Arsenal tana daga cikin ƙungiyoyin da za su iya lashe gasar Zakarun Turai a bana, inji kocin Athletic Bilbao, Ernesto Valverde.
ƙungiyar da Mikel Arteta ke jan ragama za ta kara da Bilbao a filin wasa na San Mames a karawar farko a cikin rukuni a Champions League ranar Talata.
Gunners ta kai zagayen daf da ƙarshe a bara, wadda Paris St Germain ta yi waje da ita daga gasar ta Zakarun Turai.
Bilbao ta samu gurbin shiga Champions League a bana, bayan da ta kare a mataki na huɗu a teburin La Liga a kakar da ta wuce.
