Wasanni

Hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta maye gurbin Yamal da Frutos

Hukumar ƙwallon ƙafar Sifaniya ta maye gurbin Yamal da Frutos

Hukumar ƙwallon ƙafar ƙasar Sifaniya ta maye gurbin Lamine Yamal da Jorge de Frutos. Hukumar ƙwallon ƙafa ta Sifaniya (RFEF) ce ta tabbatar da wannan labarin a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na ɗ ranar Talata. Kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Sifaniya, Luis de la Fuente ya ɗauki wani mataki na gaggawa na gayyatar Jorge de Frutos domin maye gurbin Lamine Yamal wanda bai je sansanin horarwar tawagar ba bisa dalilai na jinya. Lamine Yamal da ke taka leda a ƙungiyar Barceola ana masa kallon mahimmin ɗan wasa a tawagar ƙwallon ƙafar Sifaniyar. Sai dai kuma ya bar…
Read More
Guardiola ya ja ragamar wasanni 1,000 a Man City

Guardiola ya ja ragamar wasanni 1,000 a Man City

Kocin Manchester City, Pep Guardiala ya ja ragamar wasanni a 1,000 a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Manchester City. Ya cika na 1,000 ne a Man City ta doke Liverpool 3-0 a wasan mako na 11 a gasar Premier League da suka fafata a Etihad ranar Lahadin da ta gabata. Man City ta fara cin ƙwallo ta hannun Erling Haaland a minti na 29 daga baya Nico Gonzalez ya ci na biyu, sai kuma Jeremy Doku ya kara na uku. Karo na 14 da Haaland ya zura ƙwallo a raga daga karawa 11 a Premier League a kakar nan - karo…
Read More
Aiki tuƙuru ne sirrin dukkan nasara – Ronaldo ga matasa bayan ya zama ɗan wasa na farko da ya mallaki Dala biliyan

Aiki tuƙuru ne sirrin dukkan nasara – Ronaldo ga matasa bayan ya zama ɗan wasa na farko da ya mallaki Dala biliyan

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na duniya, Cristiano Ronaldo, ya aika da sako mai cike da ƙarfafa gwiwa ga matasa a faɗin duniya, kwanaki kaɗan bayan da ya zama ɗan wasan ƙwallon ƙafa na farko da ya kai matsayin mallakar dala biliyan. ɗan wasan mai shekaru 40, wanda ke bugawa ƙungiyar Al Nassr FC ta Saudiyya da kuma ƙasarsa Portugal, yanzu yana da dukiya da aka kiyasta ta kai dala biliyan 1.4. Wannan na zuwa ne bayan ya zura wata ƙwallo mai nisa a nasarar da ƙungiyarsa ta samu kan Al Fateh SC da ci 5–1 a gasar Saudi Pro…
Read More
Hakimi da Salah na kan gaba a ’yan takarar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na 2025

Hakimi da Salah na kan gaba a ’yan takarar gwarzon ɗan ƙwallon Afirka na 2025

Achraf Hakimi da Mohamed Salah suna kan gaba a jerin ’yan takara 10 dake fatan lashe ƙyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar Afirka na 2025. Hakimi mai tsaron bayan tawagar Morocco ya bayar da gudunmuwar da Paris St Germain ta lashe kofi uku a Faransa da Champions League a kakar da ta wuce, shi kuwa Salah ya ɗauki Premier League tare da Liverpool. ɗan wasan da ke taka leda a Everton, Iliman Ndiaye da na Tottenham, Pape Matar Sarr, waɗanda suka taka rawar da ƙasashensu suka samu damar samun tikitin shiga gasar kofin duniya da za a yi a 2026, suna…
Read More
Kano Pillars ta dakatar da mai horar da ’yan wasanta

Kano Pillars ta dakatar da mai horar da ’yan wasanta

Hukumar gudanarwar ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta sanar da dakatar da masu horas da ƙungiyar bisa jagorancin Ogenyi Evans da mataimakinsa Ahmed Yaro Yaro. Hakan na zuwa ne bayan ƙungiyar ta sha kashi a hannun Barau FC a karawar da suka yi ranar Lahadi a gasar Premier ta Nijeriya. Sanarwar da hukumar gudanarwar ƙungiyar ta fitar ta ce an dakatar da kocin da mataimakinsa ne "sanadiyyar rashin ƙowari a gasar Premier ta Nijeriya ta 20025/26 da ke gudana." Ya zuwa yanzu Pillars ta yi nasara a wasanni biyu ne kacal cikin wasa takwas da ta buga a wannan…
Read More
An buƙaci Beckham ya goyi bayan sayar da Man United

