Wasanni

Arsenal na sa ran lashe Carabao Cup domin dawo da martabarta – Timber

Arsenal na sa ran lashe Carabao Cup domin dawo da martabarta – Timber

Jurrien Timber na ganin cewa lashe kofin Carabao Cup na iya zama wata hanya ta buɗe ƙofofin samun manyan nasarori ga Arsenal a wannan kakar ta bana. Kungiyar da Mikel Arteta ke jagoranta tana daf da kawo ƙarshen shekara shida ba tare da kofi ba, bayan da ta doke Chelsea a filin Emirates 1-0, kenan ta kai wasan ƙarshe da cin 4-2 gida da waje. Arsenal ta kare a mataki na biyu sau uku a teburin Premier League, sai dai a bana tana kan teburi da tazarar maki shida tsakani da Manchester City ta biyu - kuma ita ce ta…
Read More
Abokan hamayyarmu sun fi mu kashe kuɗi wajen sayen ’yan wasa – Guardiola

Abokan hamayyarmu sun fi mu kashe kuɗi wajen sayen ’yan wasa – Guardiola

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya yi barkwanci yana mai cewa yana ɗan jin haushin ƙungiyarsa, saboda abokan hamayyarsu sun fi su kashe maƙudan kuɗi wajen cefane. Man City ce ta fi kashe kuɗi a kasuwar saye da sayar da ’yan ƙwallo da ta ci ta watse a watan Janairu, inda ta sayi Antoine Semenyo daga Bournemouth da Marc Guehi daga Crystal Palace kan kusan fam miliyan 84 gabaki ɗayansu. Sai dai Guardiola ya ce abokan hamayyarsa a gasar Premier League sun fi zuba jari mafi yawa. Idan har za a yi ƙididdigar cefane, Man City ta kashe sama da…
Read More
Ronaldo ya koma atisaye da Al Nassr bayan raɗe-raɗen saɓani da ƙungiyar

Ronaldo ya koma atisaye da Al Nassr bayan raɗe-raɗen saɓani da ƙungiyar

Fitaccen ɗan wasan ƙwallon ƙafa na Portugal, Cristiano Ronaldo, ya koma atisaye tare da ƙungiyar Al Nassr, lamarin da ya rage zazzafar jita-jitar da ta yaɗu cewa tauraron ya nuna rashin jin daɗi kan yadda ake tafiyar da jarin kulob ɗin idan aka kwatanta da sauran ƙungiyoyin da Asusun Zuba Jari na Saudiyya (PIF) ke marawa baya. Ronaldo, mai shekaru 40, ya kasance a tsakiyar muhawara a ’yan kwanakin nan bayan rahotanni sun ce yana tunanin barin Saudiyya sakamakon abin da ya ɗauka a matsayin banbanci wajen rabon tallafi tsakanin Al Nassr da manyan abokan hamayyarta kamar Al Hilal da…
Read More
Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na karo na 16

Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na karo na 16

Barcelona ta lashe Spanish Super Cup na biyu a jere na 16 jimilla, bayan doke Real Madrid 3-2 a wasan El Clasico na farko a bana da suka kara a Saudiyya ranar Lahadi. Kenan ƙungiyar Camp Nou ta lashe wasa na 10 a jere a dukkan fafata, rabon da a doke ta tun cikin watan Nuwamba da Chelsea ta samu nasara a Champions League. Wasan El Clasico na huɗu da a jere da Hansi Flick ya doke Real Madrid - biyu a Super Cup da kuma Copa del Rey - Haka kuma Barcelona ce kan gaba a teburin La Liga…
Read More
Michael Carrick ya karɓi ragamar riƙon ƙwarya a Manchester United

Michael Carrick ya karɓi ragamar riƙon ƙwarya a Manchester United

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United ta tabbatar da nadin tsohon ɗan wasanta, Michael Carrick, a matsayin koci na riƙon ƙwarya har zuwa ƙarshen kakar wasa ta bana. Fitaccen masani kan kasuwar ’yan wasa, Fabrizio Romano, ne ya fara bayyana labarin, inda ya ce an kammala yarjejeniyar baki tun ranar Litinin, sannan yanzu an cimma matsaya gaba daya, har da batun tawagar mataimakan da Carrick zai zo da su. A cewar rahotanni, tsohon ɗan wasan tsakiya na Man United zai zo da wasu amintattun mataimaka, ciki har da wani tsohon ɗan wasan gaba na ƙungiyar, domin taimaka masa wajen jagorantar…
Read More
An kama boka a Mali bayan yi wa ’yan ƙasar alƙawarin lashe AFCON

