Tattaunawa

Mai Mala Buni na musamman ne a Nijeriya – Nura Dalhatu

Mai Mala Buni na musamman ne a Nijeriya – Nura Dalhatu

Kwamared Nura Dalhatu Audu, ya bayyana cewa, Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, na musamman ne a Nijeriya. Saboda haka ne ma ya ke samun nasarori ga duk abin da ya tunkara a rayuwarsa. A cikin wannan tattaunawar da ya yi da manema labarai, ciki har da Wakilin Blueprint Manhaja, MUHAMMAD AL-AMEEN, tare da sauran muhimman batutuwa. Ga yadda cikakkiyar tattaunawar take: Masu karatu za su so sanin Kwamared Nura Dalhatu Audu?Alhamdulillah, kamar yadda duk wanda ya sanni sunana Nura Dalhatu Audu, kuma an haife ni a garin Gashuwa, ta ƙaramar hukumar mulkin Bade a jihar Yobe sannan kuma…
Read More
Tattaunawa ta musamman da Sheikh Nazifi Alkarmawy

Tattaunawa ta musamman da Sheikh Nazifi Alkarmawy

Daga BILKISU YUSUF ALI Sheikh Nazifi Alkarmawy fitaccen malami ne kuma limamin masallacin Juma’a, sannan marubuci, wanda ya yi fice wurin faɗakar da al’umma kan su tausaya wa mata, su kuma kyautata mu su. Wannan ya ƙara wa malamin farin jini, musamman a wurin mata iyayen giji, inda za ka yi ta ganin wani sashe na wa’azuzzukansa yana yawo a kafofin sadarwa. Wakiliyar Blueprint Manhaja, Bilkisu Yusuf Ali, ta samu tattaunawa da shi. Ga yadda hirar ta kasance: Za mu so mu ji tarihinka.Sunana Sheikh Muhammad Abdulwahid Muhammad Nazifi ɗan Shehi Muhammad Auwal da aka fi sani da shehu Malam…
Read More
Dalilin da ya sa na cancanci zama Shugaban APC na Ƙasa – Al-Makura

Dalilin da ya sa na cancanci zama Shugaban APC na Ƙasa – Al-Makura

Daga IBRAHEEM HAMZA MUH’D a Lafia Sanata Umaru Tanko Al-Makura shi ne tsohon Gwamnan jihar Nasarawa kuma yana ɗaya daga cikin ’yan takarar kujerar Shugaban Jam'iyyar APC ta Ƙasa. Ya zanta da Wakilin jaridar Blueprint Manhaja, Ibraheem Hamza Muhammad kan takarar tasa. Ga yadda hirar tasu ta kasance: MANHAJA: Jam'iyyar APC za ta yi zaɓen fitar da sabbin shugabannin jam'iyya. Mene ne manufarka?Maƙasudin yin takarata ita ce, Ina ɗaya daga cikin iyayen jam'iyya, don daga Jam'iyyar CPC aka samar da ACP. Wato a turance ‘Merger’ kenan. Kuma mu na son ganin an ciyar da jam'iyyar gaba da mutumci. Na yi…
Read More
Tattaunawa ta musamman da Sheikh Ibrahim Mansoor

Tattaunawa ta musamman da Sheikh Ibrahim Mansoor

Daga BILKISU YUSUF ALI Sheikh Ibrahim Mansoor Malami ne matashi kuma mabiyin ɗariƙar Tijjaniya, amma kuma wanda a kullum fatansa shine a haɗa kai a zauna lafiya tsakanin dukkan Musulmi ko kuwa masu bambancin aƙida ne, inda Sheikh Mansoor ya kasance bai yarda da rarrabuwa ba, don aƙida. Ga dai yadda Wakiliyar Blueprint Manhaja, BILKISU YUSUF ALI, ta gana da shi: Za mu so mu ji taƙaitaccen tarihinkaSunana Ibrahim amma mahaifina yana kirana Inyas kakana yana kira na Barhama ‘yan’uwana suna kirana Shehu. Sunan mahaifina malam Mansur. An haifeni a cikin garin Kaduna a wata unguwa da ake kirantaTudun Nufawa…
Read More
Sai da na girma na shiga karatun boko – Hon. Ado Rodi

Sai da na girma na shiga karatun boko – Hon. Ado Rodi

Daga MUHSIN TASIU YAU a Kano Gwarzon ɗan gwagwarmaya kuma matashi abun koyi, Hon. Ado Idris, wanda aka fi sani da Ado Rodi, ɗan kasuwa ne kuma ɗan siyasa, Kansila Mai Gafaka (Supervisory Councilor) a Ƙaramar Hukumar Kumbotso da ke Jihar Kano. Ga yadda tattaunawarsa da Wakilin Blueprint Manhaja, Muhsin Tasiu Yau, ta kasance: Za mu so mu ji taƙaitaccen tarihin rayuwarkaAn haifi ni a 1982 a unguwar Sheka. Na taso na yi shekara uku zuwa huɗu sai aka kai ni makarantar allo. Mahaifina ɗan kasuwa ne kuma ya rasu tun muna ƙanana, ba mu girma da shi ba. Mahaifina…
Read More
Mulki ya fi damun Buhari kan yi wa jama’a aiki – Isyaku Ibrahim

