Mata A Yau

Ni ce mace ta farko da aka fara ba wa shugabar jam’iya a Katsina – Mariya Abdullahi

Ni ce mace ta farko da aka fara ba wa shugabar jam’iya a Katsina – Mariya Abdullahi

“Na yi tafiye-tafiya da Obasanjo don neman a yafe wa Nijeriya bashin da ake bin ta” Daga UMAR GARBA, a Katsina Hajiya Mariya Abdullahi gogaggiyar ma'aikaciyar gwamnati ce wadda ta yi aiki a ma'aikatu daban-daban kama daga Jihar Katsina, sauran jihohin ƙasar nan da ma ƙasashen ƙetare, ta kuma kasance shahararriyar 'yar siyasa da ta yi takara kuma ta samu nasarar zama shugabar ƙaramar hukuma, mai bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Umaru Musa Yar'adua shawara ta musamman, kwamishiniyar yaɗa Labarai, ta kuma taɓa kasancewa mamba a majalisar wakilan Tarayyar Nijeriya. Manhaja ta tattauna da Hajiya Mariya Abdullahi akan batutuwan da…
Read More
A Nijeriya ne kawai miji zai bushi iska ya kori matarsa daga gida gwamnati ta ƙyale shi – Uwani Kazaure

A Nijeriya ne kawai miji zai bushi iska ya kori matarsa daga gida gwamnati ta ƙyale shi – Uwani Kazaure

“Laulayin ciki ne babban ƙalubalena a wurin aiki” Daga UMAR AƘILU MAJERI Hajiya Uwani tsohuwar malamar makaranta ce kuma masaniya akan yaren Turanci da Hausa. Ta kasance ɗaya daga cikin Mata 'yan gwagwarmayar nema wa Mata da ƙananan Yara 'yanci a Jihar Jigawa. Yanzu haka Hajiya Uwani ta fara tunanin kafa wata gidauniya mai zaman kanta saboda ta riƙa taimaka wa yara matan da aka ci zarafinsu, don ganin ta kare masu mutuncinsu kamar yadda sauran al'umma suke da. Wakilinmu na Jihar Jigawa, Umar Aƙilu Majeri ya samu nasarar zantawa da ita a gidanta da ke Dutse. Ga yadda tattaunawar ta…
Read More
Ilimin ‘ya’yan Fulani na da muhimmanci a wannan zamani – Hauwa Umar Aliyu

Ilimin ‘ya’yan Fulani na da muhimmanci a wannan zamani – Hauwa Umar Aliyu

Daga ABUBAKAR TAHEER a Haɗeja Mai karatu wannan tattaunawa ce ta musamman da Hauwa Umar Aliyu, matar da ta fito daga rugar Fulani, kuma mai taimakon mata da marasa galihu. Ta fito daga garin Birniwa na Jihar Jigawa. Ta yi gidauniya mai suna Iya Hauwa Foundation. A sha karatu lafiya: MANHAJ: Mu fara da jin tarihinki a taƙace Sunana Hauwa Umar Aliyu. 'Yar Ƙaramar Hukumar Birniwa ce a Jihar Jigawa. Ni Bafilatana ce daga riga, saboda ban ma iya Hausa ba a lokacin da yayar Mahaifina da ke zaune a Kano ta ɗauke ni ta tafi da ni Kanon. Kafin…
Read More
Ya kamata gwamnati ta fito da tsarin da zai hana matan Fulani kiwo – Ramatu Muhammed

Ya kamata gwamnati ta fito da tsarin da zai hana matan Fulani kiwo – Ramatu Muhammed

“Mafi yawan mata masu yoyon fitsari Fulani ne” - Ramatu Daga UMAR AKILU MAJERI, a Dutse Hajiya Ramatu Muhammed tsohuwar malamar makaranta ce. Ta kasance bafilatana mai kishin yarenta, tare da son taimakon marasa galihu. Hajiya Ramatu na ɗaya daga cikin malamai da ake alfahari dasu a cikin makarantun ‘ya’ya Mata da suke taimaka wa wajan baiwa ɗalibai tarbiyar da ake alfahari dasu a Jahar Jigawa. Yanzu haka malama Ramatu itace babbar sakatariya mai cikakken iko a Hukumar Raya ilimin ‘yayan Fulani makiyaya a ma'aikatar ilimi ta Jahar Jigawa ,kafin takai ga wannan matsayin, ta tava riƙe muƙamin daraktan makarantun…
Read More
Mijina ne ya dasa min sha’awar yin takara – Halima Amadu Jabiru

