Wasanni

Ni da Chelsea mun zama abu ɗaya – Mourinho

Ni da Chelsea mun zama abu ɗaya – Mourinho

Tsohon kocin ƙungiyar Chelsea ta Ingila, Jose Mourinho wanda yanzu yake horar da ƙungiyar Benfica ya ce shi da ƙungiyar ta Stanford Bridge sun zama hanta da jini. Mourinho ya bayyana haka ne a ganawarsa da manema labarai kan shirye-shiryen da yake yi na jagorantar ƙungiyar Benfica ta ƙasar Portugal a wasan da za ta fafata da Chelsea na gasar zakarun turai a Ingila a ranar Talata. Sai dai ya ce a lokacin da ake tsaka da wasan, "zan jingine ƙaunar da yake yi wa Chelsea na minti 90 domin in fuskanci aikin da nake yi wa ƙungiyar Benfica." Ya…
Read More
Postecoglou ya nemi afuwar magoya bayan Forest

Postecoglou ya nemi afuwar magoya bayan Forest

Kocin Nottingham Forest, Ange Postecoglou ya buƙaci magoya baya su kara haƙuri, bayan da har yanzu bai ci wasa ba. Ranar Alhamis Forest za ta karɓi baƙuncin Midtjylland a Europa League a City Ground a karon farko tun bayan kusan shekara 30 rabon da ta shiga gasar zakarun Turai. Tsohon kocin Celtic da Tottenham ya maye gurbin Nuno Espirito Santo a watan Satumba, amma har yanzu bai ci wasa ba. Ya fara da shan kashi 3-0 a gidan Arsenal, sannan Swansea ta yi waje da su daga Carabao Cup da yin canjaras a Burnley da kuma a Real Betis a…
Read More
’Yan wasa biyar da suka fi yawan lashe kyautar Ballon d’Or a tarihin ƙwallon ƙafa

’Yan wasa biyar da suka fi yawan lashe kyautar Ballon d’Or a tarihin ƙwallon ƙafa

Kyautar Ballon d'Or, wacce Hukumar ƙwallon ƙafar Faransa ta kafa a 1956, ita ce kyauta mafi girma da ake ba ɗan wasan ƙwallon ƙafa, wacce ke nuna maƙurar ƙwarewar ɗan wasa. A tsawon tarihin ba da wannan kyauta, akwai fitattun 'yan wasa biyar da suka lashe ta sau uku ko fiye da haka, alamar da ke nuna ƙwarewarsu a tarihin fagen ƙwallon ƙafa. ’Yan wasan ƙwallon kafa biyar ne suka taɓa lashe kyautar Ballon d'Or sau uku zuwa fiye da hakan a tarihi. Jaridar Blueprint Manhaja ta yi nazari kan 'yan wasan da suka fi yawan kyautar Ballon d'Or, tun…
Read More
Tokyo 2025: Ajayi ya kafa wa Nijeriya sabon tarihi a gasar tseren gudu

Tokyo 2025: Ajayi ya kafa wa Nijeriya sabon tarihi a gasar tseren gudu

Ɗan wasan tsalle-tsalle da guje - guje, Kayinsola Ajayi ya kafa tarihin zama ɗan Nijeriya na farko da ya kai wasan ƙarshe a gasar ƙasashen Duniya da ke ci gaba da gudana a birnin Tokyo na ƙasar Japan, bayan shafe shekaru 18. Ajayi wanda ya yi tseren Gudun Mita 100, ya ƙarƙare a mataki na biyu a wasan dab da na kusa da na ƙarshe wato semi final, da ya kammala Gudun cikin daƙiƙa 9 da digo 93 a gasar ta 'Tokyo World Championship'. Nasarar ƙarewa a matakin na biyu, ya bashi damar zuwa wasan ƙarshe da ya sa ya…
Read More
Tsohon ɗan wasan Barcelona Abidal ya musanta jita-jitar mutuwarsa

Tsohon ɗan wasan Barcelona Abidal ya musanta jita-jitar mutuwarsa

Tsohon ɗan wasan bayan Barcelona Eric Abidal ya musanta jita-jitar mutuwarsa da ya karaɗe shafukan sada zumunta a wannan makon. Labaran da aka yi ta yaɗawa  a shafukan sada zumunta sun nuna cewa Eric Abidal ya mutu ne bayan matsalar taɓarɓarewar lafiya da ya fuskanta sakamakon dashen hanta da aka yi masa a shekarar 2025, lamarin da ya sa dole ya fito ya bayyana cewa yana da rai. A shekarar 2011 ce gwaji ya fara tabbatar da cewa Abidal mai shekaru 46 ya harbu da cutar dajin hanta. A cikin shekarar aka cire ƙarin daga hantarsa, kana aka masa dashe…
Read More
Flick ya caccaki Sifaniya kan nuna halin ko-in-kula da raunin Yamal

