Mata A Yau

Ilimin ‘ya mace ya fi na namiji muhimmanci – Saratu Garba

Saratu Garba Hajiya Saratu G. Abdul ƙwararriyar malamar jinya ce kuma babbar ɗaliba wadda ta zage damtse a ɓangaren karatun aikin jinya tun a nan gida Nijeriya har zuwa ƙasashen ƙetare. A yanzu haka ta na ƙasar Amurka ta na ci gaba da karatun digiri na uku a ɓangaren aikin jinya. Saratu Garba Abdullahi dai ta na sahun farko kuma gaba-gaba a rukunin matan da su ka samu ilimi mai zurfi a arewacin Nijeriya, musamman ma a ɓangaren aikin jinya da ta ke cigaba da neman ilimi da ƙwarewa a kai. An dai ce waƙa a bakin mai ita ta…
Read More
Babban buri na shi ne in gina gidan marayu – Fauziyya D. Sulaiman

Babban buri na shi ne in gina gidan marayu – Fauziyya D. Sulaiman

Daga AISHA ASAS Sunan ki sananne ne, sai dai jin tarihin ki ne abin buƙatar masu karatu.Suna na Fauziyya D. Sulaiman. An haife ni a unguwar Fagge ta garin Kano a shekarar 1988. Na yi karatun Islamiyya a makarantar Maikwaru da ke Fagge da firamare ta ‘Festival Special Primary School’. Daga nan na tafi makarantar kwana ta ‘Yargaya inda na yi shekara uku, sannan na dawo makarantar ‘yan mata ta GGC Dala inda a nan na kammala karatu na. Daga nan na yi aure a 1999. A shekarar 2002 na koma karatu na yi difloma a ‘College of Hygiene’ a…
Read More
Idan da goyon baya mata kaɗai na iya ciyar da ƙasa – SWOFON

Idan da goyon baya mata kaɗai na iya ciyar da ƙasa – SWOFON

Daga BASHIR ISAH Kodinetar Ƙungiyar Ƙananan Manoma Mata (SWOFON) ta jihar Bauchi, Hajiya Marka Abbas, ta ƙarfafa cewa mata kaɗai na iya ciyar da ƙasa muddin suka samu goyon bayan da suke buƙata. Marka ta bayyana haka ne a wajen wani taron musayar ra'ayi game da harkokin noma, shiryawar ƙungiyar ‘Fahimta Women and Youth Development Initiative’ (FAWOYDI) tare da haɗin gwiwar ActionAid Nigeria, wanda ya gudana ran Litinin, a Bauchi. A cewarta mata sun fi maza iya tattali ta yadda za su iya amfani da kayan aiki kaɗan wajen samar da amfani mai yawa. Don haka ta yi kira ga gwamnati…
Read More
Duk wadda ta zauna za ta ga zaunau – Fatima Yusuf Muhammad

Duk wadda ta zauna za ta ga zaunau – Fatima Yusuf Muhammad

Fatima Yusuf Muhammad ta kasance mace mara kasala wajen fafutikar neman ilimi, sana’ar dogaro da kai da kuma faɗakar da al’umma da nishaɗantar da su ta hanyar rubuce-rubucen littattafan hikaya. A wannan makon Manhaja ta yi wa masu karatu kiciɓis da ita don jin yadda ta ke jifar tsuntsaye uku da dutse ɗaya, ma’ana ga neman ilimi da ta sa gaba, sana’a da kuma rubutu, ga kuma ɗawainiyar iyali. Kai, wani aiki dai sai mai shi. Ga yadda tattaunar ta kasance:  Masu karatu zasu so jin tarihin ki.Ni dai suna na Fatima Yusuf Muhammad. An haife ni a garin Kaugama…
Read More
Ya kamata gwamnati ta dinga sa mata wakilci domin samun hanyar tallafa wa mata

Ya kamata gwamnati ta dinga sa mata wakilci domin samun hanyar tallafa wa mata

Hajiya Zainab Sani Giwa mace ce ‘yar gwagwarmaya kuma mai son cigaban mata ‘yan’uwan ta ta fuskar wayewa da zamantakewa da kuma samun abin dogaro da kai. Ta yi fice sosai musamman a Ƙaramar Hukumar Giwa da ke Jihar Kaduna saboda kasancewar ta shugabar mata a yankin. A tattaunawar ta da jaridar Manhaja, masu karatu za su ji irin faxi-tashin da ta ke yi wajen faranta ran mata da marasa galihu. Daga AISHA ASAS a Abuja Masu karatu za su so jin cikakken suna da tarihin ki a taƙaice.Assalamu alaikum. To alhamdu lillahi, suna na Zainab Sani Giwa. Ni haifaffiyar…
Read More
An daina kishi na faɗan baki, sai na ƙwandala – Khadija Mahuta

