Kasuwanci

Sama da miliyan 100 za a raba wa ‘yan kasuwar Masaka da gobara ta shafa

Sama da miliyan 100 za a raba wa ‘yan kasuwar Masaka da gobara ta shafa

Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Kwamitin da shugaban ƙaramar hukumar Karu a jihar Nasarawa barista Abubakar Aliyu Madaki ya kafa domin tantance lalacewa da kuma asarar dukiyoyi da aka yi sakamakon wata mummunar gobarar wuta da ta auku a kasuwar Masaka ta garin Karu din a bara ya gabatar da rahoton sa. Kwamitin wadda ke ƙarƙashin jagorancin shugabanta wato Cif Mark Auta a yayin zaman ya kuma ba da wasu shawarwari na musamman dangane da yadda za a aiwatar da matakan hana wuta a kasuwannin domin hana irin wannan abin gaggawa sake faruwa nan gaba da tabbatar da tsaro…
Read More
Yadda ‘yan kasuwar Mile-12 a Legas suka gudanar da addu’o’in nema wa Nijeriya zaman lafiya 

Yadda ‘yan kasuwar Mile-12 a Legas suka gudanar da addu’o’in nema wa Nijeriya zaman lafiya 

Daga DAUDA USMAN a Legas A Legas, an gudanar da taron addu’o’i na musamman a kasuwar Mile 12 International Market ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban kasuwar, Alhaji Isa Muhammad Mai Shinkafa, tare da babban sakataren kasuwar, Alhaji Balarabe Idris. Taron ya mayar da hankali ne kan neman zaman lafiya da bunƙasar Nijeriya. Taron, wanda ya samu halartar manyan malamai magada Annabaw daga sassa daban-daban na Legas, ya gudana cikin natsuwa da tsari. A farkon taron an raba malaman gida uku, inda kashi na farko suka karanta ayoyi masu tsarki na Al-Kur’ani, kashi na biyu suka gudanar da addu’o’i na musamman, yayin…
Read More
Bajekolin abinci da al’adu na matan Arewa zai bunƙasa tattalin arziki – Magajiyar Zangon Daura

Bajekolin abinci da al’adu na matan Arewa zai bunƙasa tattalin arziki – Magajiyar Zangon Daura

Daga MUHAMMADU MUJJITABA a Kano  An bayyana cewa shirya taron baje kolin abincin gargajiya da na zamani, tare da nune-nunen al’adun jihohin Arewa 19, ƙarƙashin jagorancin Hajiya Shahuda Muhammad — Shugabar ƙungiyar ta ƙasa — da Dakta Zubaida Ahmad Nagi — Shugabar ƙungiyar ta Jihar Kano — zai kawo sauyi mai fa’ida a tsakanin matan Arewa da na Nijeriya baki ɗaya. Magajiyar Zangon Daura, Hajiya Jamila Buhari Sani, ta bayyana hakan a taron da ya gudana a Kano a makon da ya gabata. Ta yaba wa dukkan mahalarta taron kan fasahar da suka nuna wajen kawo abinci iri-iri na zamani…
Read More
NNPC ya samu ribar Naira Tiriliyan 5.4 a 2024

NNPC ya samu ribar Naira Tiriliyan 5.4 a 2024

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Kamfanin Man Fetur na Nijeriya (NNPC) ya bayyana cewa, ya kammala shekarar 2024 da ribar ta kai tsabar kuɗi har Naira Tiriliyan 5.4, a wani babban ci gaban da ya nuna yadda sauye-sauyen da ake yi a kamfanin ke ƙara tasiri. Shugaban Kamfanin, Injiniya Bashir Bayo Ojulari, ya sanar da hakan a tattaunawarsa da manema labarai a Abuja, inda ya bayyana cewa kamfanin ya samu kuɗaɗen shiga na naira tiriliyan 45.1, wanda ya nuna hauhawar kaso 88 cikin ɗari idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata. A cewarsa, kuɗin rabo ga masu hannun jarin kamfanin…
Read More
Zan ba da gudunmawa mai tsoka wajen bunƙasa NURTW a Legas – Kwamaret Ahmed Isah

Zan ba da gudunmawa mai tsoka wajen bunƙasa NURTW a Legas – Kwamaret Ahmed Isah

Daga DAUDA USMAN a Legas Sabon Shugaban ƙungiyar Direbobin J5 ta ƙasa, ƙarƙashin NURTW reshan Jihar Legas da ke shiyar unguwar mile12 a Legas, Kwamaret Umar Ahmed Isah ya yi alƙawarin cewa zai bayar da ɗimbim gudunmawa wajan kawo cigaban ƙungiyar a jihar da kewayenta gabaɗaya. Kwamaret Umar Ahmed Isah ya yi wannan tsokacin ne a ofishin ƙungiyar da ke kasuwar mile12 a lokacin da suke karɓar baƙuncin waɗansu daga cikin 'yan ƙungiyar ta J5 na unguwanni daban-daban a cikin garin Legas da suka zo taya shi murna tare da fatan alheri dangane da samun wannan matsayi. Sabon shugaban ƙungiyar…
Read More
Muna zaune lafiya da sauran ƙabilu mazauna Jihar Legas – Sarkin Hausawan Imota