Flick ya caccaki Sifaniya kan nuna halin ko-in-kula da raunin Yamal

Kocin Barcelona, Hansi Flick ya ce ya kamata hukumar ƙwallon kafar Sifaniya ta ɗauki matakin kula mafi inganci, bayan da Lamine Yamal ya ji rauni lokacin da yake buga wa kasar tamaula. Mai shekara 18 ba zai buga wa Barcelona wasa da Valencia ranar Lahadi a gasar La Liga ba, watakila ba zai yi fafatawar da za ta fuskanci Newcastle United ba a makon gobe a Champions League. Haka shima Frenkie de Jong ya ji rauni a lokacin da yake buga wa Netherlands tamaula, kenan shima ba zai buga wasan Valencia ba. Sai dai Marc Bernal, mai shekara 18 zai…
Read More
Arsenal za ta taka rawar gani a gasar Zakarun Turai a bana – Valverde

Arsenal za ta taka rawar gani a gasar Zakarun Turai a bana – Valverde

Arsenal tana daga cikin ƙungiyoyin da za su iya lashe gasar Zakarun Turai a bana, inji kocin Athletic Bilbao, Ernesto Valverde. ƙungiyar da Mikel Arteta ke jan ragama za ta kara da Bilbao a filin wasa na San Mames a karawar farko a cikin rukuni a Champions League ranar Talata. Gunners ta kai zagayen daf da ƙarshe a bara, wadda Paris St Germain ta yi waje da ita daga gasar ta Zakarun Turai. Bilbao ta samu gurbin shiga Champions League a bana, bayan da ta kare a mataki na huɗu a teburin La Liga a kakar da ta wuce.
Read More
An zargi tsohon alƙalin wasa Coote da cin zarafin yaro

An zargi tsohon alƙalin wasa Coote da cin zarafin yaro

An tuhumi tsohon alkalin wasan Firimiya David Coote da fitar da hoton da ya zama cin zarafin yaro. Tsohon jami'in, mai shekaru 43 kuma daga Collingham, zai gurfana a gaban Kotun Majistare ta Nottingham ranar Alhamis. Laifin ya shafi rabawa ko adana hotuna ko bidiyo cin zarafin da ya shafi faifan bidiyo da jami’an ‘yan sandan Nottinghamshire suka kwaso a watan Fabrairu, inji rundunar. An gurfanar da Coote a ranar 12 ga watan Agusta kuma yana kan beli. Mahukutan kwamitin rafli sun kori Coote a watan Disamba, bayan wani faifan bidiyo na kalaman ɓatanci da ya yi kan tsohon kocin…
Read More
An fara sayar da tikitin kallon gasar kofin duniya

An fara sayar da tikitin kallon gasar kofin duniya

Daga ranar Laraba za a fara sayar da tikitin kallon gasar cin kofin duniya, ƙasa da shekara ɗaya da za a yi bikin buɗe wasannin a birnin Mexico. Ana sa ran kuɗin tikitin zai kama daga matsaikaicin kuɗi dalar Amurka 60 zuwa wasan ƙarshe dalar Amurka 6,730. Za a fara gasar cin kofin duniya daga 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin baɗi. Kimanin ’yan kallo miliyan 6.5 ake sa ran za su halarci gasar cin kofin duniya da tawaga 48 za ta kece raini a wasa 104 da za a buga tsakanin Mexico da Canada da kuma…
Read More
Forest ta naɗa Postecoglou a matsayin sabon kocinta

Forest ta naɗa Postecoglou a matsayin sabon kocinta

Nottingham Forest ta sanar da naɗa Ange Postecoglou a matakin sabon kocinta, bayan da ta kori Nuno Espirito Santo. Nuno ya bar City Ground a tsakar daren Litinin, bayan wata 21 yana jan ragama da yin wasa uku da fara kakar bana ta Premier League. Postecoglou ya koma aikin horar da tamaula a Premier League, bayan wata uku da Tottenham ta kore shi, sakamakon da ta kare a mataki na 17 a kasan teburin Premier League. Sai dai mai shekara 60 ya lashe Europa League a ƙarshen kakar da ta wuce, hakan ya kawo ƙarshen tsawon shekaru ba tare da…
Read More