Wasanni

Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Gasar Zakarun Turai: Arsenal da Barcelona sun kai zagayen kusa da ƙarshe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Arsenal ta kai zagayen daf da na kusa da na ƙarshe, bayan da ta yi nasara a kan FC Porto da cin 4-2 a bugun fenariti ranar Talata a Emirates. Tun farko Arsenal ce ta ci 1-0 ta hannun Leandro Trossard saura minti hutu su je hutu, irin wannan sakamakon Porto ta samu a Portugal a wasan farko. Hakan ne ya sa aka yi ƙarin lokaci daga nan aka je bugun daga kai sai mai tsaron raga. Gunners ta ci ƙwallaye a bugun fenariri ta hannun Odegaard da Kai Havertz da Bukayo Saka da kuma Declan…
Read More
An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

An dakatar da ’yan wasan Kamaru 62 saboda zaftare shekaru

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Kamaru ta dakatar da 'yan wasan ƙasar 62 bisa laifin coge wajen bayyana shekaru, cikinsu har da matashi mafi ƙarancin shekaru a tawagar da ta buga gasar kofin nahiyar Afirka da aka yi a watan Janairu. Hukumar ta FECAFOOT ta fitar da jerin sunayen a hukumance a ƙarshen wannan makon, ciki harda Wilfried Nathan Douala mai shekaru 17 wanda ya ba da mamaki cikin tawagar Rigobert Song a gasar da aka kammala a Ivory Coast. A cewar FECAFOOT, mai tsaron ragar Victoria United ya yi ƙarya game da shekarunsa, don haka an hana…
Read More
La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

La Liga za ta binciki batun cin zarafin Vinicius

Daga MAHDI M. MUHAMMAD La Liga na nazarin wani bidiyo da ake zargin yana nuna wariyar launin fata ga Vinicius Jr a wasan da Real Madrid ta buga da Valencia a ƙarshen makon da ya gabata. Bidiyon da aka wallafa a shafukan sada zumunta na Intanet ya nuna yadda wani yaro mai goyon bayan Valencia ke jagorantar cin zarafin ɗan wasan. Vinicius ya zura ƙwallaye biyu a wasan da suka tashi 2-2 a ranar Asabar kuma ya yi murna ta hanyar ɗaga hannunsa sama. Ɗan wasan mai shekaru 23 ya fuskanci cin zarafi na wariyar launin fata sau da dama…
Read More
Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Ahmed Musa ya dakatar da kwantiraginsa da Sivasspor ta Turkiyya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rahotanni sun bayyana cewa kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa ya soke kwantiraginsa da ƙungiyar Sivasspor ta Turkiyya. An kawo ƙarshen kwantiragin tsakanin Musa da Sivasspor ta hanyar yarjejeniya. Ɗan wasan mai shekaru 31 ya ɗauki matakin ne bayan ƙungiyar ta kasa biyan albashin sa na watanni shida da suka gabata. Ɗan wasan gaba ya riga ya fara aiki don komawa wani kulob a lokacin bazara. Musa ya koma Sivasspor daga wata ƙungiyar Turkiyya Fatih Karagumruk a shekarar 2022. Ya buga wasanni tara a ƙungiyar ba tare da samun nasarar zura ƙwallo ko ɗaya a raga…
Read More
Rashin ɗa’a: An dakatar da Ronaldo wasa ɗaya a Al-Nassr

Rashin ɗa’a: An dakatar da Ronaldo wasa ɗaya a Al-Nassr

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An dakatar da ɗan ƙwallon Al-Nassr Cristiano Ronaldo daga buga wasa ɗaya saboda tanka wa ’yan kallo a wasan da suka doke Al-Shabab a gasar ƙwallon Saudiyya. Magoya bayan Al-Shaabab sun yi ta ihun sunan 'Messi', mutumin da ya kasance babban abokin hamayyar Ronaldo. Al-Nassr ta samu nasara a wasan da ci uku da biyu a birnin Riyadh. Kyaftin ɗin Portugal mai shekaru 39, ya rufe kunnensa sannan ya yi wata alama da hannu. Hukumar ƙwallon Saudiyya - SAFF ta kuma ci tarar Ronaldo ɗin Riyal dubu 30. Kwamitin ɗa'a na ƙwallon Saudiyyar ya ce Ronaldo…
Read More
Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yi murabus

