Wasanni

Mai tsaron raga da mataimakin kocin Algeria sun mutu a haɗarin mota

Mai tsaron raga da mataimakin kocin Algeria sun mutu a haɗarin mota

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wani haɗarin mota da ya faru a Algeria ya halaka nai tsaron raga da kocin ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Mouloudia Club El Bayadh lamarin da ya tilastawa hukumar ƙwallon ƙafar aasar ɗage dukkan wasannin da aka tsara bugawa. Kamfanin Dillancin Labarai na ƙasar ya ce, mai tsaron ragar ƙungiyar Zakaria Bouziani mai shekara 27 da mataimakin koci, Khalid Muftah sun mutu sanadin haɗarin. ’Yan wasan na hanyar zuwa Tizi Ouzou domin buga wasa da JS Kabylie ranar Juma'a lokacin da motar ɗauke da tawagar ’yan wasan ta yi haɗari kusa da birnin Tiaret da ke Arewa…
Read More
Osimhen da Oshoala: ’Yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwarazan ‘yan wasan Afirka a 2023

Osimhen da Oshoala: ’Yan Nijeriya da suka lashe kyautar gwarazan ‘yan wasan Afirka a 2023

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan tawagar Nijeriya, Victor Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan ƙwallon ƙafar Afirka na 2023, inda takwararsa, Asisat Oshoala a ɓangaren ƙwallon ƙafar mata ta zama gwarzuwar ’yar wasan ta Afirka. Ɗan wasan Super Eagles ya lashe kyautar a bikin da aka gudanar a Marrakech, wanda ya ja ragamar Napoli ta lashe Serie A karon farko bayan shekara 33. Osimhen ya yi takara tare da ɗan wasan Morocco Achraf Hakimi da na Masar Mohamed Salah. Ɗan wasan shi ne ya kai Super Eagles gasar kofin Afirka da za a yi a Ivory Coast a baɗi,…
Read More
2023 AFCON: Dole ne Super Eagles su saka tunanin cin nasara – Aghahowa

2023 AFCON: Dole ne Super Eagles su saka tunanin cin nasara – Aghahowa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon ɗan wasan Nijeriya, Julius Aghahowa ya buƙaci Super Eagles da su bunƙasa tunanin samun nasara a gasar kofin Afrika na 2023. A rukunin A da Cote d'Ivoire, Equatorial Guinea da Guinea-Bissau, zakarun na AFCON sau uku za su sake lashe gasar karo na huɗu. Super Eagles za ta buxe gasar ta ne a AFCON 2023 da Equatorial Guinea a filin wasa na Alhassan Quattara, Ebimpe ranar 14 ga watan Janairu. Sai dai a wata hira da Kamfanin Dillancin Labaran Nijeriya (NAN), Aghahowa ya bayyana cewa dole ne 'yan wasan su nuna jajircewa da juriya idan…
Read More
Babu wata matsala a Man United – Ten Hag

Babu wata matsala a Man United – Ten Hag

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Manchester United Erik ten Hag ya yi watsi da raɗe-raɗin cewa an samu rabuwar kai a Old Trafford, yana mai jaddada cea ƙungiyar na tafiya kan turbar da ta dace. Da ƙwallo biyun da Scott McTominay ya zura a ragar Chelsea a wasan da suka tashi 2-1 ranar Talata, shi ne karon farko da ƙungiyar ta Ten Hag ta ci wata ƙungiya da ke cikin goman farko a Firimiya da ake yi yanzu. Kocin ya ce da Manchester sun yi amfani da damar da suka samu a wasan da bai wahalar da su ba kamar…
Read More
Super Eagles ta faɗo mataki na 42 a teburin FIFA

Super Eagles ta faɗo mataki na 42 a teburin FIFA

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Super Eagles ta Nijeriya ta yi ƙasa zuwa mataki na 42 a jerin waɗanda ke kan gaba a ƙwallon aafa a duniya, kamar yadda FIFA ta sanar. A jadawalin da FIFA ta fitar ranar Alhamis, Nijeriya ta ɓarar da maki 16.04, wadda ta haxa 1474.44, wadda ta ke da maki 1490.48 a cikin Oktoba. Sai dai wannan koma bayan bai shafi matakin Super Eagles a nahiyar Afirka ba, har yanzu tana nan a matsayi na shida. Biye da Moroko da Senegal da Tunisia da Algeria da kuma Masar a jerin waɗanda ke kan gaba a taka…
Read More
Na’urar VAR na ɓarna fiye da gyara – Bincike

