokokin Jihar ta ce a halin yanzu babu sarki a Kano. Shugaban Masu Rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Chediyar Yan Gurasa, shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake yi wa manema labarai ƙarin haske dangane da matakin rushe masarautun da majalisar ta ɗauka. Ya ce a halin da ake ciki an aike da dokar masarautun da aka yi wa kwaskwarima ga Gwnan Kano, Abba Kabir, don ya rattaɓa hannu. Ya kara da cewa, dokar ta bai wa Gwamna…
Read More
Majalisar Dokokin Kano ta rushe sabbin masarautun da Ganduje ya ƙirƙiro

Majalisar Dokokin Kano ta rushe sabbin masarautun da Ganduje ya ƙirƙiro

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da rushe sabbin masarautu huɗu da tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ta ƙirƙiro a jihar. Majalisar ta kuma rage matsayin sarakunan masarautun da abin ya shafa zuwa hakimai. Masarautun da lamarin ya shafa su ne; Bichi, Gaya, Karaye da kuma Rano. Majiyarmu ta ce an girke jami’an tsaron hukumar DSS a Fadar Sarkin Kano a safiyar Alhamis da ake soke sabbin masarautun.
Read More