Wasanni

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya bai wa ’yan wasan Super Eagles tukwicin filaye da gidaje bayan dawowa daga Gasar AFCON 2023

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu ya bai wa ’yan wasan Super Eagles tukwicin filaye da gidaje bayan dawowa daga Gasar AFCON 2023

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Bola Tinubu, ya karrama ‘yan wasan Super Eagles da lambar yabo ta MON hadi da tukwicin fili da gida a birnin tarayya Abuja. Tinubu ya yi wa ‘yan wasan goma ta arzikin ne a ranar Talata a lokacin da ya karbi bakuncinsu tare da jami’an Hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya (NFF) a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja. Tawagar ta ziyarci Tinubu ne bisa jagorancin Ministan Bunkasa  Wasannin Motsa Jiki, Saenata John Owan Enoh. Wata sanarwar da ya fitar, Kakakin Shugaban Kasa, Ajuri Ngelale, ya ce Shugaba Tinubu ya yaba wa tawagar Super Eagles bisa…
Read More
Nijeriya ta gaza lashe Kofin AFCON 2023

Nijeriya ta gaza lashe Kofin AFCON 2023

Daga BASHIR ISAH A ranar Lahadi aka kammala Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) na 2023 inda aka ɓarje gumi tsakanin Nijeriya da Ivory Coast a wasan ƙarshe. A ƙarshe, Ivory Coast ce ta zo ta ɗaya a gasar bayan da ta doke Najeriya da ci 2 da 1 a wasan ƙarshe na gasar. Mai masaukin bakin ta zama zakara ne, bayan ta warware ƙwallon da Nijeriya ta jefa mata kafin tafiya hutun rabin lokaci. AFCON: Tinubu ya janye aniyyarsa ta zuwa kallon wasan Nijeriya na ƙarshe, ya wakilta Shettima a madadinsa Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen…
Read More
AFCON: Tinubu ya janye aniyyarsa ta zuwa kallon wasan Nijeriya na ƙarshe, ya wakilta Shettima a madadinsa

AFCON: Tinubu ya janye aniyyarsa ta zuwa kallon wasan Nijeriya na ƙarshe, ya wakilta Shettima a madadinsa

Daga BASHIR ISAH Shugaban Kasa Bola Tinubu ya janye niyyarsa ta zuwa kallon wasan karshe da Nijeriya za ta kara da Côte d’Ivoire a gasar AFCON 2023 da ke gudana a kasar Côte d’Ivoire.  Maimakon haka, Tinubu ya wakilta Mataimakin Shugaban Kasa,  Kashim Shettima kan ya jagoranci tawagar Shugaban Kasa zuwa wajen kallon wasan wanda za a buga a ranar Lahadi. Hadimin Shugaban Kasa kan sha’anin yada labarai da sadarwa, Stanley Nkwocha, shi ne ya  bayyana haka  a ranar Asabar. MANHAJA ta rawaito da fari cewar, Tinubu zai halarci kallon wasan na karshe da Nijeriya za ta buga da Côte…
Read More
AFCON: A ranar Lahadi Nijeriya za ta haɗu da Ivory Coast a wasan ƙarshe

AFCON: A ranar Lahadi Nijeriya za ta haɗu da Ivory Coast a wasan ƙarshe

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tawagar Ƙwallon Ƙafar Nijeriya ta Super Eagles za ta haɗu da mai masaukin baƙi Ivory Coast a wasan ƙarshe na kofin nahiyar Afrika bayan nasararorin da ƙasashen biyu suka samu a wasanninsu na daren Laraba, wasan ƙarshen da zai gudana a ranar Lahadi 11 ga watan Fabarairu. Nijeriya dai ta doke Afrika ta kudu ne da ƙwallaye 4 da 2 a bugun fenariti yayin wasan daf da ƙarshe ƙarƙashin gasar ta AFCON, nasarar da ta kawo ta wannan mataki na wasan ƙarshe wanda rabonta da kai wa tun a shekarar 2013 wanda kuma ta lashe kofin…
Read More
AFCON 2023: Tinubu zai halarci kallon wasan ƙarshe da Nijeriya za ta buga

