10
Apr
Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya (FIFA), ta tabbatar da cewa tana duba wani shiri da aka gabatar na faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta shekarar 2030 zuwa ƙasashe 64, a wani yunƙuri na bikin cika shekara 100 da fara gasar. Rahotanni sun nuna cewa wannan ra’ayi ya samo asali ne daga shugaban ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta ƙasar Uruguay, Ignacio Alonso, a wani taron majalisar FIFA da aka gudanar a watan Maris na shekarar 2025. Daga bisani, ƙungiyar ƙasashen Kudancin Amurka ta CONMEBOL ta gabatar da wannan shawara a hukumance, inda shugabanta Alejandro Domínguez ya bayyana cewa hakan zai bai wa duk…
