05
Mar
Hajiya Zainab Sani Giwa mace ce ‘yar gwagwarmaya kuma mai son cigaban mata ‘yan’uwan ta ta fuskar wayewa da zamantakewa da kuma samun abin dogaro da kai. Ta yi fice sosai musamman a Ƙaramar Hukumar Giwa da ke Jihar Kaduna saboda kasancewar ta shugabar mata a yankin. A tattaunawar ta da jaridar Manhaja, masu karatu za su ji irin faxi-tashin da ta ke yi wajen faranta ran mata da marasa galihu. Daga AISHA ASAS a Abuja Masu karatu za su so jin cikakken suna da tarihin ki a taƙaice.Assalamu alaikum. To alhamdu lillahi, suna na Zainab Sani Giwa. Ni haifaffiyar…