Mijina ne ya dasa min sha’awar yin takara – Halima Amadu Jabiru

“Ba zai yiwu a samu cigaba ba tare da gudunmawar mata ba” - Halima Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Hon. Halima Amadu Jabiru gogaggiyar ’yar siyasa ce da ta daɗe ta kuma ƙware a harkar siyasar Jihar Nasarawa da ƙasa bakiɗaya. Ta fito takarar kujerun siyasa da dama a jihar. Ta na daga cikin yan siyasa da su ka fara kafa jamiyyar PDP a jihar kafin daga baya ta canja sheka zuwa APC. A yanzu ita ce Kwamishiniyar Ma’aikatar mata da bunƙasa walwalar jama’a a Jihar Nasarawa. A tattaunawarta da wakilinmu a ofishinta da ke ma’aikatar a Lafiya, ta…
Read More
Namiji tamkar bishiya ne, idan ya faɗi mata da yawa za su shiga matsala- Hauwa Bala Geidam

Namiji tamkar bishiya ne, idan ya faɗi mata da yawa za su shiga matsala- Hauwa Bala Geidam

Ƙarancin imani ne ke sa mata kashe mazajensu, ba rashin so ba - Hauwa Bala Geidam Yanzu dai mata sun fahimci ma’anar wadda ta zauna za ta ga zannau, domin sun miƙe haiƙan wurin ganin sun taimaki kan su har ma da mata ‘yan’uwan su da su ke cikin mawuyacin hali. A wannan satin shafin mata a yau na wannan jarida mai farin jini ya samu damar zaƙulo wa masu karatu ɗaya daga cikin matasan mata da ke kishin ‘yan’uwan su mata har ma da ƙananan yara. Hajiya Hauwa Bala Geidam mace da ta amsa sunan ta na mace a…
Read More
Koyon girki ba wai ga yaya mata kawai ya kamata ya tsaya ba, har da maza- Fatima Gwadabe

Koyon girki ba wai ga yaya mata kawai ya kamata ya tsaya ba, har da maza- Fatima Gwadabe

*An wuce lokacin bawa mata shawarar su nemi sana'a saboda abu ne da yake a fili - Fatima Gwadabe Fatima Gwadabe suna ne da ya karaɗe ƙasar nan musamman a wajen mata da ke kallon tashar Arewa24, domin kuwa Fatima Rabiu Gwadabe ƙwararriya ce da ta ke koyar da girki irin na Afirka, na Turawa da na gargajiya. Fatima Gwadabe ta shekara 3 ta na koyar da girke-girke daban-daban a tashar Arewa24, kuma ta samu kyautuka masu yawa a wannan ɓangare. A hirar ta da wakilinmu a Kano za ku ji tarihinta da kuma yadda shirin ya samo asali: Daga…
Read More
HOTUNA: Taron horar da ma’aikatan hukumar NAHCON

HOTUNA: Taron horar da ma’aikatan hukumar NAHCON

Ranar farko kenan ta bada horo kan shirin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da 'yan kasuwa (PPP) wajen gina al'umma, wanda hukumar ICRC ta shirya a babban zauren taro na Hukumar Hajji ta Ƙasa (NAHCON) a ranar Laraba. Mahalarta taron sun haɗa da Shugaban hukumar NAHCON na ƙasa, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, Kwashinan NAHCON, Alhaji Abdullahi Magaji Hardawa da sauran ma'aikatan NAHCON Staff. Zauren taro Zauren taro Zauren taro
Read More
Ina son kafa gidauniya, sai dai ba na son a yayata manufuta – Zainab Santali

Ina son kafa gidauniya, sai dai ba na son a yayata manufuta – Zainab Santali

Daga UMAR AƘILU MAJERI a Jigawa Zainab Baba Aliyu Santali fitacciyar malamar makaranta ce a yankin masarautar Kazaure, kuma ita ce mace ta farko a Jihar Jigawa da take aikin jami'ar hulɗa da jamaa a jihar. Ta kasance ɗaya daga cikin mata matasa masu kishin addini. Wakilin MANHAJA a Jihar Jigawa ya zanta da ita a ofishin ta don jin wasu batutuwa da suka shafi rayuwar ta da kuma faɗi-tashin da ta sha. Ga yadda tattaunawar ta kasance: Ma su Karatu za su so ki gabatar musu da kanki a taƙaice?Assalamu alaikum. To Alhamdulillahi ni dai sunan Zainab Baba Aliyu…
Read More
Fushin miji na

Fushin miji na

Daga AISHA ASAS Zamani ya kai mu lokacin da mata ke ganin damuwa da fushin miji zubar da aji ne. yayin da waɗansu ke kallon sa a matsayin rashin sanin ciwon kai. A cewar wasu ƙyale shi har ya gaji ya huce dan kan sa. Waɗansu matan kuwa cewa suke yi “idan ka nuna wa namiji ka na tsoron fushinsa to kin zama marainiyar shi. Kuma ai da ma namiji ba ɗan goyo ba ne. Kuma duk wadda ta ɗauke shi uba za ta mutu marainiya." To uwar gida, ya aka yi ki ka tsufa da gatanki a ƙarƙashin inuwar…
Read More