Yadda Tinubu ya rufe ƙofa da Aminu Ɗantata

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMAMAD

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya karɓi baƙuncin hamshaƙin ɗan kasuwa, shugaban rukunin kamfanonin Dantata, Alhaji Aminu Alhassan Dantata, a fadar shugaban aasa da ke Abuja a ranar Talata.

Lokaci na ƙarshe da aka ga mutanen biyu tare a bainar jama’a shi ne a shirye-shiryen zaɓen 2023, Tinubu ya ziyarci fitaccen ɗan kasuwan a Kano.

Ba a bayyana cikakkun bayanai kan tattaunawar ta ranar Talata ga jama’a ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

By Editor