Majalisar Dokokin Kano ta rushe sabbin masarautun da Ganduje ya ƙirƙiro

Spread the love

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta amince da rushe sabbin masarautu huɗu da tsohuwar gwamnatin Abdullahi Ganduje ta ƙirƙiro a jihar.

Majalisar ta kuma rage matsayin sarakunan masarautun da abin ya shafa zuwa hakimai.

Masarautun da lamarin ya shafa su ne; Bichi, Gaya, Karaye da kuma Rano.

Majiyarmu ta ce an girke jami’an tsaron hukumar DSS a Fadar Sarkin Kano a safiyar Alhamis da ake soke sabbin masarautun.

By Editor