An buƙaci Beckham ya goyi bayan sayar da Man United

Rahotanni sun bayyana cewa an tuntuɓi David Beckham, domin ya goyi bayan sayar da Manchester United. A raɗe-raɗin da ake yi wasu attajirai masu zuba hannun jari daga Haɗaɗɗiyar Daulal Larabawa ne ke shirye-shiryen sayen hannun jarin da iyalan Glazer suka mallaka. Kamar yadda Star da Mirror ta wallafa, attajiran na son Beckham ya zama jakada a lokacin da za a yi cinikin. Tsohon ɗan wasan United, wanda yake da hannun jari Inter Miami da Salford, zai iya samun damar mallakar hannun jari a ƙungiyar Old Trafford. Beckham wanda ya daɗe yana caccakar iyalan Glazer kan yadda suke gunadar da…
Read More
Aubameyang ya yi barazanar doke Nijeriya a wasan neman gurbin Gasar Kofin Duniya

Aubameyang ya yi barazanar doke Nijeriya a wasan neman gurbin Gasar Kofin Duniya

Kyaftin ɗin Tawagar ƙwallon ƙafa ta Gabon, Pierre-Emerick Aubameyang, ya aika da saƙo ga tawagar Super Eagles ta Nijeriya, inda ya bayyana cewa ƙasarsu ta shirya tsaf don ganin ta samu gurbin shiga Gasar Kofin Duniya ta 2026. Aubameyang, wanda ya taka muhimmiyar rawa wajen kai Gabon matakin zagayen share fage, ya ce tawagarsu ta shiga sabon yanayi na ƙwazo don kafa tarihi ta hanyar samun nasarar zuwa gasar duniya a karon farko. Da yake magana da jaridar The Standard, tsohon ɗan wasan Arsenal da Barcelona ya bayyana yadda yake ji da ƙwazon gasar, inda ya ce, “Burina yanzu shi…
Read More
NFF ta dakatar da alƙalan wasan da su ka busa wasan Kano Pillars da Shooting Stars

NFF ta dakatar da alƙalan wasan da su ka busa wasan Kano Pillars da Shooting Stars

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Kwamitin alƙali wasa na hukumar ƙwallon ƙafa ta ƙasa NFF ta dakatar da alƙalan wasa guda uku da suka busa wasan Kano Pillars da Shooting Stars na gasar firimiya ta ƙasa, NPFL, wanda aka tashi 1-1 a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar Kano. An dakatar da su ɗin ne bisa gaza bin ƙa'idojin busa na ƙasa a wasan na mako na 8, lamarin da ya haifar da rikici bayan an tashi daga wasan. A sanarwar da sakataren kwamitin, Aminu Muhammad, ya sakawa hannu aka rabawa manema labarai , NFF ta dakatar da…
Read More
Joshua ya shirya komawa Nijeriya don fafatawa da Bakole a Rumble in the Jungle II

Joshua ya shirya komawa Nijeriya don fafatawa da Bakole a Rumble in the Jungle II

Fitaccen ɗan dambe ɗan asalin Nijeriya, Anthony Joshua, na iya komawa ƙasar mahaifansa domin yin gagarumin fafatawa da abokin hamayyarsa Martin Bakole a wani babban gasa da ake shirin kira “Rumble in the Jungle II”, wanda ake sa ran gudanarwa a birnin Legas cikin shekarar 2026. Rahotanni daga majiyoyi kusa da masu shirya gasar sun bayyana cewa an kammala tattaunawa tsakanin Joshua da hukumar wasanni ta Nijeriya (NSC), tare da tallafin wasu manyan kamfanonin sadarwa da bankuna da ke son ɗaukar nauyin taron. Idan wannan lamari ya tabbata, zai zama karo na farko da Joshua zai yi fafatawa a wasar…
Read More
Gasar Kofin Duniya: FIFA na fuskantar matsin lamba a duniya bayan barazanar Trump

Gasar Kofin Duniya: FIFA na fuskantar matsin lamba a duniya bayan barazanar Trump

Shugaban Amurka Donald Trump ya jefa FIFA cikin ruɗanin siyasa, yana mai gargaɗin cewa zai iya ɗauke wasannin gasar kofin duniya daga garuruwan da Amurka ke karɓar baƙuncin da yake ganin ba su da tsaro kafin shekarar 2026. Barazanar shugaban Amurka mai ci ya haifar da tambayoyi game da ’yancin cin gashin kai na FIFA, da kwanciyar hankali a gasar, da kuma ko ƙwallon ƙafa ta duniya za ta iya jure tsoma bakin siyasa daga ofishin da ke da ƙarfi a duniya. Gasar cin kofin duniya ta 2026 za ta kasance mai tarihi, gasar farko ta faɗaɗa zuwa ƙungiyoyi 48…
Read More