Kocin Super Eagles, Jose Peseiro ya yi murabus

Daga BASHIR ISAH Jose Peseiro ya murabus a matsayin mai horar da 'yan wasan Super Eagles na Nijeriya. Peseiro ya sanar da hakan ne a shafinsa na X a ranar Juma'a, 1 ga Maris, 2024. Ya ce kwatiraginsa da Hukumar Ƙwallon Ƙafa ta Nijeriya (NFF) ta ƙare, kuma ba a ƙulla sabo ba. Ya bayyana watanni 22 da ys shafe a matsayin babban kocin Super Eagles, a matsayin sadaukarwa. Ya kuma yi amfani da wannan dama wajen nuna godiya ga 'yan wasan na Super Eagles da hukumar NFF, yana mai cewa a duk lokacin da aka buƙace za a same…
Read More
Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Kocin Bayern, Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar a ƙarshen kakar bana

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Koci Thomas Tuchel zai bar ƙungiyar Bayern Munich a ƙarshen kakar wasa ta bana. Ɗan shekaru 50 ɗin ya maye gurbin Julian Nagelsmann a watan Maris din 2023, inda ya ƙulla yarjejeniyar har zuwa watan Yunin 2025. Sai dai tsohon kocin Chelsea ɗin zai raba gari da ƙungiyar saboda "sauye-sauyen da Bayern ke yi". Tuchel ya jagoranci Bayern lashe gasar Bundesliga a kakar wasan da ta wuce amma a yanzu Bayer Leverkusen ta basu tazarar maki takwas. Sannan kuma an doke Bayern a wasa uku a jere. Shugaban Bayern, Jan- Christian Dreesen ya ce "duka ɓangarorin…
Read More
Laifin fyaɗe: Kotu ta yanke wa Dani Alves hukuncin ɗaurin shekara huɗu da rabi

Laifin fyaɗe: Kotu ta yanke wa Dani Alves hukuncin ɗaurin shekara huɗu da rabi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A ranar Alhamis ne wata kotu a ƙasar Sifaniya ta yanke wa tsohon ɗan wasan Brazil Dani Alves hukuncin ɗaurin shekara huɗu da rabi bayan samunsa da laifin yi wa wata budurwa fyaɗe a wani gidan rawa na Barcelona a watan Disamban 2022. Wata sanarwa da kotun Barcelona ta fitar ta ce "Wadda abin ya shafa ba ta yarda ba." Masu gabatar da ƙara sun buƙaci da a yanke wa ɗan wasan da ya lashe gasar zakarun Turai hukuncin ɗaurin shekaru tara a gidan yari, sai kuma na shekaru 10 na gwaji. Ɗaya daga cikin 'yan…
Read More
Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Rahana Ibrahim Bunzawa wacce ta lashe gasar iyo (Linƙaya) wato tsere cikin ruwa ta ce ta yi bankwana da wannan wasa na ruwa har abada. Ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke ganawa da wakilinmu a garin Yawuri jim kaɗan bayan kammala bikin 'Rigata' da aka gudanar kwanan nan. Ta ce wannan shi ne karo na biyu da ta ke lashe wannan gasar a jere kuma a duk lokacin da ta shiga ita ce samun nasara saboda haka ta yi bankwana da shiga gasar Rigata daga bana. "Na soma shiga gasar tun…
Read More
HOTUNA: Yadda aka yi zagayen gari da kofin da Ivory Coast ta lashe a Gasar AFCON 2023

HOTUNA: Yadda aka yi zagayen gari da kofin da Ivory Coast ta lashe a Gasar AFCON 2023

A ranar Talata mazauna Abidjan, babban birnin kasar Ivory Coast, suka yi dafifi a wasun manyan hanyoyin birnin domin tarbar 'yan wasan kasar dauke da kofin da suka lashe a Gasar AFCON 2023 da aka kammala a Lahadin da ta gabata. Ivory Coast ta zama zakaran gasar ce bayan da ta doke Super Eagle na Nijeriya da ci 2 da 1. Ga karin hotuna daga zagayen garin da aka yi da kofin Abidjan:
Read More