Tattaunawa

Karamcin marubuta ne ya sa na zama marubuciya – Fadila Lamiɗo

Karamcin marubuta ne ya sa na zama marubuciya – Fadila Lamiɗo

"Ba ƙaramar asara masu satar fasaha ke jawo wa marubuta ba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubutan Jihar Kaduna kamar na sauran jihohi na ba da gagarumar gudunmawa ga cigaban harkokin adabi. Kama daga matakin ƙungiyoyi har zuwa a ɗaiɗaiku, Jihar Kaduna ta kasance sahun gaba wajen ƙyanƙyashe jajirtattun marubuta, masu ƙwazo da basira wajen ƙirƙirar labarai da ayyukan adabi iri daban daban. Fadila Lamiɗo, ɗaya ce daga cikin irin waɗannan marubuta masu ƙwazo da himma, kuma tun fara rubutun ta a shekarar 2016 ta samu karɓuwa da shahara cikin lokaci ƙanƙani. Ta kasance daga cikin matasan marubuta na onlayin da…
Read More
Macen da ba ta da abin yi na saurin gundurar namiji – Aisha Adamu Sadiq

Macen da ba ta da abin yi na saurin gundurar namiji – Aisha Adamu Sadiq

"Wasu matan babu ce ke jefa su halin rashin kamun kai" Daga AISHA ASAS Masu azancin zance suna cewa, sana’a goma maganin mai gasa. A wannan makon shafin Gimbiya na jaridar Manhaja ta ɗauko maku matashiya mai sana'ar sarrafa fara, siyar da abayoyi, akwatuna da ma haɗa lefe bakiɗaya. A tattaunawar Manhaja da matashiyar, ta tavo yadda sana'ar siyar da fara ke bayar da abin rufa asiri, saɓanin yadda mutane da dama suke kallonta a matsayin shiririta. Sannan kuma ta yi ƙarin haske kan yadda sana'arta ta haɗa lefe ke gudana. Babban fatanmu dai mata su amfana da wannan shafin,…
Read More
Soyayyata ga kayan gona ya sa na tsunduma sana’ar kayan gwari – Ummu Sodeeq

Soyayyata ga kayan gona ya sa na tsunduma sana’ar kayan gwari – Ummu Sodeeq

"Samarin yanzu ma sun fi son mace mai sana'a" Daga AISHA ASAS Mai karatu yau fa mun zo da abinda ba ku yada gani ba, mace da ta tabbatar da zancen ba sana'ar da namiji zai yi da mace ba zata iya ba matuƙar ta sa wa ranta za ta iya. A daidai wannan lokacin da mata suka miƙe, suka yi tarayya wurin kama sana'ar kayan qawa na mata da maza, kama daga tufafi, takalma zuwa huluna, gyale da sauransu, waɗanda su ne sana'oin da aka cika ganin mata na yi. A cikin haka ne, aka samu wata matashiya da…
Read More
Matasan marubuta ba sa son ana musu gyara – Mukhtar Ƙwalisa

Matasan marubuta ba sa son ana musu gyara – Mukhtar Ƙwalisa

"A rubutu na yi aure, na yi muhalli na kaina" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Ga duk wani tsohon makarancin littattafan Hausa, musamman littattafan labaran yaƙe-yaƙe da na barkwanci ba zai kasa sanin littattafan marubuci Mukhtar Ƙwalisa ba, wanda ya yi suna wajen tsara labarai masu ɗaukar hankali da sanya nishaɗi a zuciyar mai karatu. A wannan makon, shafin Adabi ya gayyato muku ɗan ƙwalisar marubuta, don jin abin da ya sa har yanzu yake ci gaba da wallafa littattafai duk kuwa da kasancewar takwarorinsa da dama yanzu harkar ta gagare su. A tattaunawar da suka yi da wakilin Blueprint Manhaja,…
Read More
Wacce ta ce jari ya hana ta sana’a, ba ta tashi yi ba – Hafsat Adamu 

Wacce ta ce jari ya hana ta sana’a, ba ta tashi yi ba – Hafsat Adamu 

"Ilimin 'ya mace har mijinta ke amfana" Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkan mu da sake ganin zagayowar sati lafiya. Kamar kowanne mako, shafin Gimbiya na yi maku tanadi na musamman wanda muke da tabbacin mata za su amfana ta vangarori da dama, ya Allah ya zama ƙwarin gwiwa ga wasu, wasu ya zama ilimi da zai taimaka masu wurin miƙewa neman na kai, yayin da yake zama allon kwaikwayo don saisaita rayuwarsu bisa ga turba da za ta tsirar da su. A wannan satin, mun samu baƙuncin wata matashiya da ta ɗauki sana'a da muhimmanci, mai sana'ar 'yankunne ce,…
Read More
Babu amfanin samun mace in har ba za ta taimaki mijinta ba – Jiddah Haulat Nguru (2)

