Editor

9513 Posts
Gasar ƙwallon ƙafa: Ekiti ta shirya karɓar baƙi

Gasar ƙwallon ƙafa: Ekiti ta shirya karɓar baƙi

Daga BASHIR ISAH A halin da ake ciki jihar Ekiti ta ce ta shirya tsab domin karɓar baƙuncin ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa su 16 daga jihar Kwara da na sauran jihohi daga shiyyar Kudu maso-yamma sakamakon gasar ƙwallon ƙafa ta ƙasa da aka shirya gudanarwa a jihar. A zantawarsu da manema labarai, Shugaban Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa na Jihar, Ekiti Bayo Olanlege, ya bayyana farin cikinsa tare da bada tabbacin cewa jihar ta shirya karɓar baƙi albarkacin gasar. Olanlege ya yi amfani da wannan dama wajen yi wa baƙinsu albishir da cewa lallai za su ji daɗin gwargwadon zaman da za su…
Read More
Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Nijeriya ta samu ƙarin mutum 240 da suka harbu da cutar korona

Daga WAKILINMU An bada sanarwar cewa Nijetiya ta samu ƙarin wasu mutum 240 da suka kamu da cutar korona a 'yan sa'o'in da suka gabata. Cibiyar Yaƙi da Yaɗuwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) ce ta bada sanarwar haka da daddare a Lahadin da ta gabata, ta shafinta na twita. Ƙarin da NCDC ta ce an samu ya shafi wasu jihohi ne su 13 kamar haka: Anambra 85, Lagos 82, Osun 17, Ogun 10, Kwara 9, FCT 8, Kano 7, Abia 6, Ekiti5, Borno 4, Edo 2, Bayelsa 2, Kaduna 2 da kuma Rivers 1. Cibiyar ta ce katafariyar cibiyar bada…
Read More
Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Minista Bello ya ƙaddamar da shirin kiyaye dokokin hanyoyi a Abuja

Daga AISHA ASAS Ministan Abuja Malam Muhammad Musa Bello, ya ƙaddamar da shirin yaƙi da karya dokokin hanya a birnin Abuja a matsayin wani mataki na tabbatar da jama'a na kiyaye dokokin hanya yadda ya kamata a cikin birnin. Ƙaddamar da shirin ya auku ne a ƙarshen makon da ya gabata a Abuja. A lokacin da yake jawabi a wajen taron ƙaddamarwar, Bello ya tunatar da mazauna Abuja cewa dukkanin ƙa'idoji da alamomin da aka sanya a hanyoyi, an yi hakan ne da nufin kare rayukan masu amfani da hanyoyin da kuma hana cunkoso. Yana mai cewa, duba da yadda…
Read More
Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Hukumar Zaɓe za ta yi wa ma’aikatan ta bita kan aikin faɗakarwa

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa za ta shirya wata bita ta musamman domin wayar da kan ma'aikatan ta na sashen faɗakar da masu zaɓe da ke hedikwatar ta da kuma jihohi. Wata sanarwa da ta fito daga hukumar a ranar Asabar ta ce bitar, mai taken "Faɗakar da Mai Faɗakarwa", wato "Train-the- Trainers (ToT)", an kasa ta zuwa gida biyu saboda matsalar annobar korona (COVID-19) da ake fama da ita. Kashin farko za a yi bitar ga shugabannin sashen faɗakar da masu zaɓe (HODs VEP) da ke jihohin Kudu da kuma waɗanda su ke…
Read More
Hajjin 2021: Babu kujerar Hajji da aka bai wa Nijeriya – inji NAHCON

Hajjin 2021: Babu kujerar Hajji da aka bai wa Nijeriya – inji NAHCON

Daga BASHIR ISAH Hukumar Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta kore batun da aka yi ta yayatawa wai ta samu kujerun Hajji daga Gwamnatin Saudiyya na Hajjin bana. Sanarwar da hukumar NAHCON ta fitar a Juma'ar da ta gabata wadda ta samu sa hannun shugabar sashen hulɗa da jama'a ta hukumar, Fatima Sanda, ta nuna hankalin hukumar ya kai ga wani saƙon talla da aka yi ta yaɗawa a soshiyal midiya kan cewa Nijeriya ta samu gurbin mahajjata 50,000 na Hajjin 2021/1442 AH a hukumance. Tallar ta buƙaci maniyyata Hajji suna iya soma ajiyar wani kaso na kuɗi don sayen kujerar…
Read More
An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

An sako ɗaliban Sakandaren Kagara

Daga FATUHU MUSTAPHA Bayanai daga Jihar Neja sun nuna an sako ɗalibai da malamai na Sakandaren Kimiyya Kagara da 'yan bindiga suka yi garkuwa da su 'yan kwanakin da suka gabata. Wata majiya mai tushe ta tabbatar wa jaridar PRNigeria batun sakin ɗaliban a safiyar wannan Asabar. Idan dai za a iya tunawa, Manhaja ta ruwaito batun sace ɗaliban su 27 da ma'aikata 3 da iyalansu su 12, a ranar 17 ga Fabrairun 202.
Read More
Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Yaƙin Badar tsakanin Buba Marwa da ’yan ƙwaya

Daga IBRAHIM SHEME A ranar Litinin da ta gabata, sabon shugaban Hukumar Yaƙi da Safara da Shan Muggan Ƙwayoyi (NDLEA), Janar Mohammed Buba Marwa (ritaya), ya yi wata magana wadda ya kamata ta farkar da duk ɗan Nijeriya game da matsalar da fataucin muggan ƙwayoyi ke janyo wa ƙasar nan. Cewa ya yi kashi 90 cikin ɗari na muggan laifukan da ake aikatawa a Nijeriya, sakamakon ɗirkar muggan ƙwayoyi da wasun mu ke yi ne. A cewar sa, laifuka irin su hare-haren ‘yan bindiga, ta’adda, satar mutane, fyaɗe da sauran su duk ‘yan ƙwaya ne ke aikata su. Marwa, wanda…
Read More