An kama boka a Mali bayan yi wa ’yan ƙasar alƙawarin lashe AFCON

Hukumomin tsaro a ƙasar Mali sun kama wani boka da ya kira kansa masani bayan ya yi alƙawarin zai taimaka wa ƙasar su lashe Gasar Kofin ƙasashen Afrika (AFCON) ta hanyar sihiri, inda ya karɓi fiye da yuro dubu talatin da uku daga jama’a. An kama mutumin ne bayan fitar Mali daga gasar. Rahotanni sun bayyana cewa mutumin, mai suna Sinayogo, an kama shi ne a Bamako ranar Asabar, kwana guda bayan Senegal ta doke Mali da ci 1-0 a wasan kwata fainal na AFCON 2025.  Kafin haka, Sinayogo ya riƙa bayyana kansa a matsayin marabout, wato boka na gargajiya,…
Read More
Chelsea ta naɗa Rosenior a matsayin sabon kocinta

Chelsea ta naɗa Rosenior a matsayin sabon kocinta

Kungiyar ƙwallon ƙafa ta Chelsea ta tabbatar da naɗa Liam Rosenior a matsayin sabon babban kocinta, inda ta ba shi kwantaragi na tsawon shekaru shida domin jagorantar sabon shiri da kulob ɗin ke fatan dawowa kan turbar nasara. Sanarwar ta zo ne a cikin wata takarda da kulob ɗin ta fitar, inda ta jaddada cewa hankalinsa zai ci gaba da karkata kan gina ’yan wasa da bunƙasa hazaƙa, tare da tabbatar da cewa burin Chelsea na lashe manyan kambu bai ragu ba. Chelsea ta bayyana cewa sabon tsarin da ta ɗauka na dogon lokaci yana da nufin samar da kwanciyar…
Read More
Me ya sa Man United ta kori Amorim?

Me ya sa Man United ta kori Amorim?

Kungiyar Manchester United ta sanar da raba gari da kocinta, Ruben Amorim, matakin da ya girgiza magoya ya tare da sake buɗe muhawara kan matsalolin da ke addabar ƙungiyar tun bayan fara kakar wasa. Duk da zuwansa da babban fata da kuma suna a matsayin ɗaya daga cikin matasan koci-kocin da suka fi tasiri a Turai, tafiyar Amorim a Old Trafford ta zo ƙarshe cikin gaggawa fiye da yadda aka zata. Rahotanni daga Ingila na nuni da cewa rashin daidaiton sakamako shi ne babban dalilin yanke wannan shawara. Manchester United ta kasa samun kwanciyar hankali a gasar Premier League, inda…
Read More
AFCON 2025: Nijeriya za ta kece raini da Algeria a wasan daf da ƙarshe

AFCON 2025: Nijeriya za ta kece raini da Algeria a wasan daf da ƙarshe

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta haɗu da takwararta ta ƙasar Algeria a wasan zagayen daf da ƙarshe na gasar ƙasashen nahiyar Afirika da ake ci gaba da bugawa a Moroko. Nijeriya ta kai zagayen Kwata Fainal bayan lallasa ƙasar Mozambiƙue a wasan zagayen yan 16 a ranar Litinin. Hakazalika, Algeria ta doke Dimokuraɗiyyar Congo a wasan zagayen 16 da ci 1-0 bayan karin mintuna 30 da alƙalin wasa yayi a wasan, ƙasashen biyu za su haɗu a ranar Asabar 10 ga watan Janairu domin sanin ƙasar da zata kai matakin Semi Fainal. Nijeriya ta samu nasara a dukkan…
Read More
Da Ɗumi-Ɗumi: Manchester United ta sallami kocinta Amorim

Da Ɗumi-Ɗumi: Manchester United ta sallami kocinta Amorim

Daga BELLO A. BABAJI a Abuja Rahotanni daga ƙasar Ingila sun tabbatar da cewa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester United ta kori mai horar da 'yan wasanta, Ruben Amorim bayan shafe watanni 14 a matsayin. TheAlthletic ta wallafa haka ta kafar X a safiyar yau Litinin, inda ta ƙara da cewa, mataimaki Darren Fletcher ne zai maye gurbinsa na wucin-gadi. Sanarwar ta bayyana cewa, tuni aka sanar da kocin mai shekaru 40 kuma ɗan ƙasar Portugal matakin a hukumance. Ana ganin hakan na da alaƙa da rashin nasara akai-akai da ƙungiyar ta ke yi musamman a gasar Premier League ta…
Read More