Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Ƙungiyoyin masu kula da fursunonin Falasɗinu sun ce wani babban likita Bafalasɗine ya mutu a gidan yarin Isra’ila bayan shafe sama da watanni huɗu yana tsare.
Dr Adnan Al-Bursh, mai shekaru 50, shi ne shugaban likitoci a asibitin al-Shifa.
Ma’aikatar gidan yarin Isra’ila ta tabbatar da cewa wata sanarwa da aka buga a ranar 19 ga Afrilu game da wani fursuna da aka tsare saboda dalilan tsaron ƙasa ya mutu a gidan yarin Ofer shine Dr Al-Bursh.
Ba a bayar da cikakken bayani kan musabbabin mutuwar ba, kuma hukumar gidan yarin ta ce ana binciken lamarin.
Sai dai ƙungiyoyin fafutukar kare haƙƙin Falasɗinu a cikin wata sanarwar haɗin gwiwa da suka fitar a ranar Alhamis sun ce mutuwar Dr Al-Bursh “kisa ce” kuma har yanzu gawarsa tana hannun Isra’ila.
Dr Al-Bursh shi ne shugaban likitoci a cibiyar kiwon lafiya mafi girma a Gaza, asibitin al-Shifa, wanda sojojin Isra’ila suka kai farmaki sau da dama.
Yana aiki na wucin gadi a asibitin Al-Awada da ke arewacin Gaza lokacin da sojojin Isra’ila suka tsare shi.
Abokan aikinsa sun karrama marigayi likitan tiyatar, inda suka bayyana shi a matsayin “mai tausayi” da kuma “jarumi”.
Daraktan Al-Shifa, Dr Marwan Abu Saada, ya ce labarin rasuwarsa abu ne mai ƙona rai.
Wani abokin aikinsa, Dokta Suhail Matar, ya kira Dr Al-Bursh “ma’abocin aminci” ga kowane sashen kiwon lafiya a duk asibitocin Gaza.
