01
Mar
Daga BASHIR ISAH A halin da ake ciki jihar Ekiti ta ce ta shirya tsab domin karɓar baƙuncin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa su 16 daga jihar Kwara da na sauran jihohi daga shiyyar Kudu maso-yamma sakamakon gasar ƙwallon ƙafa ta ƙasa da aka shirya gudanarwa a jihar. A zantawarsu da manema labarai, Shugaban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Jihar, Ekiti Bayo Olanlege, ya bayyana farin cikinsa tare da bada tabbacin cewa jihar ta shirya karɓar baƙi albarkacin gasar. Olanlege ya yi amfani da wannan dama wajen yi wa baƙinsu albishir da cewa lallai za su ji daɗin gwargwadon zaman da za su…