Na’urar VAR na ɓarna fiye da gyara – Bincike

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Masu ruwa da tsaki na cigaba da miƙa ƙorafe-ƙorafe game da kuskuren da na’urar taimakawa alƙalin wasa ta VAR ke c gaba da tafkawa a wasannin gasar Firimiyar Ingila, ta yadda na'urar ke sahale bugun fenariti a wajen da bai kamata ba, baya ga soke ƙwallayen da suka cancanta. Lamarin da ya faru a wasan da Fulham ta yi nasara kan Wolverhampton Wanderes da ƙwallaye 3 da 2 jiya Litinin ƙarƙashin gasar ta Firimiyar ya ja hankalin masharhanta bayan da alƙalin wasa Michael Salisbury ya amince da bugun fenariti ga Fulham a wajen da kowanne ɓangare…
Read More
Nijeriya na duba yiwuwar sallamar kocin Super Eagles

Nijeriya na duba yiwuwar sallamar kocin Super Eagles

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya ta fara laluben wanda zai maye gurbin mai horas da tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar, Super eagles, Jose Peseiro, yayin da ta ke duba yiwuwar sallamar sa. Kwamitin gudarwar hukumar, ya ce bai gamsu da yadda kocin ke jagorantar Super Eagles ba, inda ya yanke shawarar nemo mai horaswa daga cikin gida. Tun lokacin da Kocin ɗan ƙasar Portugal ya karvi jagorancin ƙungiyar a shekarar 2022, wasanni shida kacal ya samu nasara a kai, inda ya yi rashin nasara a wasanni 15. Shugaban kwamitin, Shariff Ahlan yayin wata ganawa da manema labarai, ya…
Read More
Euro 2024: Ƙungiyoyin da suka samu gurbin shiga gasar

Euro 2024: Ƙungiyoyin da suka samu gurbin shiga gasar

Daga MAHDI. MUHAMMAD Ƙungiyoyi 20 sun samu gurbin shiga gasar Euro 22024 kai tsaye, inda Jamus za ta karɓi baƙuncin wasannin a 2024. Ingila, wadda Gareth Southgate ke jan ragama tana cikin tawagogin da za su jira raba jadawali, bayan da ta ja ragamar rukuni na uku, itama Scotland ta samu gurbi. Dukkan wadda ta yi ta daya da ta biyu a kowanne rukuni, su ne suka samu tikiti kai tsaye a wasannin da za a fara daga Yuni zuwa Yulin 2024. Yanzu kenan saura gurbi uku ya rage, inda tawaga 12 za ta buga wasannin cike gurbin shiga Euro…
Read More
Liverpool tana shirin faɗaɗa Anfield kafin wasanta da Manchester United

Liverpool tana shirin faɗaɗa Anfield kafin wasanta da Manchester United

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Liverpool na shirin buɗe saman filin wasanta na Anfield lokacin da za ta fafata da Manchester united a ranar 17 ga watan Disamba. Wannan dai na cikin wani shiri na faɗaɗa filin da ta ke yi daga mai ɗaukar mutum 7,000 zuwa 61,000, wanda zai ci maau kallo miliyan 80. Ana cewa aikin zai samu tsaiko zuwa 2024, bayan ƙungiyar ta sauya kwataragi da kamfanin da za su yi aikin. Amma Liverpool ta ce shirin buɗe filin wasan gabanin wasanta da Manchester na ƙila-wa-ƙala, domin sai masana sun yi nazari kai, saboda kare rayuwar 'yan kallo.…
Read More
El-Ghazi ya maka Mainz a kotu kan sallamarsa daga ƙungiyar

El-Ghazi ya maka Mainz a kotu kan sallamarsa daga ƙungiyar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan ƙasar Holland Anwar El Ghazi na shirin ɗaukar matakin shari'a a kan tsohon ƙungiyarsa Mainz saboda korar da aka yi masa ba bisa ƙa'ida ba. Mainz ta soke kwantiragin El Ghazi a ranar 2 ga Nuwamba bayan wasu jerin rubuce-rubucen da ya yi a shafukan sada zumunta game da rikicin Isra'ila da Gaza. Mainz ta ce tawagar lauyoyin El Ghazi ne suka sanar da ita game da lamarin. A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ƙara da cewa ba za ta ƙara yin tsokaci ba domin shari'a ce da ke gudana a halin…
Read More