An daina kishi na faɗan baki, sai na ƙwandala – Khadija Mahuta

Hajiya Khadija Abdulrasheed Mahuta mace ce wadda ya kamata mata su yi koyi da ita, kasancewar ta jaruma kuma tsayayya, sannan da ta san ciwon kan ta. Ta kasance cikin jerin mata da su ke tauna taura biyu a lokaci guda. Ma’ana, mace ce wadda ba ta zauna ba don jiran sai wani ya samo ya kawo mata, a’a, ta tashi tsaye ne haiƙan wajen rufa wa kan ta asiri. Wakiliyar Manhaja ta tattauna da ita inda ta bayyana wa masu karatu rayuwar ta wadda za ta iya zama makaranta ga mata. Daga AISHA ASAS Masu karatu za su so…
Read More
Ina daga cikin mutanen farko da su ka kafa Kannywood – Zainab Ahmad

Ina daga cikin mutanen farko da su ka kafa Kannywood – Zainab Ahmad

Hajiya Zainab Ahmad mace ce mai kamar maza kuma ‘yar gwagwarmaya da fafutikar nema wa marasa ƙarfi ko galihu haƙƙin su a wajen waɗanda su ka tauye ma su haƙƙin, da kuma kiraye-kiraye ga Gwamnati da tunasar da ita akan haƙƙin da ya rataya a wuyan ta, musamman ma a Arewacin Nijeriya inda ake fama da matsanancin rashin tsaro. Hajiya Zainab Ahmad ta yi fice a ɓangaren ayyukan agaji da taimakon al’umma wajen shige musu gaba don kwato ‘yancin su. Ga dai hirar da wakiliyar Manhaja ta yi da ita: Daga AISHA ASAS Mu fara da jin tarihin ki a…
Read More
Mace da kwalliya aka san ta

Mace da kwalliya aka san ta

Daga MARYAM ABDURAHMAN Mace da kwalliya aka san ta, wacce ba ta kwalliya ba ta cika mace a zahirin ta ba. Babu mace mummuna sai dai macen da ba ta kwalliya. Sai dai kwalliyar ma kala-kala ce, wasu kwalliyar suna su ka tara, don ba zai yiwu a shafa 'foundation' a fuskar da ba ta da haske a yi tsammanin samun kwalliyar raɗau ba. In nace haske ba ina nufin farin fata ba, ina nufin ƙyalli na gyara. Yawancin mutanen mu suna tsorata da maganar kayan gyaran jiki don tsadar su, a rashin sanin su da kuɗi ƙalilan za su…
Read More
Lokacin siyasa ne lokacin da na fi so – Farida Abubakar

Lokacin siyasa ne lokacin da na fi so – Farida Abubakar

Daga AISHA ASAS Hajiya Farida Abubakar mace mai kamar maza, wadda ta ke da kishin neman na kanta ba tare da jiran miji ko iyaye sun yi mata hidimar ta ba, kuma macen da ta riƙi sana’ar gasa Burodi da hannu bibbiyu, wadda har ta kai ta matsayin da ta ke a yanzu. mace ce da ya kamata mata su yi koyi da ita, domin ta haɗa taura biyu a lokaci guda, wato aiki da kasuwanci. A wannan hirar da wakiliyar mu ta yi da ita, masu karatu za su ji yadda ta fara wannan sana’a. Masu karatun mu za…
Read More
Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Daga Aisha Asas Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya ja hankulan 'yan Nijeriya a kan su daina barin son zuciyarsu yana tasiri wajen daukar matakai wanda hakan ka iya haifar da rikici. Makarfi ya nuna bukatar da ke akwai 'yan Nijeriya su fahimci cewa matsalar tsaron da ke addabar kasar nan aba ce da ke bukatar a yi mata taron dangi domin dakile ta. Yana mai cewa, "Wannan matsala ce da ta shafe mu baki daya." Makarfi ya yi wadannan bayanan ne a wata sanarwa da ya fitar inda ya nuna damuwarsa kan tabarbarewar sha'anin tsaron Nijeriya.…
Read More