02
Feb
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Kwallon Kafar Nijeriya, ta bayyana cewa babu wata yarjejeniya da ke tsakaninta da kocin tawagar Nijeriya a gasar kofin Afirka ta AFCON da ke gudana a kasar Ivory Coast, Peseiro Wary bayan kammala gasar. Shugaban hukumar Ibrahim Musa Gusau ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwa. Ya kara da cewa, "abin farin ciki yanzu shi ne duk wasu basuka da yake bi, mun samu daga Gwamnatin Tarayya za a biya shi." Sai dai ya ce, za su iya daukar koci daga kowace irin kasa ta duniya ba lallai sai dan Nijeriya ba. "Abin da…