Wasanni

Yadda Son da Muller suka fara nuna bajinta a Amurka

Yadda Son da Muller suka fara nuna bajinta a Amurka

Tsohon kyaftin ɗin ƙungiyar Tottenham ta Ingila, Son Heung-min da da tsohon kyatfin ɗin ƙungiyar Bayern Munich ta Jamus Thomas Muller sun fara taka leda da ƙafar dama a gasar Amurka ta Major League Soccer, inda suka fara da zura ƙwallo a wasannin da suka buga a ranar Asabar. Son ɗan asalin ƙasar Koriya ta Kudu mai shekara 33 ya jefa ƙwallo ne a bugun tazara a minti shida da shigarsa filin wasa domin fara taka leda a ƙungiyar Los Angeles FC a gasar MLS, inda aka tashi wasan 1-1 da ƙungiyar FC Dallas. ƙungiyar ta kafa tarihin cinikayya mai…
Read More
 Lookman ya koma atisaye da Atalanta bayan rushewar shirin komawa Inter Milan

 Lookman ya koma atisaye da Atalanta bayan rushewar shirin komawa Inter Milan

Dan wasan Nijeriya na tawagar Super Eagles Ademola Lookman ya koma atasaye tare da ƙungiyarsa Atalanta, bayan rushewar tattaunawa tsakanin ƙungiyar da Inter Milan kan sauyin sheƙar ɗan wasan. Kafin yi wa Atalanta kome dai, sai da Lookman ya yi ƙoƙarin tilasta wa ƙungiyarsa tasa amincewa ya koma Inter ta hanyar ƙauracewa zuwa atasaye, har ma da tattara wasu ’yan komatsansa ya kwashe daga ɗakin ajiyar kayayyakin ’yan wasa. Sai dai haƙar ɗan wasan na Nijeriya ba ta cimma ruwa ba, saboda a ranar Litinin da ta gabata tattaunawa takanin Atalanta da Inter Milan ta watse ba tare da an…
Read More
Rodri zai sake yin jinyar watanni – Guardiola

Rodri zai sake yin jinyar watanni – Guardiola

Kocin Manchester City, Pep Guardiola ya ce ɗan wasan tsakiyar ƙungiyar, Rodri ya sake jin rauni kuma da wuya ya murmure kafin hutun watan Satumba. ɗan ƙwallon na Sifaniya ya shafe mafi yawan kakar bara a gadon jinya saboda turguɗe gwiwa da ya yi a watan Satumban 2024. Mai riƙe da kambin Ballon d'Or na 2024, ya koma taka leda a matsayin canji a wasan ƙarshe na Man City na gasar Premier League da ta buga da Bournemouth. Sai kuma wasan da Al-Hilal ta fitar da su daga gasar Club World Cup a Amurka, inda aka yi canjinsa daga baya.…
Read More
 Ko Amorim zai iya kai Manchester United tudun-mun-tsira a kakar wasan bana?

 Ko Amorim zai iya kai Manchester United tudun-mun-tsira a kakar wasan bana?

Manchester United ta kwashe fiye da shekara 10 ba ta yi wani kataɓus ba, idan aka kwatanta da yadda ta saba a baya, musamman lokacin da Sir Alex Ferguson yake horas da 'yan wasan ƙungiyar. Tun bayan da Sir Alex ya yi ritaya a 2013 United ke neman kocin da ya dace da ita inda suka gwada irin su Jose Mourinho da Erik Ten Haag da David Moyes da Ralph Rangnick da sauran su, amma kowanensu ya gaza dawo da Manchester United kan ganiyarta duk da cewa wasu daga cikinsu sun lashe kofuna. A watan Nuwamban 2024 ne Manchester United…
Read More
Katsina United ta sayi sabbin ‘yan wasa domin tunkarar kakan wasan 2025-26

Katsina United ta sayi sabbin ‘yan wasa domin tunkarar kakan wasan 2025-26

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina A wata sanarwa ɗauke da sa hannun jami'in hulɗa da jama'a na ƙungiyar, malam Nasiru Gide ya ce sayen ƴan wasan zai ƙarawa ƙungiyar ƙarfin tunkarar kakan wasan da za a shiga. Nasiru Gide ya na mai tabbacin cewa da wannan sabbin ƴan wasa, Katsina United za ta taka rawar gani a gasar Firimiya ta ƙasa. Sabin yan wasan sun haɗa da Adekunle Oluwasegun daga kwara United sai Philip Clement Oguche daga Abia warriors da wasu cikinsu daga Bendel United. Sai ta ɗauki Moses daga Enugu Rangers da Falotu Azeez Al'amuran daga Alnasar Zlitan na…
Read More
Kano Pillars ta naɗa Evans Ogenyi a matsayin sabon mai horaswa