Muna zaune lafiya da sauran ƙabilu mazauna Jihar Legas – Sarkin Hausawan Imota

Daga DAUDA USMAN a Legas Sarkin Hausawan karamar hukumar Imota da ke yankin Ikorodu a jihar Legas, Alhaji Ibrahim Haruna, ya bayyana cewa al’ummar Hausawa mazauna yankin Imota da sauran ƙabilun Arewacin Nijeriya suna zaune lafiya da sauran kabilu mazauna Legas da kewaye. Alhaji Ibrahim Haruna, wanda asalinsa daga karamar hukumar Bagwai ta jihar Kano ne, ya bayyana haka ne a hirarsa da Jaridar Blueprint Manhaja a Legas, inda ya ce tun shekaru da dama da suka gabata ake samun zaman lafiya da jituwa tsakaninsu da sauran al’ummomin jihar. Ya ce tun bayan rikicin da aka taba samu tsakanin Hausawa…
Read More
 Yadda nake gudanar da sana’ar da mata ke yi a Legas — Babangida Musawa

 Yadda nake gudanar da sana’ar da mata ke yi a Legas — Babangida Musawa

Daga DAUDA USMAN a Legas Shugaban ƙungiyar masu sana’ar sayar da dafaffen abinci a Legas, wato masu tuwo, shinkafa da sauran dangoginsu, Alhaji Babangida Mati Musawa, wanda ke gudanar da sana’arsa a kasuwar Mile 12 International Market a Legas, ya shawarci mata Hausawa da sauran ‘yan ƙungiyarsa su ƙara himma wajen tsaftace abincin da suke girkawa don kare lafiyar masu siya da al’umma baki ɗaya. Alhaji Babangida Mati Musawa, ɗan asalin Jihar Katsina, ya yi wannan jawabi ne a yayin taron wata-wata na ƙungiyar ’Yan Tuwo-Tuwo da aka gudanar a Mile 12, inda suka tattauna kan matsalolin ƙungiyar da hanyoyin…
Read More
M.D na kasuwannin Sabon Gari, Singa da Galadima ya gwangwaje mata 150 da jarin N10,000 kowaccen su

M.D na kasuwannin Sabon Gari, Singa da Galadima ya gwangwaje mata 150 da jarin N10,000 kowaccen su

Daga RABIU SANUSI a Kano Shugaban kasuwannin Sabon Gari, Singa da Galadima, Alhaji Abdul Bashir ya raba wa mata kimanin ɗari da hamsin jarin dubu goma-goma ga kowaccensu. A jawabin shi, Manajan Daraktan kasuwannin Sabon Gari, Galadima Alhaji Abdul Bashir ya ce yana ƙara godiya ga Allah bisa wannan nasarar ta yau da ya yi namijin ƙoƙarin. Shugaban rukunin kasuwannin ya ce wannan tunani na yau na da nasaba da irin ƙoƙarin mata bisa riƙe amana da jajircewa da suke da shi a dukkan rayuwar. Yace wannan karon sun ɗauko mata 150 don basu wani ɗan tallafi wanda ba shi…
Read More
Gwamnatin Katsina za ta sakar wa ƙananan hukumomi 34 kuɗaɗensu duk wata

Gwamnatin Katsina za ta sakar wa ƙananan hukumomi 34 kuɗaɗensu duk wata

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Gwamna Dikko Raɗɗa ya yanke wannan shawara domin ƙarfafa shugabancin ƙananan hukumomi daga rushe. Mai baiwa Gwamna Shawara kan ƙananan hukumomi da babban mai binciken kuɗin na ƙananan hukumomi Alhaji Lawal Rufa'i Safana sanar da haka lokacin da ya ke ganawa da shi da babban audita na ƙananan hukumomi da shugabannin ƙananan hukumomi da Ma'ajin su a Katsina. Ya ce yanzu haka gwamnati na shirin biyan ƙananan hukumomin kuɗaɗen su da suka rage na watan Agusta da ya gudana. Safana ya faɗa masu cewa dole ne a matsayin su na masu sa hannu a fitar…
Read More
JIBWIBS ta sanar da rufe masallacin juma’a na Kankiya a Katsina

JIBWIBS ta sanar da rufe masallacin juma’a na Kankiya a Katsina

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Kwamitin masallacin juma'a na kungiyar Jama'atul Izalatul Bidi'a Wa Ikamatul Sunnah ta sanar da rufe masallacin da ke garin Kankiya sakamakon ambaliyar ruwa da ya mamaye masallacin. Masallacin da ke unguwar Layi quaters ya kai shekara 40 da tubawa,kuma wannan shine karo na farko ya fuskanci wannan iftala'i. Mai magana da yawun kwamitin Sheikh Khalid Kashim ya bayyana cewa yanzu za a rinƙa gudanar da sallar juma'a a Masallacin Masjid ibn Taymayya a unguwar Gurara. Ya ce sakamakon ambaliyar ruwa an dakatar da gudanar da salla a masallacin har sai wani lokaci. Sheikh Kashim ya…
Read More