Labarai

Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Runduna ta ƙaryata labarin kashe sosjoji 20

Daga FATUHU MUSTAPHA Rundunar Sojojin Nijeriya ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta buga mai nuni da 'yan Boko Haram da mayaƙan ISWAP sun kashe sojoji 20 a yankin Arewa maso-gabas. A sanarwar da rundunar ta fitar a Alhamis, Daraktan Sashen Hulɗa da Jama'a na rundunar, Brig.-Gen Mohammad Yerima, ya ce wannan labari ba shi da tushe balle makama. Ya ce an yaɗa labarin ne da manufar sanyaya wa al'umma guiwa game da sha'anin yaƙi da matsalolin tsaro da sojojin ke yi da ma su kansu sojojin da ke yaƙin. A cewarsa harin baya-bayan nan da aka kai wa…
Read More
Jami’ar Bauchi ta yi sabon suna

Jami’ar Bauchi ta yi sabon suna

Daga AISHA ASAS Majalisar Zartarwa ta Gwamnatin Jihar Bauchi ta aminta da batun sauya wa Jami'ar Bauchi, Gadau, suna zuwa Jami'ar Sa'adu Zungur. Sanarwar da Kwamishinan Ilimin Jihar Bauchi, Dr. Aliyu U. Tilde ya fitar, ta nuna an ɗauki matakin sauya wa jami'ar suna ne domin raya sunan marigayi Sa'adu Zungur (1915-1958) a matsayinsa na ɗaya daga cikin mazan jiya da suka bada gudunmawarsu wajen samun 'yancin kan ƙasa. A halin rayuwarsa, Malam Sa'adu Zungur ya riƙe muƙamin sakataren NCNC, ɗan gwagwarmayar sisaya ne wanda basirarsa ta yi tasiri wajen daidaita harkar siyasar Arewa, har wa yau mutum ne wanda…
Read More
BUA ya saya wa Nijeriya rigakafin korona guda milyan ɗaya… da magana – inji CACOVID

BUA ya saya wa Nijeriya rigakafin korona guda milyan ɗaya… da magana – inji CACOVID

Daga FATUHU MUSTAPHA Fitaccen kamfanin nan BUA Group, ya saya wa Nijeriya maganin rigakafin cutar korona guda milyan ɗaya a matsayin gudunmawarsa ga ƙasa wajen yaƙi da annobar korona. Bayanai sun nuna BUA ya sayi maganin ne tare da haɗin guiwar haɗakar masu taimaka wa Gwamnatin Nijeriya da saurarnsu wajen yaƙi da koro da aka fi sani da CACOVID a taƙaice. Ana sa ran magani ya iso Nijeriya a mako mai zuwa wanda idan hakan ya tabbata, a iya cewa shi ne ya zama rigakafi na farko da Nijeriya ta samu tun bayan ɓullar annobar korona. Kamfanin BUA ya ce…
Read More
A shirye muke mu samar wa makiyaya wuraren kiwo –   Gwamnonin Arewa

A shirye muke mu samar wa makiyaya wuraren kiwo – Gwamnonin Arewa

Daga AISHA ASAS Gwamnonin Arewa sun yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta tallafa musu da kuɗaɗen da za su yi amfani da su wajen samar da gandun dazazzuka a sassan yankinsu don amfanin makiyaya. Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Arewa kuma gwamnan jihar Filato Simon Lalong shi ne ya yi wannan kira yayin wani shirin talabijin da aka yi da shi a Talatar da ta gabata. Yana mai cewa, da dadewa gwamnonin Arewa sun yi na'am da shirin samar da gandun dazuzzukan. Ya ce duba da yadda harkokin sace sacen mutane ke ta ƙaruwa da kuma batun umarnin ficewa da aka…
Read More
Hukuma ta yi ɗamarar farfaɗo da birnin Abuja

Hukuma ta yi ɗamarar farfaɗo da birnin Abuja

Daga FATUHU MUSTAPHA Duba da yadda ayyukan ɓata-gari irin sace-sace da lalata kadarorin gwamnati da na ɗaiɗaikun mutane ke ta ƙaruwa a ƙwaryar birnin Abuja, hakan ya sanya Hukumar Abuja ƙarƙashin jagorancin Ministan Abuja, Malam Muhammad Musa Bello ta kafa kwamiti na musamman da zai tattara bayanan adadin ɓarnar da aka tafka. Sakataren Hukumar Abuja, Engr. Umar Gambo Jibrin, shi ne ya jagoranci ƙaddamar da kwamitin a ranar Litinin. Babban aikin da aka ɗora wa kwamitin shi ne, ya zagaya birnin Abuja kaf tare da tattara bayanan da suka danganci lalata kadarori da sace-sacen kayayyaki da suka faru a birnin…
Read More
Babu abin da zai cika sai da mace a ciki – Hajiya Halima