Kano Pillars ta naɗa Evans Ogenyi a matsayin sabon mai horaswa

Daga IBRAHIM HAMISU a Kano Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars FC ta sanar da naɗin Evans Ogenyi a matsayin sabon mai horarwa ko kuma kocin ƙungiyar, domin jagorantar shirin kakar gasar Firimiya ta Najeriya ta shekarar 2025/2026. Sanarwar hakan ta fito ne daga shafin sada zumunta na ƙungiyar da yammacin ranar Laraba, inda ta bayyana cewa Evans zai fara aiki nan take ba tare da wani ɓata lokaci ba. Wannan naɗi ya zama wani komo gida ga Evans Ogenyi wanda ya jagoranci Pillars zuwa samun ɗaukaka zuwa gasar Firimiya (NPFL) a shekara ta 2023, amma daga baya aka sallame…
Read More
Yamal na fuskantar tara kan bikin cikarsa shekaru 18

Yamal na fuskantar tara kan bikin cikarsa shekaru 18

Gwamnatin Sifaniya ta buƙaci a gudanar da bincike kan cin zarafi da baɗala da ya wuce ƙima da ake zargin an aikata yayin shagalin bikin zagayowar ranar haihuwar fitaccen jarumin ƙungiyar ƙwallon ƙafa na Barcelona, Lamie Yamal. Gwamnatin ta kuma ce za ta ci tarar ɗan wasan, bayan da ƙungiyar masu kare waada, ta yi zargin an ci zarafin mambobinta bayan da aka gayyaci wasu waadanni tare da wasu ’yan mata 12 masu halitta ta musamman domin nishaɗantar da baƙi a wajen taron bikin cikarsa shekaru 18 da haihuwa. ɗan wasan na ƙasar Sifaniya ya yi bikin cika shekaru 18…
Read More
Mun samu nasarar gudanar da gasar Club World Cup – Infantino

Mun samu nasarar gudanar da gasar Club World Cup – Infantino

Shugaban Hukumar ƙwallon ƙafa ta Duniya, Gianni Infantino ya ce sun yi nasarar gudanar da Fifa Club World Cup, kuma sun ɗauki darasa kan yadda za su shirya gasar kofin duniya a Amurka a 2026. Infantino ya ce FIFA, wadda ta tsara wasannin a Amurka tun daga watan jiya tsakanin ƙungiya 32 ta samu kuɗin da ya kusan kai yuro biliyan 1.5. Za a rufe labulen gasar ranar Lahadi da karawar ƙarshe tsakanin mai riƙe da Champions League, Paris St Germain da Chelsea mai buga Premier League. Ana kuma sa ran shugaban Amurka, Donald Trump zai halarcin karawar ƙarshe.
Read More
Tsohon ɗan wasan Man United, Tuanzebe ya maka ƙungiyar a kotu

Tsohon ɗan wasan Man United, Tuanzebe ya maka ƙungiyar a kotu

Tsohon ɗan wasan baya na Manchester United Axel Tuanzebe ya kai ƙarar ƙungiyar bisa zargin ba shi shawarar da ba ta dace ba a kan lafiyarsa. A makon da ya wuce ne ɗan wasan mai shekara 27, wanda ya koma Burnley daga Ipswich a bazaran nan, ya shigar da ƙara ne a kan United. ƙarar da danganci wani lokaci ne daga watan Yuli na shekara ta 2022, wanda ya danganci wani rauni da ba a sani ba - wanda kuma ake ganin zai iya cin har sama da fam miliyan 1. A shekararsa ta ƙarshe a United Tuanzebe, ya tafi…
Read More
Vazquez ya yi bankwana da Real Madrid

Vazquez ya yi bankwana da Real Madrid

Lucas Vazquez ya sanar da yin bankwana da Real Madrid, ba tare da bayyana makomarsa ba. ɗan wasan wanda ya fara yi wa Madrid wasa tun yana ɗan shekara 16 a 2007 ya sanar da matakin ne a shafinsa na Instagram. Tun a ranar 13 ga Yuli ne kwangilar shi ta kawo ƙarshe a Madrid. "A yau bayan buga wasa 400, lokaci ne da zan yi bankwana da ƙungiyar rayuwata. Zan bar Real Madrid amma ba zan taɓa mantawa da Real Madrid ba, inji ɗan wasan mai shekara 34. Vazquez ya ci awallo 38 a bara, tare taimakawa a ci…
Read More