Daga MAHDI M. MUHAMMAD
Ɗan wasan ƙasar Holland Anwar El Ghazi na shirin ɗaukar matakin shari’a a kan tsohon ƙungiyarsa Mainz saboda korar da aka yi masa ba bisa ƙa’ida ba.
Mainz ta soke kwantiragin El Ghazi a ranar 2 ga Nuwamba bayan wasu jerin rubuce-rubucen da ya yi a shafukan sada zumunta game da rikicin Isra’ila da Gaza.
Mainz ta ce tawagar lauyoyin El Ghazi ne suka sanar da ita game da lamarin.
A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta ƙara da cewa ba za ta ƙara yin tsokaci ba domin shari’a ce da ke gudana a halin yanzu.