Haƙƙi na ne fitar da Arsenal kunya – Arteta

Spread the love

Daga MAHDI M. MUHAMMAD

Kocin Arsenal, Mikel Arteta ya bayyana cewa, dole ne ya fitar da ƙungiyar kunya a idon duniya bayan wasar da suka lallasa Sevilla da ci 2-0 a gasar Zakatun Turai.

A kwanakin baya ma ya ce, ya zama wajibi ya kare kulob ɗin bayan ya caccaki alkalin wasa a karawar da Newcastle ta doke su da ci 1-0 a ranar Asabar ɗin da ta gabata.

Ya ce, shawarar da aka yanke kan ƙwallon Anthony Gordon a St James’ Park “abin kunya ne” kuma “abin takaici”.

Arsenal ta goyi bayan kalaman Arteta a wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, wadda tsohon ɗan wasan Manchester United Gary Neville ya kira abu “mai haɗari”.

“Ya zama wajibi gare ni in tsaya a gabanku in bayyana gaskiya ,” inji Arteta a ranar Talata.

“Aikina shi ne kare ‘yan wasana da kuma kulob ɗina ta hanya mafi kyau, abin da nake da niyyar yi ke nan a kowanne lokaci.”

Rashin nasara a Newcastle ya kawo ƙarshen wasan da Arsenal ta yi a gasar Firimiya ba tare da an doke ta ba, abin da ya sa ta zama ta huɗu, inda akwai maki uku tsakaninta da Manchester City da ke jan ragamar teburin.

By Editor