Editor

9416 Posts
Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi a Adamawa

Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi a Adamawa

Daga BASHIR ISAH Gwamnan jihar Adamawa Ahmadu Umaru Fintiri ya ƙaddamar da hanyoyi na sama da kilomita 340 a sassan jihar da zimmar sauƙaƙa wa 'yan karkara sha'anin zirga-zirga Aikin samar da hanyoyin haɗin guiwa ne tsakanin gwamnatin Adamawa da Bankin Duniya da cibiyar French Development Agency ƙarkarshin Shirin Samar wa Karkara Hanyoyi na Gwamnatin Tarayya (RAMP-2). Hanyoyin da aka aka ƙaddamar sun shafi ƙananan hukumomi 21 da jihar ke da su ne. Yayin da yake magana a wajen ƙaddamar da hanyoyin, Gwamna Fintiri ya ce gwamnatinsa ba ta sa wasa ba wajen biyan kasonta ga shirin haɗin guiwar wanda…
Read More
Peters ya maye gurbin Farfesa Adamu a NOUN

Peters ya maye gurbin Farfesa Adamu a NOUN

Daga FATUHU MUSTAPHA Farfesa Olufemi A. Peters ya kama aiki a matsayin sabon Mataimakin Shugaban Buɗaɗɗiyar Jami'ar Nijeriya (NOUN) inda ya maye gurbin Farfesa Abdalla Uba Adamu wanda wa'adin aikinsa ya kammala a ranar Laraba, 10 ga Fabrairun 2021. Da yake jawabi yayin bikin karɓar ragamar aiki da ya gudana a ranar Alhamis a Abuja, Petaers ya bayyana cewa jami'ar ba za ta taɓa mancewa da gudunmawar da Adamu ya bayar wajen cigabanta ba a zamaninsa. Ya ce, "Zamanin Farfesa Adamu a jami'ar abu ne da ba za a manta da shi ba, kuma zai zama abin kwatance a gare…
Read More
Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Daga FATUHU MUSTAPHA Rundunar Sojojin Nijeriya ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta buga mai nuni da 'yan Boko Haram da mayaƙan ISWAP sun kashe sojoji 20 a yankin Arewa maso-gabas. A sanarwar da rundunar ta fitar a Alhamis, Daraktan Sashen Hulɗa da Jama'a na rundunar, Brig.-Gen Mohammad Yerima, ya ce wannan labari ba shi da tushe balle makama. Ya ce an yaɗa labarin ne da manufar sanyaya wa al'umma guiwa game da sha'anin yaƙi da matsalolin tsaro da sojojin ke yi da ma su kansu sojojin da ke yaƙin. A cewarsa harin baya-bayan nan da aka kai wa…
Read More
Tsohon gwamnan Legas ya rasu

Tsohon gwamnan Legas ya rasu

Daga AISHA ASAS Allah ya yi wa gwamnan farar hula na farko a jihar Legas, Lateef Kayode Jakande rasuwa. Marigayin ya bar duniya yana da shekara 91. A halin rayuwarsa, Jakande wanda tohon ɗanjarida ne, ya yi gwamna a Jihar Legas daga 1979 zuwa 1983. Haka nan, ya riƙe muƙamin Ministan Ayyuka a zamanin mulkin marigayi Sani Abacha. An haifi marigayin ne a ranar 23 ga Yulin 1929, a Legas. Gwamnan Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya nuna alhinin dangane da rasuwar, tare da bayyana marigayin a matsayin babban rashi.
Read More
Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kayayyaki

Daga WAKILIN MU Ofishin Hukumar Yaƙi da Fasa-ƙwauri ta Ƙasa na 'Zone C', ya ce ya samu nasarar kama kayayyakin da aka haramta shigo da su cikin ƙasa wanda harajinsu ya haura milyan N869 a Janairun da ya gabata. Kayayyakin da ofishin ya ce ya kama ciki har da katan 1,024 na magungunan da ba a yi musu rajista ba, da shinkafar ƙetare buhu 1,046, da katan 62 na sabulun, da mota ƙirar Toyota da dai sauransu. A cewar Comptroller Yusuf Lawal, haƙƙinsu ne tabbatar da cewa ana kiyaye dukkan ƙa'idojin da gwamnati ta shimfiɗa dangane da haramcin shigo da…
Read More
Jami’ar Bauchi ta yi sabon suna

