03
Nov
“Na yi tafiye-tafiya da Obasanjo don neman a yafe wa Nijeriya bashin da ake bin ta” Daga UMAR GARBA, a Katsina Hajiya Mariya Abdullahi gogaggiyar ma'aikaciyar gwamnati ce wadda ta yi aiki a ma'aikatu daban-daban kama daga Jihar Katsina, sauran jihohin ƙasar nan da ma ƙasashen ƙetare, ta kuma kasance shahararriyar 'yar siyasa da ta yi takara kuma ta samu nasarar zama shugabar ƙaramar hukuma, mai bai wa tsohon Shugaban Ƙasa Umaru Musa Yar'adua shawara ta musamman, kwamishiniyar yaɗa Labarai, ta kuma taɓa kasancewa mamba a majalisar wakilan Tarayyar Nijeriya. Manhaja ta tattauna da Hajiya Mariya Abdullahi akan batutuwan da…