Babu abin da zai cika sai da mace a ciki – Hajiya Halima

Hajiya Halima Idris ita ce Mai Taimaka wa Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir Ahmed El-Rufa’i, a fannin Fikira da Ƙirƙira. Ta yi fice ta fuskoki da dama tun gabanin muƙamin ta, musamman wajen kishin Arewa da son cigaban mata da matasa. A wannan hirar da wakiliyar manhaja, AISAH ASAS, ta  yi da Halima Idris, ta bayyana abubuwa da dama da suka haɗa da ayyukan ta  a gwamnati da kuma fannin kwalliya. Ga yadda hirar ta kasance: Kin yi fice a harkokin cigaban matasa da suka shafi fikira da ƙirƙira. Me ya ba ki wannan sha’awar?Gaskiya ba zan iya ce miki…
Read More
‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da mutum 4 a Tungan Maje

Daga AISHA ASAS Wasu 'yan bindiga sun kai hari a Tungan Maje da ke yankin Gwagwalada, Abuja, inda suka yi garkuwa da wasu mutum huɗu. Al'amarin wanda ya auku a tsakar daren wannan Lahadin, sai da 'yan bindigar suka shafe kimanin sa'o'i uku suna abin da suka ga dama a Tungan Maje kafin daga bisani suka yi awon gaba da wani tsohon jami'in Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS) Abdulahi Idris Rakieu da wasu mutum biyu daga iyalan gidansa. A cewar jaridar TheCable, harin ya shafi wani mai suna Olusola Agun, wanda shi ya zama cikon na…
Read More
NUJ ta yi gargaɗin a sako mata ɗanta da aka sace

NUJ ta yi gargaɗin a sako mata ɗanta da aka sace

Daga AISHA ASAS Ƙungiyar 'Yan Jarida ta Ƙasa (NUJ) reshen Birnin Tarayya, Abuja, ta yi kira da a gaggauta sako mata ɗanta Okechukwu Nnodim ma'aikaci a Jaridar Punch. Bayanan da suka fito daga ƙungiyar sun yi zargin cewa har gida wasu 'yan bindiga suka bi Nnodim suka yi gaba da shi, bayan da suka yi harbe-harbe a iska da bindigoginsu. Takardar da ƙungiyar ta fitar wadda shugabanta Comrade Emmanuel Ogbeche da sakatarenta Ochiaka Ugwu suka sanya wa hannu, ta nuna yadda ƙungiyar ta yi tir da wannan ɗanyen aiki, tare da neman a sako Nnodim ba tare da wani sharaɗi…
Read More
Cutar Korona: An samu ƙarin mutum 1,340 da suka harbu a faɗin ƙasa

Cutar Korona: An samu ƙarin mutum 1,340 da suka harbu a faɗin ƙasa

Daga FATUHU MUSTAPHA A halin da ake ciki, birnin tarayya, Abuja da jihar Legas da River da kuma Oyo, su ne jihohin da ke kan gaba wajen samun mafi yawan waɗanda suka harbu da cutar korona a tsakanin sa'o'i 24 da suka gabata. Bayanan Cibiyar Daƙile Yaɗuwar Cututtuka ta Ƙasa (NCDC), sun nuna an samu ƙarin mutum 1,340 da suka kamu da cutar korona. Ƙarin da cibiyar ta ce ya shafi wasu jihohin ƙasar nan su 22, ciki har da Abuja 320, Lagos 275, Rivers 117, da kuma Oyo 100. Sauran sun haɗa da Sakkwato 3, Kaduna 31, Katsina 14,…
Read More
Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Yajin aiki: Muna nan kan bakanmu – SSANU/NASU

Daga AISHA ASAS Haɗaɗɗen Kwamitin Ƙungiyar Ma'aikatan Jami'o'i (NASU) da kuma Ƙungiyar Manyan Ma'aikatan Jami'o'i (SSANU), ya tsayar da ranar Juma'a (05/02/2021) a matsayin ranar da mambobin ƙungiyoyin biyu za su soma yajin aiki na sai baba-ta-gani sakamakon gazawar da suka ce gwamnati ta yi wajen biya musu buƙatunsu. Tun farko, sai da ƙungiyoyin suka bai wa gwamnati wa'adin makonni kan ta magance musu matsalolinsu ko kuma su tsunduma yajin aiki. Shugaban SSANU Muhammed Haruna, ya shaida wa Manhaja cewa, babu wata yarjejeniya da ƙungiyoyin suka cim ma da gwamnati kan janye ƙudirin shiga yajin aikin. Yana mai cewa, tattaunawar…
Read More