Wasanni

Nijeriya na duba yiwuwar sallamar kocin Super Eagles

Nijeriya na duba yiwuwar sallamar kocin Super Eagles

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya ta fara laluben wanda zai maye gurbin mai horas da tawagar ƙwallon ƙafar ƙasar, Super eagles, Jose Peseiro, yayin da ta ke duba yiwuwar sallamar sa. Kwamitin gudarwar hukumar, ya ce bai gamsu da yadda kocin ke jagorantar Super Eagles ba, inda ya yanke shawarar nemo mai horaswa daga cikin gida. Tun lokacin da Kocin ɗan ƙasar Portugal ya karvi jagorancin ƙungiyar a shekarar 2022, wasanni shida kacal ya samu nasara a kai, inda ya yi rashin nasara a wasanni 15. Shugaban kwamitin, Shariff Ahlan yayin wata ganawa da manema labarai, ya…
Read More
Euro 2024: Ƙungiyoyin da suka samu gurbin shiga gasar

Euro 2024: Ƙungiyoyin da suka samu gurbin shiga gasar

Daga MAHDI. MUHAMMAD Ƙungiyoyi 20 sun samu gurbin shiga gasar Euro 22024 kai tsaye, inda Jamus za ta karɓi baƙuncin wasannin a 2024. Ingila, wadda Gareth Southgate ke jan ragama tana cikin tawagogin da za su jira raba jadawali, bayan da ta ja ragamar rukuni na uku, itama Scotland ta samu gurbi. Dukkan wadda ta yi ta daya da ta biyu a kowanne rukuni, su ne suka samu tikiti kai tsaye a wasannin da za a fara daga Yuni zuwa Yulin 2024. Yanzu kenan saura gurbi uku ya rage, inda tawaga 12 za ta buga wasannin cike gurbin shiga Euro…
Read More
Liverpool tana shirin faɗaɗa Anfield kafin wasanta da Manchester United

Liverpool tana shirin faɗaɗa Anfield kafin wasanta da Manchester United

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Liverpool na shirin buɗe saman filin wasanta na Anfield lokacin da za ta fafata da Manchester united a ranar 17 ga watan Disamba. Wannan dai na cikin wani shiri na faɗaɗa filin da ta ke yi daga mai ɗaukar mutum 7,000 zuwa 61,000, wanda zai ci maau kallo miliyan 80. Ana cewa aikin zai samu tsaiko zuwa 2024, bayan ƙungiyar ta sauya kwataragi da kamfanin da za su yi aikin. Amma Liverpool ta ce shirin buɗe filin wasan gabanin wasanta da Manchester na ƙila-wa-ƙala, domin sai masana sun yi nazari kai, saboda kare rayuwar 'yan kallo.…
Read More
El-Ghazi ya maka Mainz a kotu kan sallamarsa daga ƙungiyar

El-Ghazi ya maka Mainz a kotu kan sallamarsa daga ƙungiyar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan ƙasar Holland Anwar El Ghazi na shirin ɗaukar matakin shari'a a kan tsohon ƙungiyarsa Mainz saboda korar da aka yi masa ba bisa ƙa'ida ba. Mainz ta soke kwantiragin El Ghazi a ranar 2 ga Nuwamba bayan wasu jerin rubuce-rubucen da ya yi a shafukan sada zumunta game da rikicin Isra'ila da Gaza. Mainz ta ce tawagar lauyoyin El Ghazi ne suka sanar da ita game da lamarin. A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ƙara da cewa ba za ta ƙara yin tsokaci ba domin shari'a ce da ke gudana a halin…
Read More
Haƙƙi na ne fitar da Arsenal kunya – Arteta

Haƙƙi na ne fitar da Arsenal kunya – Arteta

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Arsenal, Mikel Arteta ya bayyana cewa, dole ne ya fitar da ƙungiyar kunya a idon duniya bayan wasar da suka lallasa Sevilla da ci 2-0 a gasar Zakatun Turai. A kwanakin baya ma ya ce, ya zama wajibi ya kare kulob ɗin bayan ya caccaki alkalin wasa a karawar da Newcastle ta doke su da ci 1-0 a ranar Asabar ɗin da ta gabata. Ya ce, shawarar da aka yanke kan ƙwallon Anthony Gordon a St James' Park "abin kunya ne" kuma "abin takaici". Arsenal ta goyi bayan kalaman Arteta a wata sanarwa da ƙungiyar…
Read More
Pepe ya kafa sabon tarihi a gasar Zakarun Turai

