15
Mar
Daga BASHIR ISAH Kodinetar Ƙungiyar Ƙananan Manoma Mata (SWOFON) ta jihar Bauchi, Hajiya Marka Abbas, ta ƙarfafa cewa mata kaɗai na iya ciyar da ƙasa muddin suka samu goyon bayan da suke buƙata. Marka ta bayyana haka ne a wajen wani taron musayar ra'ayi game da harkokin noma, shiryawar ƙungiyar ‘Fahimta Women and Youth Development Initiative’ (FAWOYDI) tare da haɗin gwiwar ActionAid Nigeria, wanda ya gudana ran Litinin, a Bauchi. A cewarta mata sun fi maza iya tattali ta yadda za su iya amfani da kayan aiki kaɗan wajen samar da amfani mai yawa. Don haka ta yi kira ga gwamnati…
