Kasuwanci

Babu batun rage farashin fetur da gas, inji NNPC

Babu batun rage farashin fetur da gas, inji NNPC

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kamfanin Man Fetur na Nijeriya, NNPCL, ya musanta rahotannin da ake yaɗawa ya cewa ya rage farashin man fetur da iskar gas. NNPCL ya mayar da martanin ne kan wasu rahotanni da wasu kafafen watsa labaran Nijeriya ke yaɗawa cewar ya rage farashin man fetur da gas. Babban jami'in sadarwa na kamfanin Olufemi Soneye ne ya yi watsi da jita-jitar a wata sanarwar da ya rabawa manema labarai. Ya kuma buƙaci jama'a da su yi watsi da rahotannin. Sanarwar ta ce, "Kamfanin NNPCL na so ya yi wa al'umma ƙarin haske kan wasu rahotannin da ke…
Read More
Duk da taɓarɓarewar tattalin arziki, CBN ya ƙara kuɗin ruwa da kashi 24.75

Duk da taɓarɓarewar tattalin arziki, CBN ya ƙara kuɗin ruwa da kashi 24.75

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Babban Bankin Nijeriya ya ɗaga darajar manufofin hada-hadar kuɗi da aka fi sani da 'kuɗin ruwa' da kashi 200 cikin 100 zuwa kashi 24.75 daga kashi 22.75 cikin 100 a ƙoƙarin da ake na magance hauhawar farashin kayayyaki. Gwamnan babban bankin ƙasar CBN, Olayemi Cardoso, ne ya bayyana hakan a ranar Talata a wajen taron manema labarai na kwamitin kula da harkokin kuɗi karo na 294 a Abuja. Sabon kuɗin ruwa shi ne  kashi 2% daga kashi 22.75 cikin dari da MPC ta sanar kusan wata daya da ya gabata da kuma hauhawar farashi na biyu…
Read More
Sakamakon cire tallafin mai: Adadin fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan guda – Idris

Sakamakon cire tallafin mai: Adadin fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan guda – Idris

Daga BASHIR ISAH Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kan 'Yan Ƙasa, Muhammad Idris, ya bayyana cewa, adadin man fetur da ake amfani da shi a Nijeriya ya ragu da lita biliyan ɗaya, kwatankwacin kashi 53 na adadin man da ake amfani da shi gabanin cire tallafin mai. A cewarsa, hakan ya faru ne sakamakon tallafin fetur da gwamanti ta cire a watan Mayun Bara. Ya bayyana haka ne a wajen buɗe-baki tare da 'yan jarida da aka shirya kwanan nan a Kano. Idris ya ce, la'akari da yawan raguwar amfani da fetur da aka gani, hakan na nuni da…
Read More
Gwamnati ta dakatar da karɓar kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba

Gwamnati ta dakatar da karɓar kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa’ida ba

Daga BASHIR ISAH Ministan Tattalin Arziki kuma mai sanyo ido kan fannin kuɗi, Mr. Wale Edun, ya unarci Hukumar Kwastom da ta dakatar da karɓar kashi 25 daga hannun masu shigo da motoci daga ƙetare ba bisa ƙa'ida ba. Kakakin hukumar na ƙasa, Abdullahi Maiwada, shi ne ya bayyana haka cikin sanarwar da ya fitar a ranar Juma'a. Kwanan nan ne Gwamnatin Tarayya ta ba da sanarwar buɗe dama na tsawon kwana 90 don shigowa da wasu keɓaɓɓun motoci. Da ma dai hukumar kan amshi kashi 25 kan motocin da aka shigo da su ba bisa ƙa'ida ba a matsayin…
Read More
Akwai hanyoyin bunƙasa arziki a sauƙaƙe da ba kowa ya sani ba – Ƙiru

Akwai hanyoyin bunƙasa arziki a sauƙaƙe da ba kowa ya sani ba – Ƙiru

Daga AMINA YUSUF ALI (Cigaba daga kashi na farko) Assalamu Alaikum, barkan mu da wannan lokaci. Kamar yadda na yi alƙawari ta hannun Yayata AMINA YUSUF ALI, Wakiliyar Blueprint Manhaja, cewa, idan na samu damar samun wannan shafi na tattalin arziki mai albarka zan bayyana muku wasu hanyoyi da na gano da mutum zai iya zuba kuɗinsa kuma ya samu riba masu kyau in sha Allah. Kamar yadda na fara kwararo wa masu karatu wasu bayanai na daga dabarun da mutum zai yi amfani da su ya samu bunƙasar arziki a rayuwarsa.  A makon da ya gabata mun bayyana cewa, mutum…
Read More
Ku yi wa Allah ku tallafa wa talakawan ƙasa, roƙon Tinubu ga su Ɗangote

