Kocin ƙasar Brazil, Carlo Ancelotti, ya tayar da muhawara a fagen dabarun ƙwallon ƙafa bayan ya jaddada cewa tsaron gida mai ƙarfi ne ginshiƙin nasarar lashe Gasar Kofin Duniya na FIFA, ba yawan cin ƙwallaye ba.
Ancelotti ya bayyana haka ne yayin wata ganawar manema labarai da aka gudanar kafin wasan sada zumunci tsakanin Brazil da Croatia a Orlando, inda ya ce tarihin gasar ya nuna cewa ƙungiyar da ke rage yawan ƙwallayen da ake zura mata ita ce mafi yawan lashe kofin.
A cewarsa, duk da cewa kai hari yana buƙatar ƙwarewa da basira, tsaron gida yana buƙatar tsari mai kyau da haɗin kai — wani fanni da ya ce shi ne zai fi mayar da hankali wajen horas da ‘yan wasansa.
Ya ce, “Ba wanda ya fi cin ƙwallaye ne ke lashe Kofin Duniya ba, wanda ya fi kare ragarsa daga zura ƙwallo ne ke cin nasara.”
Duk da wannan ra’ayi, tsohon kocin na Italiya ya ƙaryata zargin cewa shi koci ne mai fifita tsaro kawai, yana mai tunatar da nasarorin da ya samu a baya da ƙungiyoyin da suka yi fice wajen cin ƙwallaye, sai dai ya jaddada cewa tsaro muhimmin ginshiƙi ne a irin manyan gasa kamar Kofin Duniya.
Ancelotti ya kuma bayyana cewa dabararsa na nufin samar da yanayi da zai bai wa taurarin Brazil damar haskawa, musamman ‘yan wasa irin su Vinicius Junior da Raphinha, ba tare da barin ƙungiyar cikin haɗari ba.
Wannan tsari na zuwa ne yayin da Brazil ke shirin fara gasar 2026 FIFA World Cup da Moroko a ranar 13 ga Yuni, bayan wasu wasannin gwaji da suka haɗa da rashin nasara da ci 2-1 a hannun Faransa a Boston.
A ƙarshe, kocin ya bayyana cewa zaɓin ’yan wasansa zai dogara ne kan lafiyar jiki da kuma ɗabi’a, ba suna ko shahara ba. Wannan ya bayyana dalilin da ya sa ya bar fitaccen ɗan wasa Neymar daga cikin jerin ’yan wasan da ya gayyata, yana mai cewa sai waɗanda ke cikin cikakkiyar ƙoshin lafiya ne za su samu damar buga gasar.
Haka kuma, rahotanni sun nuna cewa Hukumar ƙwallon ƙafa ta Brazil na ƙoƙarin tsawaita kwantiragin Ancelotti har zuwa gasar Kofin Duniya ta 2030, alamar amincewa da tsare-tsarensa na dogon lokaci.