Babu amfanin samun mace in har ba za ta taimaki mijinta ba – Jiddah Haulat Nguru (2)

"A wannan zamani sana'a kamar dole ta zamewa 'ya mace" Daga AISHA ASAS A satin da ya gabata, mai karatu idan bai manta ba, mun ɗauko fira da matashiya Jiddah Haulat Nguru, inda ta fara bayyana mana tarihi da kuma irin sana'ar da take yi, wadda ta tabbatar mana ana cin kasuwarta ne a kafafen sadarwa, sannan ta yi mana bayanin yadda ta fara, da hanyoyin da take bi don siya da siyar da kayanta a kafafe kamar Fesbuk, WhatsApp da sauransu. A wannan satin, za mu ɗora ne daga inda muka tsaya. Kamar yadda muka sanar, baƙuwar tamu za…
Read More
Matar da har yau ban san ta ba ce ta koya min yadda zan gyara rubutuna – Zee Kumurya

Matar da har yau ban san ta ba ce ta koya min yadda zan gyara rubutuna – Zee Kumurya

"Rashin haɗin kan marubta onlayin ne ya fi damuna" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A wannan makon muna ɗauke ne da tattaunawar da wakilin Blueprint Manhaja Abba Abubakar Yakubu ya yi da marubuciya Zainab Shehu Abdullahi, wacce aka fi sani da Zee Kumurya. A cikin tattaunawar tasu za ku ji yadda ta fara samun kanta a harkar rubutun adabi, da buƙatarta na ganin an samu haɗin kai da kyakkyawan jagoranci a tsakanin marubuta. A yi karatu lafiya. MANHAJA: Ina son ki gabatar mana da kanki? ZEE KUMURYA: To, Alhamdulillahi. Cikakken sunana shi ne Zainab Shehu Abdullahi, wacce aka fi sani da…
Read More
Muna so matasa su karkato ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askar Jihar Filato

Muna so matasa su karkato ga sana’o’in gargajiya – Sarkin Askar Jihar Filato

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A yayin da sana'o'in gargajiya daban-daban ke samun koma baya, saboda sauye sauyen zamani da rashin samun tallafin hukumomi. An fara ganin farfaɗowar wasu tsofaffin sana'o'in Hausawa na iyaye da kakanni da ke ƙoƙarin jawo hankalin matasa ga raya al'adunsu na gado, don samun abin dogaro. Harkar wanzanci na daga cikin waɗannan sana'o'in da daruruwan matasa ke cin abinci a cikinta, sakamakon sabbin jinin shugabanni da aka samu da ke ƙoƙarin inganta sana'ar da kuma ƙara kusantar da ƙungiyar raya harkar wanzanci ga gwamnati, don kawo wa sana'ar cigaba. Wakilin Blueprint Manhaja a Jos, ABBA ABUBAKAR…
Read More
Manufarmu ce tsamo matasa daga ƙangin talauci da aikata laifuffuka – Kwamaret Alkamatu

Manufarmu ce tsamo matasa daga ƙangin talauci da aikata laifuffuka – Kwamaret Alkamatu

Kamfanin Alkamatu Kamfani ne da ya yi fice a jahar Kano, wajen samar wa da al'umma mafita don dogaro da kai. Sannan suna samar wa da mutane bashi daga bankuna tare da tallafin kuɗaɗe don cigaba da kasuwanci don tsayawa da ƙafafunsu. Wakilin Blueprint Manhaja a Kano, Babangida S. Gora ya samu tattaunawa da Shugaban Kamfanin Alkamawa. Ga yadda tattaunawar ta kasance.  MANHAJA: Da farko za mu so mu ji da wa muke tare. ALKAMATU: Ni Sunana Alkamatu Hussaini Abdulƙadir, Kuma ni ne shugaban wannan kamfani na Alkamatu BrainBox Solutions. Mene ne manufarka ta samar da wannan kamfani? to kusan…
Read More
Henderson ya koma Al-Ettifaq ta Saudiyya

Henderson ya koma Al-Ettifaq ta Saudiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kyaftin ɗin Liverpool, Jordan Henderson ya koma Al-Ettifaq mai buga babbar gasar ƙwallon ƙafa ta Saudiyya. Ɗan ƙwallon tawagar Ingila, mai shekara 33 ya amince da ƙunshin yarjejeniyar fam miliyan 12 har da ƙarin tsarabe-tsarabe. A sakon ban kwana da ya yi wa Liverpool, ya ce zai bar ƙungiyar inda ya yi kaka 12, wadda ya lashe firimiya da Champions League a ita da sauran nasarori. Henderson yana Liverpool tun bayan da ya koma Anfield daga Sunderlandn kan fam miliyan 20 a watan Yunin 2011. Ya buga karawa 492 da cin ƙwallo 33 da bayar da…
Read More