Mata A Yau

Mace da kwalliya aka san ta

Mace da kwalliya aka san ta

Daga MARYAM ABDURAHMAN Mace da kwalliya aka san ta, wacce ba ta kwalliya ba ta cika mace a zahirin ta ba. Babu mace mummuna sai dai macen da ba ta kwalliya. Sai dai kwalliyar ma kala-kala ce, wasu kwalliyar suna su ka tara, don ba zai yiwu a shafa 'foundation' a fuskar da ba ta da haske a yi tsammanin samun kwalliyar raɗau ba. In nace haske ba ina nufin farin fata ba, ina nufin ƙyalli na gyara. Yawancin mutanen mu suna tsorata da maganar kayan gyaran jiki don tsadar su, a rashin sanin su da kuɗi ƙalilan za su…
Read More
Lokacin siyasa ne lokacin da na fi so – Farida Abubakar

Lokacin siyasa ne lokacin da na fi so – Farida Abubakar

Daga AISHA ASAS Hajiya Farida Abubakar mace mai kamar maza, wadda ta ke da kishin neman na kanta ba tare da jiran miji ko iyaye sun yi mata hidimar ta ba, kuma macen da ta riƙi sana’ar gasa Burodi da hannu bibbiyu, wadda har ta kai ta matsayin da ta ke a yanzu. mace ce da ya kamata mata su yi koyi da ita, domin ta haɗa taura biyu a lokaci guda, wato aiki da kasuwanci. A wannan hirar da wakiliyar mu ta yi da ita, masu karatu za su ji yadda ta fara wannan sana’a. Masu karatun mu za…
Read More
Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Matsalar Tsaro: Makarfi ya gargadi ‘yan Nijeriya

Daga Aisha Asas Tsohon gwamnan Jihar Kaduna Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya ja hankulan 'yan Nijeriya a kan su daina barin son zuciyarsu yana tasiri wajen daukar matakai wanda hakan ka iya haifar da rikici. Makarfi ya nuna bukatar da ke akwai 'yan Nijeriya su fahimci cewa matsalar tsaron da ke addabar kasar nan aba ce da ke bukatar a yi mata taron dangi domin dakile ta. Yana mai cewa, "Wannan matsala ce da ta shafe mu baki daya." Makarfi ya yi wadannan bayanan ne a wata sanarwa da ya fitar inda ya nuna damuwarsa kan tabarbarewar sha'anin tsaron Nijeriya.…
Read More
Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Daga Umar Gombe Bayanan da jaridar Manhaja ta samu daga Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, sun nuna Shugaba Muhammadu Buhari ya nada sabbin hafsoshin sojin Nijeriya. Wadanda nadin ya shafa su ne; Major General Leo Irabor a matsayin babban hafsan tsaron kasa da Maj. Gen. I Attairu a matsayin babban hafsan sojojin kasa, sai A Z Gambo a matsayin babban hafsan sojojin ruwa da kuma AVM IO Alao a msatsayin babban hafsan sojojin Sama. Kafin wannan lokaci, 'yan Nijeriya da dama sun yi ta bayyana ra'ayoyinsu kan bukatar da ke akwai na yi wa shugabannin sojoji garambawul don inganta…
Read More
‘Yan-bindiga sun kai hare-hare a sassan Neja

‘Yan-bindiga sun kai hare-hare a sassan Neja

Daga jaridar Manhaja 'Yan-bindiga sun kai hare-hare a wasu kauyukan karamar hukumar Paikoro da ke Jihar Neja, inda suka hallaka mutum shida tare da yin garkuwa da mutum biyar sannan suka jikkata sama da mutum 20. Bayanai daga jihar sun nuna 'yan-bindigar sun soma ta'addacinsu ne daga Asabar da ta gabata zuwa washegari Lahadi da rana. Wani mazaunin daya daga cikin kauyukan da harin ya shafa mai suna Abubakar Azaido, ya shaida wa Manhaja ta tarho cewa sama da mutum 20 da suka jikkata a harin aka kai babbar asibitin Kafin Koro. Ya ce, akalla mutum 3000 ne suka tsere…
Read More