09
Dec
Daga JOHN D. WADA, a Lafiya Kwamitin da shugaban ƙaramar hukumar Karu a jihar Nasarawa barista Abubakar Aliyu Madaki ya kafa domin tantance lalacewa da kuma asarar dukiyoyi da aka yi sakamakon wata mummunar gobarar wuta da ta auku a kasuwar Masaka ta garin Karu din a bara ya gabatar da rahoton sa. Kwamitin wadda ke ƙarƙashin jagorancin shugabanta wato Cif Mark Auta a yayin zaman ya kuma ba da wasu shawarwari na musamman dangane da yadda za a aiwatar da matakan hana wuta a kasuwannin domin hana irin wannan abin gaggawa sake faruwa nan gaba da tabbatar da tsaro…