Pepe ya kafa sabon tarihi a gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ɗan wasan baya na Portugal Pepe ya zama ɗan wasa mafi yawan shekaru da ya zura ƙwallo a raga a tarihin gasar zakarun Turai, inda ya ci qwallon da ta taimaka wa FC Porto ta doke Royal Antwerp. Pepe mai shekaru 40 da kwana 254 da haihuwa, ya zura ƙwallo ta biyu a ragar Antwerp a minti na 91, inda ya zama ɗan wasa na farko da ya haura 40 da ya zura ƙwallo a gasar. Francesco Totti ke riƙe da tarihin mai mafi yawan shekaru da ya zura ƙwalo a shekara 38 da kwanaki 59.…
Read More
An sako mahaifin ɗan wasan Liverpool, Luis Diaz

An sako mahaifin ɗan wasan Liverpool, Luis Diaz

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majiyoyin ’yan sanda da kafafen yaɗa labarai na ƙasar Colombia sun bayyana cewa ’yan bindigar da suka yi garkuwa da mahaifin ɗan ƙwallon Liverpool Luis Diaz na tsawon kwanaki 13 sun sako shi. Jami’an rundunar 'yan tawaye na ELN sun miƙa Luis Manuel Diaz ga Jami’an Majalisar Ɗinkin Duniya da jami’an cocin Katolika. An sace shi ne a ranar 28 ga Oktoba a garinsu, Barrancas. An kuma kama mahaifiyar ɗan wasan, amma an sako ta cikin 'yan sa'o'i. Kafofin yaɗa labaran cikin gida sun ce Mista Diaz na tafiya ne da helikwaftan soji zuwa birnin Valledupar,…
Read More
Zan daidaita komai a Man United – Erik ten Hag

Zan daidaita komai a Man United – Erik ten Hag

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kocin Manchester United Erik ten Hag ya ce, aungiyar na cikin wani irin yanayi amma har yanzu yana ganin shi ne mutumin da ya dace ya saita komai a Old Trafford. Nasarar da Newcastle ta samu da ci 3-0 a gasar kofin EFL ita ce babbar nasarar da suka samu a gidan Manchester United cikin shekaru 93. Wannan shi ne rashin nasara na takwas da United ta yi cikin wasanni 15 da ta buga, mafi muni a farkon kakar wasa tun 1962-63. Bayan da United ta sha kashi a hannun Manchester City a ranar Lahadi, shi…
Read More
Messi ya lashe kyautar Ballon d’Or karo na takwas

Messi ya lashe kyautar Ballon d’Or karo na takwas

Lionel Messi ya lashe kyutar gwarzon ɗan kwallon ƙafa na duniya na 2023, Ballon d'Or. Wannan shi ne karo na takwas da Messi ke lashe wannan kyauta ta bajinta a duniyar wasan tamaula. Messi tsohon ɗan wasan Barcelona da Paris St Germain mai taka leda a Inter Miami a Amurka ya ɗauki kofin duniya a Qatar a 2022. Shi ne ya ja ragamar Argentina ta lashe babban kofin duniya na farko a wajensa, sannan na uku a kasar jimilla.
Read More
Barcelona ta haɗa maki tara a wasa uku a gasar Zakarun Turai

Barcelona ta haɗa maki tara a wasa uku a gasar Zakarun Turai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD A wasan da Ferran Torres ya zura ƙwallo ya bayar da ɗaya aka zura a raga a bai wa Barcelona damar doke Shakhtar Donetsk da ci 2-1. Ƙungiyoyin sun buga wasa na uku-uku a cikin rukuni na takwas a Champions League. Torres ne ya fara cin ƙwallo a minti na 28 da take leda, bayan da ya Fermin Lopez ya buga ƙwallo ta gefen raga sai ta koma ta wajensa shi kuma ya zura a raga. Daga baya tsohon ɗan wasan Manchester City, ya bai wa Lopez ƙwallon da ya zura a raga a minti takwas…
Read More