AFCON 2023: Tinubu zai halarci kallon wasan ƙarshe da Nijeriya za ta buga

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai halarci kallon wasan ƙarshe da Nijeriya za ta buga a Gasar Cin Kofin Nahiyar Afirka (AFCON) 2023 da ke gudana a Côte d’Ivoire. Ya zuwa ranar Lahadi ake sa ran Nijeriya da Côte d’Ivoire za su fafata a wasan ƙarshe na gasar wanda za a buga a Abidjan. Shugaban hukumar ƙwallon ƙafa ta CAF, Patrice Motsepe, shi ne ya bayyana haka yayin taron manema labarai da ya shirya ranar Juma'a a Abidjan. Za a buga wasan ƙarshen ne a filin wasannin motsa jiki na Alassanne Ouattara, Ebimpe, Abidjan. Tuni dai 'yan…
Read More
Kamaru ta ƙi amincewa da murabus ɗin Eto’o

Kamaru ta ƙi amincewa da murabus ɗin Eto’o

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Ƙwallon Ƙafar Ƙasar Kamaru, ta ƙi amincewa da buƙatar ajiye aiki da tsohon ɗan wasan gaba na ƙasar, Samuel Eto’o, ya gabatar mata. A ranar Litinin ne, Eto’o ya miƙa takardar ajiye muƙamin shugabancin hukumar, yayin wani taron ganawa da aka gudanar a birnin Yaounde. Tsohon ɗan wasan na Kamaru ya ce matakin nasa ya biyo bayan gazawar ’yan wasan ƙasar na ƙasa taɓukawa a gasar kofin nahiyar Afirka ta AFCON da ke gudana a ƙasar Ivory Coast. Sai dai mambobin hukumar sun ce suna da qƙwarin gwiwa a kansa na ci gaba da aiwatar…
Read More
Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen karshe a garsa AFCON 2023

Shettima ya taya Super Eagles murnar shiga zagayen karshe a garsa AFCON 2023

Daga BASHIR ISAH Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima ya taya ’yan wasan Super Eagles murnar samun nasarar kaiwa zagayen karsahe a gasar AFCON 2023 da ke gudana a Ivory Coast. ‘Yan wasan Super Eagles na Nijeriya sun taki wannan nasarar ce bayan da suka yi galaba a kan ‘yan wasan Bafana Bafana na Afirka ta Kudu a wasan da suka buga ranar Laraba a filin Stade de la Paix da ke Bouake. An kare wasan ne da 1-1 bayan shafe mintoci sama da 100, wanda a karshe wasan ya kammala da bugun fenariti. Yanzu dai tun da ta samu tsallake…
Read More
AFCON 2023: Tsohon ɗan majalisar Nijeriya ya mutu a wajen kallon wasan Super Eagles da Afirka ta Kudu

AFCON 2023: Tsohon ɗan majalisar Nijeriya ya mutu a wajen kallon wasan Super Eagles da Afirka ta Kudu

Daga BASHIR ISAH Bayanai da MANHAJA ta samu na nuni da cewa wani tsohon dan majalisar wakilai daga Jihar Delta ya mutu a wajen kallon wasan kwallon da aka buga tsakanin Super Eagles da Afrika ta Kudu na gasar AFCON 2023 a ranar Laraba. Wata majiya ta kusa da ahalin marigayin ta ce, Ojuogboh ya yanke jiki ya fadi ne a lokacin da aka bai wa Afirka ta Kudu damar buga fenariti a kurarren lokaci a yayin wasan da aka buga a filin Stade de la Paix da ke Bouake. A halin rayuwarwa, marigayi Cairo Ojuogboh tsohon dan Majalisar Wakilai…
Read More
AFCON 2023: Osimhen na fuskantar matsin lamba wajen zura ƙwallaye – Udeze

AFCON 2023: Osimhen na fuskantar matsin lamba wajen zura ƙwallaye – Udeze

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon dan wasan Nijeriya Ifeanyi Udeze ya ce dan wasan Super Eagles Victor Osimhen yana fuskantar matsin lamba wajen zira kwallaye a gasar AFCON 2023. An yi hasashen Osimhen ya shiga gasar ta bana a matsayin daya daga cikin ’yan wasan da za su fafata domin samun kyautar dan wasan da ya fi yawan zura kwallaye. Sai dai Osimhen ya samu nasarar zura awallo daya ne kawai kuma ya rasa damar cin kwallo da dama. Da yake waiwayar rawar da Osimhen ya taka bayan wasanni uku na rukuni, Udeze ya yi imanin cewa rashin samun karin…
Read More