Jami’ar Bauchi ta yi sabon suna

Daga AISHA ASAS Majalisar Zartarwa ta Gwamnatin Jihar Bauchi ta aminta da batun sauya wa Jami'ar Bauchi, Gadau, suna zuwa Jami'ar Sa'adu Zungur. Sanarwar da Kwamishinan Ilimin Jihar Bauchi, Dr. Aliyu U. Tilde ya fitar, ta nuna an ɗauki matakin sauya wa jami'ar suna ne domin raya sunan marigayi Sa'adu Zungur (1915-1958) a matsayinsa na ɗaya daga cikin mazan jiya da suka bada gudunmawarsu wajen samun 'yancin kan ƙasa. A halin rayuwarsa, Malam Sa'adu Zungur ya riƙe muƙamin sakataren NCNC, ɗan gwagwarmayar sisaya ne wanda basirarsa ta yi tasiri wajen daidaita harkar siyasar Arewa, har wa yau mutum ne wanda…
Read More
BUA ya saya wa Nijeriya rigakafin korona guda milyan ɗaya… da magana – inji CACOVID

BUA ya saya wa Nijeriya rigakafin korona guda milyan ɗaya… da magana – inji CACOVID

Daga FATUHU MUSTAPHA Fitaccen kamfanin nan BUA Group, ya saya wa Nijeriya maganin rigakafin cutar korona guda milyan ɗaya a matsayin gudunmawarsa ga ƙasa wajen yaƙi da annobar korona. Bayanai sun nuna BUA ya sayi maganin ne tare da haɗin guiwar haɗakar masu taimaka wa Gwamnatin Nijeriya da saurarnsu wajen yaƙi da koro da aka fi sani da CACOVID a taƙaice. Ana sa ran magani ya iso Nijeriya a mako mai zuwa wanda idan hakan ya tabbata, a iya cewa shi ne ya zama rigakafi na farko da Nijeriya ta samu tun bayan ɓullar annobar korona. Kamfanin BUA ya ce…
Read More
Tsohon ɗanwasan Super Eagles ya rasu

Tsohon ɗanwasan Super Eagles ya rasu

Daga WAKILIN MU Tsohon ɗan wasan Super Eagles Yisa Sofoluwe, ya rasu. Sofoluwe ya rasu ne a Talatar da ta gabata a Asibitin Koyarwa ta Jami'ar Legas bayan fama da ya yi da lalurar ƙwaƙwalwa. Tun farko sai da aka kai marigayin wata asibiti a yankin Ikorodu kafin daga bisani aka ɗauke shi zuwa asibitin jami'ar Legas. A halin rayuwarsa, marigayin ya buga wa Nijeriya wasa da dama, ciki har da gasar cin kofin Afirka (AFCON) a 1984 da 1988. Haka nan, ya samu zarafin buga ma wasu manyan ƙungiyon ƙwallon ƙafa na ƙasa, irin su 3SC da Julius Berger…
Read More
A shirye muke mu samar wa makiyaya wuraren kiwo –   Gwamnonin Arewa

A shirye muke mu samar wa makiyaya wuraren kiwo – Gwamnonin Arewa

Daga AISHA ASAS Gwamnonin Arewa sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta tallafa musu da kuɗaɗen da za su yi amfani da su wajen samar da gandun dazazzuka a sassan yankinsu don amfanin makiyaya. Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma gwamnan jihar Filato Simon Lalong shi ne ya yi wannan kira yayin wani shirin talabijin da aka yi da shi a Talatar da ta gabata. Yana mai cewa, da dadewa gwamnonin Arewa sun yi na'am da shirin samar da gandun dazuzzukan. Ya ce duba da yadda harkokin sace sacen mutane ke ta ƙaruwa da kuma batun umarnin ficewa da aka…
Read More
Buhari ya ƙaddamar da aikin layin dogo daga Kano Zuwa Nijar

Buhari ya ƙaddamar da aikin layin dogo daga Kano Zuwa Nijar

Daga BASHIR ISAH A Talatar da ta gabata Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ƙaddamar da aikin gina layin dogo wanda zai tashi daga Kano-Katsina-Jibiya-Maraɗi, da kuma wanda zai ratse zuwa Dutse a jihar Jigawa. Da yake jawabi ta bidiyo daga fadarsa da ke Abuja yayin bikin ƙaddamawar, Buhari ya ce bayan kammala aikin hakan zai taimaka wajen bunƙasa harkokin tattalin arzikin ƙasa musamman ma hada-hadar kasuwanci a tsakanin Nijeriya da Nijar. Daga nan ya kira ga 'yan kasuwa da su yi amfani da wannan dama wajen gudanar da harkokin kasuwancin da ba su saɓa wa dokoki ba da nufin bunƙasa…
Read More