24
Jul
Daga AMINU AMANAWA a Sakkwato Ƙasa da watanni biyu da soma mulkin Shugaban Ƙasa Bola Ahmad Tinibu al’umma na cigaba da bayyana damuwarsu kan kamun ludayin gwamnatin musamman a ɓangaren tsaro. A cewar galibin waɗanda Jaridar Manhaja ta zanta da su sun bayyana damuwar su, kan yadda duk da alƙawurran da gwamnatin Tinibun ta yi wa ‘yan ƙasa kan lamarin tsaro, al’umma ke cigaba da ɗanɗana kuɗar su sakamakon har-haren ‘yan bindiga musamman ma a jihohin Arewa maso Yammacin Nijeriya. Kwamared Bishir Dauda Sabon Unguwa Katsina, shi ne Babban Magatakardan Ƙungiyar Muryar Talaka a Nijeriya, a zantawar da wakilinmu a…
