27
Dec
Rashin tsaro na daga cikin manyan matsalolin da suka addabi arewacin Najeriya a yau. Abin ya kasance har kusan kowa ya sadaqar, an kasa kamo bakin zaren. A yayin da shugabannin yankin suke ta laluben yadda za a magance matsalar, da yawa kuma sun naxe hannu, sun haqura. Shin menene abin yi? Daya daga cikin dattijan Arewa da suke kwana suna tashi cikin tunanin yadda za a shawo kan al’amarin shi ne tsohon Gwamnan Jihar Sokoto, kuma tsohon xan takarar zama shugaban qasa, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa (Garkuwan Sokoto), wanda har qasida ya tava gabatarwa ga takwarorin sa manyan yankin…
