Rahoto

Kasuwar Kurmi: Kasuwar da ta gina Jihar Kano ta kuma sauya tarihin kasuwancin Afirka ta Yamma

Kasuwar Kurmi: Kasuwar da ta gina Jihar Kano ta kuma sauya tarihin kasuwancin Afirka ta Yamma

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Blueprint Manhaja na ci gaba da kawo wa masu karatu shafinta na tarihi domin tunatar da al'umma muhimman abubuwan da suka taka rawa wajen gina tarihin Nijeriya, musamman waɗanda ba kasafai ake ba su kulawar da ta dace ba. A wannan makon, mun waiwayi tarihin Kasuwar Kurmi ta Kano, ɗaya daga cikin tsofaffin kasuwannin Afirka da ta yi fice wajen bunƙasa kasuwanci, sana'o'i da tattalin arziki tun sama da ƙarni biyar da suka gabata. Wannan nazari zai bayyana yadda kasuwar ta kasance ginshiƙin ci gaban Kano da kuma rawar da ta taka wajen haɗa Afirka Ta…
Read More
Koya wa matasa kamun kifi

Koya wa matasa kamun kifi

A ƙasar mu Nijeriya, musamman yankin Arewa, zaman kashe wando da matasa ke yi na ci wa gwamnati da duk wani mai kishin cigaban matasa tuwo a ƙwarya. Mun wayi gari mafi yawan matasanmu basu da ayyukan yi. Yayin da wasu da dama sun gama karatun su na digiri a jami'o'i a fannoni daban-daban amma babu aikin yi.  Sai dai a maimakon waɗannan matasa su nemi ananan sana'o'i da za su yi, sai dai ka ga mafi yawan su sun raina ƙananan sana'o'i da ayyukansu, suna ganin in ba aikin gwamnati da za a biya su kuɗaɗe masu yawa ba,…
Read More
Ta’addanci a Arewa: Ina mafita ta ke?

Ta’addanci a Arewa: Ina mafita ta ke?

A halin yanzu, babu shakka Arewa na matuƙar buƙatar mafita daga matsalolin rashin tsaro, musamman ta'addanci, garkuwa da mutane domin neman kuɗin fansa da kuma hare-haren 'yan bindiga. A cikin wannan makon ne muka samu rahoton yadda wasu da ake zargin 'yan ta'adda ne suka yi garkuwa da wani Alƙalin Babbar Kotu a Jihar Kebbi. Haka kuma, an kuma yi garkuwa da wani ɗan siyasa a Jihar Zamfara. Waɗannan al'amura abin takaici ne matuƙa. Sai dai, a wani ɓangaren kuma, an kama wasu da ake zargi da hannu wajen sace ɗalibai a Jihar Oyo, inda ake cewa alamu sun nuna…
Read More
Mu koyi hana juna ɓarna da yin ba daidai ba

Mu koyi hana juna ɓarna da yin ba daidai ba

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  Mai karatu yau za ka ji rubutuna na wannan makon ya ɗauki wani salo kamar na mai wa'azi to, ba wa'azi ba ne, faɗakarwa ce da tunatarwa daga almajiri mai neman ilimi. Domin shi wa'azi malamai masu tawali'u da tsoron Allah ne ke yin sa, da baki ko a cikin ayyukansu. Na ce haka ne don mu fahimci shi wa'azi ba kawai sai a wajen aikin addini ko a wurin ibada ake yin sa ba. Muna ganin abubuwan wa'azi da dama daga ayyukan malamai da koyarwar su, da kuma abubuwan da ke faruwa a kewayen mu.…
Read More
Shin ko kasan saka takalma marasa kyau na lalata ƙafa?

Shin ko kasan saka takalma marasa kyau na lalata ƙafa?

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake kasancewa a shafin Kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja. Sannunku da jimirin bibiyar mu.  Na san mai karatu zai iya ɗan saka alamar tambaya kan darasin namu, wato kalamar 'takalma mai kyau'. Idan tunaninka ya tafi kan tsari na kyau da ake gani a zahiri ne, to ka dawo baya, hakan zai sa ka fahimci inda darasin namu ya dosa. Takalma masu kyau da muka ambata na magana ne kan takalma masu bada lafiya, ba masu wahalar da ƙafa ba. Akwai takalma da muke wa laƙabi da 'orthopedic shoes' su musamman an gina…
Read More
Yadda cutar damuwa ta iyaye ke shafar ‘ya’yansu 

