Tinubu ya bai wa fasinjoji alakoron wata biyu a sabon jirgin ƙasan Abuja

Spread the love

Daga WAKILINMU

A yayin da aka kammala shirye-shiryen buɗe tashar sabon jirgin ƙasan Abuja a ranar 29 ga watan Mayu, Ministan babban birnin, Nyesom Wike, ya shaida wa manema labarai cewa tuni Shugaba Tinubu ya buƙaci da a ɗebi fasinjoji kyauta na tsayin wata biyu a jirgin ba tare da an karɓi ko sisinsu ba.

Hakan na zuwa ne a yayin da Gwamnatin Tarayya ta ce ta sami ragin Dala Milyan 53 a aikin wanda a ka kammala shi a kan kuɗi Dala milyan 75 maimakon Dala milyan 128 da gwamnatin baya ta ce za a yi aikin.

Ministan ya ce, za su yi amfani da wani sashi na rarar kuɗin don samar da wasu ababe da ba a tanadarwa tashoshin jirgin ƙasan ba wanda suka haɗa da na’urorin sanyaya wuri a inda fasinjoji ke dakon jirgi, da samar da matattakalar dattijai da masu buƙata ta musamman da ma kumbon hawa da sauka, wato Lifter a Turance.

Zuwa yanzu, sabon jirgin jigilar na da tashoshi takwas ne da suka haɗa da Abuja Metro, Stadium, Kukwaba I, Kukwaba II, Wupa, Idu, Basanjiwa, sai tasharsa ta filin jirgin sama.

By Editor