Mulki ya fi damun Buhari kan yi wa jama’a aiki – Isyaku Ibrahim

Daga IBRAHIM HAMZA MUHAMMAD Alhaji Isyaku Ibrahim, dattijo ne mai shekaru 85 a Duniya. Ya kasance ɗan siyasa ne, kuma mai tallafa wa al'umma. Ya yi sharhi dangane da mulkin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, hukumar Zabe ta ƙasa, (INEC) da kuma Gwamnoni. Ya yi bayani dangane da yadda za a gina ƙasa dungurungun don rage zaman kashe wando a tsakanin miliyan goma sha uku na matasa marasa aikin yi kamar yadda hukumar kididdiga ta kasa, (NBS) ta tabbatar. MANHAJA: Mene ne ra'ayinka dangane da  dimbin matasa marasa aikin yi a ƙasar nan?ISYAKU IBRAHIM: A matsayina na Uba kuma kaka mai…
Read More
Mun kakkaɓe miyagu a dazukan Katagum, cewar magajin Ali Ƙwara

Mun kakkaɓe miyagu a dazukan Katagum, cewar magajin Ali Ƙwara

Daga BAKURA K. MUHAMMAD a Bauchi Ahmad Muhammad Ƙwara ƙani ne ga Marigayi Alhaji Ali ƙwara, kuma uwarsu ɗaya ubansu ɗaya da marigayin, kuma shine ya gaje shi wajen yaƙi da 'yan fashi da ɓarayi. A farkon makon da ya gabata ne Ƙungiyar Matasan Arewa ta shirya taron lakca don tunawa da Marigayi Ali Ƙwara kan irin gudunmawar da ya bayar wajen inganta harkokin tsaro, kasuwanci da kuma taimakon al'umma, wanda aka gudanar a garin Azare ta ƙasar Katagum da ke cikin jihar Bauchi. A ƙarshen taron, manema labarai sun tattauna da Ahmad Ƙwara, kamar haka: Me za ka ce kan…
Read More
Ko yau na bar shugabancin Jami’ar Nasarawa na kafa tarihi – Farfesa Sulaiman

Ko yau na bar shugabancin Jami’ar Nasarawa na kafa tarihi – Farfesa Sulaiman

Daga JOHN D. WADA a Lafiya A yayin da mahukuntan Babbar Jami’ar Jihar Nasarawa da Gwamnatin Jihar ke cigaba da murnar cikar jami’ar shekaru 20 da kafuwa, Wakilin Manhaja, John D. Wada, ya samu damar tattauna da shugaban Jami’ar Farfesa Suleiman Bala Mohammed inda ya bayyana nasarori da ƙalubale da jami’ar ke fuskanta kawo yanzu, da suka haɗa da shirin hura wisu wato 'whistle blowing policy' a Turance da ta kirkiro don gano tare da hukunta miyagun ɗalibai da malamanta, da batun ƙungiyoyin asiri da sauransu. Ga yadda tattaunawar ta kasance: Manhaja: A kwanakin baya kun kafa wata doka ta…
Read More
Yadda zakin da na harba ya rikiɗe zuwa mutum – Sarkin Maharban Akko

Yadda zakin da na harba ya rikiɗe zuwa mutum – Sarkin Maharban Akko

Daga MOHAMMED ALI a Gombe Alhaji Lamido Muhammad, wanda aka fi sani da Sarkin Yaƙi, shine  Shugaban Rundunar Maharba na yankin Akko a Ƙaramar Hukumar Akko da ke cikin Jihar Gombe. Shi dai Alhaji Lamido ya yi suna da tasiri, saboda irin bajitarsa da gwagwarmaya a cikin dazuzzukan Gombe, musamman dazuzzukan Akko, wurin da ya yi fice saboda ƙungurumin dazuzzuka masu cike da  dabbobi da iskokai wasu halitttun ɓoye waɗanda a cewar maharba sai ka shirya za ka iya shiga cikin su. To amma, Alhaji Lamido shi waɗannan dazuzzuka tamkar gari ne ko gida a wurin shi. 'Na shige su…
Read More
Aikin albashin Naira 270,000 na ajiye na koma gyaran takalmi a zamance – Abubakar Sadik Umar

Aikin albashin Naira 270,000 na ajiye na koma gyaran takalmi a zamance – Abubakar Sadik Umar

Daga Ibrahim Hamisu, Kano Malam Abubakar Sadik Umar wani haziƙin mtashi ne ɗan baiwa da ya ke gyaran takalmi a zamanance a cikin ƙwaryar Birnin Kano. A hirarsa da Wakilin Manhaja, Ibrahim Hamisu a Kano, za ku ji irin yadda tsohon ɗan takarar Gwamna na Jihar Kano ya bayyana irin yadda ya ke gyara wa manyan mutane a Nijeriya takalmansu da kuma yadda ya ke biyan ma'aikatansa albashin Naira 350,000 a wata. Ku biyo mu. Za mu so ka gabatar mana da kanka?Sunana Abubakar Sadik Umar. An haife ni a shekarar 1973, a ƙaramar hukumar Gwaram, ta jihar Jigawa. Na yi…
Read More