Yadda cutar damuwa ta iyaye ke shafar ‘ya’yansu 

Daga AISHA ASAS Mai karatu, barkanmu da sake saduwa a shafin Iyali na jaridar Blueprint Manhaja. A wannan mako za mu tattauna wani muhimmin batu da duk da girman tasirinsa ga rayuwar iyali, ba kasafai ake ba shi kulawar da ta dace ba, musamman a Arewacin Najeriya. Batu ne da ya shafi lafiyar ƙwaƙwalwa, musamman cutar damuwa (anɗiety) da kuma baƙin ciki mai tsanani (depression). A gidaje da dama, akwai matsalolin da ba sa bayyana a ido, amma suna girgiza zaman lafiyar iyali. Cutar damuwa da baƙin ciki na daga cikin irin waɗannan matsaloli. Mutane da yawa na rayuwa da…
Read More
Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (II)

Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (II)

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Bayan da Muhammadu Kanta ya samu nasarar tabbatar da 'yancin Daular Kabi, ya mayar da hankali wajen faɗaɗa mulkinsa. A cewar masana tarihi, mulkinsa ya bazu zuwa manyan yankuna na ƙasar Hausa da wasu sassan Yammacin Afirka. A gabas, iyakar mulkinsa ta kai har yankin Nguru, a masarautar Borno ta tsohon lokaci. A yamma kuma ya miƙa ikonsa zuwa yankunan da suka yi iyaka da tsohuwar Daular Oyo. A arewa kuwa, ya mamaye yankunan Arewa, Zabarma da wasu sassan da yanzu suke cikin Jamhuriyar Nijar. Haka kuma ya shimfiɗa ikonsa zuwa wasu yankunan da yanzu…
Read More
Majalisar Dokokin Katsina ta buƙaci gwamnati ta gyara muhimman hanyoyi

Majalisar Dokokin Katsina ta buƙaci gwamnati ta gyara muhimman hanyoyi

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina A zaman majalisar dokokin na ranar ƙarƙashin jagoranci mataimakin kakakin majalisar Rt Hon. Abduljalal Haruna Runka, majalisar ta gabatar da ƙuduri na tunatar da ɓangaren zartarwa na gwamnatin jihar, kan buƙatar sake gina wasu muhimman hanyoyi da suka lalace domin sauƙaƙa zirga-zirga da bunƙasa tattalin arziƙin al'ummomin da abin ya shafa. A ƙudurin da Hon. Umar Ali Bindawa, ɗan majalisa mai wakiltar ƙaramar hukumar Bindawa, ya gabatar, inda ya buƙaci majalisa ta turawa ɓangaren zartarwa da ta sake gina hanyar Bindawa, Dallaje, Doro Geremawa zuwa Kwanar Duwan. Hanyar wadda ta ratsa ƙananan hukumomin Bindawa da…
Read More
Zaɓen gwaji na hukumar INEC

Zaɓen gwaji na hukumar INEC

Hukumar Zaɓe ta ƙasa Mai Zaman Kanta (INEC) ta sanar da cewa za ta gudanar da zaɓen gwaji gabanin babban zaɓen ƙasa. Wannan mataki ya haifar da muhawara, inda wasu ke ganin tamkar wata alama ce da za ta iya bayyana ko za a samu gaskiya da adalci a zaɓe ko akasin haka. Akwai kuma masu nuna rashin amincewa da shugabancin shugaban INEC, bisa wasu kalaman da ake zargin ya taɓa furtawa tun kafin ya hau kan wannan muƙami. Wasu na fargabar cewa hakan na iya sa a yi duk mai yiwuwa wajen bai wa gwamnati mai ci goyon baya…
Read More
Waƙa:Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

Waƙa:Ta’aziyyar Hauwa Ƙamshi

Dags MUHAMMED BALA GARBA  1. Rabbana Sarki Ilahu,       Rabbi mai tayar da ruhu,    Rabbi ga baiwarka Hauwa. 2. Babu mai tsarki ya naka,  Babu mai rahama kamarka, Rabbi kai rahama ga Hauwa.  3. Babu mai jin ƙai kamarka,          Babu mai tausai irinka,   Don Rasulu ka dubi Hauwa. 4. Duk Karamci na wurinka,         Ragwame ita ce sifarka,   Rabbi rangwantawa Hauwa. 5. Yadda duk kayi babu mita,        Ba mu jayayya da yin ka, Rabbi kai rahama ga Hauwa. 6. Hauwa Ƙamshi jaruma ce,       Babu shakka malama ce,     Mai rubuce-rubuce Hauwa. 7. Rabbi duk an mata shaida,               Kamila ce mai ibada,      Sayyada laƙabi…
Read More