05
Oct
"Ba ƙaramar asara masu satar fasaha ke jawo wa marubuta ba" Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Marubutan Jihar Kaduna kamar na sauran jihohi na ba da gagarumar gudunmawa ga cigaban harkokin adabi. Kama daga matakin ƙungiyoyi har zuwa a ɗaiɗaiku, Jihar Kaduna ta kasance sahun gaba wajen ƙyanƙyashe jajirtattun marubuta, masu ƙwazo da basira wajen ƙirƙirar labarai da ayyukan adabi iri daban daban. Fadila Lamiɗo, ɗaya ce daga cikin irin waɗannan marubuta masu ƙwazo da himma, kuma tun fara rubutun ta a shekarar 2016 ta samu karɓuwa da shahara cikin lokaci ƙanƙani. Ta kasance daga cikin matasan marubuta na onlayin da…