Ku yi wa Allah ku tallafa wa talakawan ƙasa, roƙon Tinubu ga su Ɗangote

Daga BASHIR ISAH Shugaban Ƙasar Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya roƙi hamshaƙan 'yan kasuwar ƙasar, wato Aliko Dangote, Abdulsamad Rabiu da sauran masu ƙumbar susa, da su dubi Allah sannan su taimaka wa marasa galihu musamman a wannan wata na Ramadan. Tinubu ya yi wannan kira ne ranar Lahadi a Kano a wajen ƙaddamar da shinkafar da Santa Abdullahi Yari ya tanada don tallafa wa jama'a don girmamawa ga Shugaba Tinubu. Tinubu ya bayyana hakan ne ta bakin wakilinsa kuma hadiminsa, Abdulaziz Abdulaziz, inda ya yaba da karamcin da sanatan ya nuna masa. Ya ce an ƙaddamar da tallafin ne…
Read More
Ku mayar wa ‘yan kasuwa kayan abinci da kuka ƙwace, umarnin Tinubu ga Hukumar Kwastom

Ku mayar wa ‘yan kasuwa kayan abinci da kuka ƙwace, umarnin Tinubu ga Hukumar Kwastom

Daga UMAR GARBA a Katsina Babban Kwantorola na Hukumar Hana Fasa-ƙwauri ta Ƙasa, Bashir Adewale Adeniyi, ya ce Shugaban Ƙasa asa Bola Ahmed Tinubu, ya ba wa hukumar umarni a kan ta mayar da kayan abinci da ta ƙwace daga hannun wasu 'yan kasuwa don sake kai su kasuwanni a sayar wa 'yan ƙasa. Shugaban hukumar ya bayyana haka ne lokacin da yake ganawa da masu ruwa da tsaki a garin Kwangwalam dake iyakar ƙaramar hukumar Mai'adua a jihar Katsina. A cewarsa, umarnin mayar da kayan abincin, wani jinƙai ne daga Shugaba Tinubu da kuma tabbatar da cewa al'umar ƙasar…
Read More
Canjin Dala kashi biyar ne a Nijeriya – Bashir Na’iya

Canjin Dala kashi biyar ne a Nijeriya – Bashir Na’iya

Daga AMINA YUSUF ALI Duk da cewa 'yan kasuwa su ma suna da rawar da za su taka wajen samun sauƙin tsadar kaya, amma ka da mu yi ta jibga musu laifi ba tare da mun dubi yadda canjin dalar kanta ya koma ba a Nijeriya. A halin da ake ciki yanzu a Nijeriya canjin dollar ya kasu kusan kashi biyar, kowa yana da farashinsa na canji. Misali: Canjin CBN daban,Canjin bayan fage ko kamfanonin canji daban,Canjin hukumar kwastam daban,Canjin 'yan Fesbuk ma daban,Canjin mazauna ƙasashen waje daban. Wallahi ni wannan bambanci har dariya yake ba ni, na rasa sanin…
Read More
Yadda kamfanonin layin waya suka kulle layuka miliyan 40 saboda Lambar ’Yan Ƙasa

Yadda kamfanonin layin waya suka kulle layuka miliyan 40 saboda Lambar ’Yan Ƙasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sama da layukan waya miliyan 40 ne kamfanonin sanadar na MTN, Airtel, Glo suka kulle a ƙarshen mako biyo bayan ƙarewar wa'adin ranar 28 ga Fabrairu, 2024 da Hukumar Sadarwa ta Nijeriya ta bayar na tilasta wa masu amfani da layuka haɗawa da Lambobin Shaidar Ɗan Ƙasa, NIN. Hakan ya nuna an samu ƙaruwar miliyan 28 daga layukan waya miliyan 12 da aka fara shirin kullewa, biyo bayan umarnin NCC. A cikin sanarwar Disamba 2023, NCC ta buƙaci kamfanoin da su toshe layukan da ba a haɗa su da lambar NIN na masu su ba a…
Read More
Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Ramadan: ‘Ku sassauta farashin kayan abinci’ — kiran Sarkin Kano, Ado-Bayero ga ‘yan kasuwa

Daga BASHIR ISAH Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado-Bayero, ya yi kira ga 'yan kasuwa da su sauke farashin kayan abinci da sauransu domin bai wa al'umma damar yin azumin Ramadan cikin walwala. Basaraken ya yi wannan kira ne a wajen taron ƙaddamar da littafi mai taken: “Dauloli a Ƙasar Hausa” wallafar Farfesa Sa’idu-Mohammed Gusau wanda ya gudana ranar Lahadi a Zaria. Kazalika, ya yi kira ga masu hannu da shuni da su dubi Allah su taimaka wa mabuƙata yayin watan na Ramadan. Ado Bayero ya yaba wa marubucin littafin bisa ƙoƙarin da ya yi wajen bayyana Masarautun Hausa da ke…
Read More