Rahoto

Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Kayan miliyoyin Naira sun kone a gobarar kasuwar Legas

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kayayyaki da darajarsu ta kai na miliyoyin Naira sun kone kurmus a ranar Larabar da ta gabata, yayin da wata gobara ta tashi a wasu shaguna a sashen Nnamdi Azikiwe da Docemo na Kasuwar Idumota a Jihar Legas. Gobarar ta shafi gine-gine guda uku da suka haɗa da benaye biyu da wani gini mai hawa uku a kasuwar waɗanda suka shahara  wajen sayar tufafi da jaka da takalma. Hukumar kashe gobara ta jihar Legas da sauran masu bada agajin gaggawa sun isa wurin, inda suka yi ta koƙarin aikin kashe gobarar. "Hukumomin kashe gobara a Ebute…
Read More
Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Tinubu zai tsige ministocin da suka gaza kataɓus

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Nijeriya Bola Tinubu yana shirin fara wani tsari mai matakai uku domin tantance ƙoƙarin ministoci, shugabannin ma’aikatu da hukumomin gwamnati. Manufar ita ce samar da wani shafi da zai ba jama'a damar yin bayanai game da koƙarin ministocin da ba da shawarar waɗanda za a riƙe da waxanda za a kora. Wannan yunkuri na zuwa ne yayin da Gwamnatin Tinubu ke tunkarar bikin cika shekara gyda a kan madafun iko a ranar 29 ga Mayu, 2024. Wasu majiyoyi masu ƙarfi a fadar shugaban kasa sun ce Shugaban kasar Tinubu zai ƙaddamar da wannan shafi ne…
Read More
Yadda jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Yadda jarumi Ali Nuhu ya karɓi ragamar aiki a matsayin Shugaban NFC

Daga AISHA ASAS A ranar Talata da ta gabata ne, shahararren jarumi a masana’antar Kannywood Dakta Ali Nuhu ya kama aiki a hukumance a matsayin Shugaban Hukumar Finafinai ta Qasa (NFC) tare da alƙawarin hanzarta kawo cigaba a masana’antar finafinan Nijeriya. Bayanin wanda ya fito daga wurin Daraktan Ya daa Labarai na hukumar, Mista Brian Etuk. A sanarwar wadda ya gabatar ga ‘yan jarida, Mista Brian ya ce, a ƙwarya-ƙwaryar bikin miqa mulki da aka gudanar a shelkwatar hukumar da ke Jos ta Jihar Filatu, wanda ya samu halartar manyan baqi, da suka haɗa da jiga-jigan masana’antar fim, ma’aikatan hukumar…
Read More
Ramadan: Abincin da ya kamata a ci da waɗanda za a ƙaurace wa

Ramadan: Abincin da ya kamata a ci da waɗanda za a ƙaurace wa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Miliyoyin Musulmai a faɗin duniya sun fara azumin watan Ramadana, ɗaya daga cikin watanni masu tsarki a addinin Musulunci. A lokacin Sahur (kafin alfijir) da kuma buɗa baki (magariba), yana da kyau a san takamaiman nau'ikan abincin da ya kamata a ci don tabbatar da ɗorewar kuzari da jin daɗin rayuwa gabaɗaya. Abubuwan da ya kamata a ci lokacin Sahur: A yayin Ramadan idan kana son ka yini da kwarinka da lafiya shi ne a ci abinci mai gina jiki, da sauransu, kuma dole ka sha ruwa sosai. A kuma ci abinci mara nauyi mai lafiya…
Read More
Naira 100,000 ba zai riƙe rayuwar ma’aikaci ba – Majalisar Wakilai

Naira 100,000 ba zai riƙe rayuwar ma’aikaci ba – Majalisar Wakilai

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Majalisar Wakilai ta bayyana cewa ya zama wajibi a daidaita albashin ma'aikatan Nijeriya, domin kuwa ƙasa da Naira 100,000 a wata ba zai riƙe rayuwar ma'aikaci ba. Majalisar ta ce ɗauki matakin tabbatar da ƙarin albashi ga ma’aikatan Nijeriya. An cimma wannan matsaya ne a zaman da aka yi a ranar Laraba, biyo bayan ƙudirin da shugaban marasa rinjaye Kingsley Chinda da wasu 39 suka gabatar. Yayin muhawara kan ƙudirin mai taken "Buƙatar ƙarin albashin ma'aikata a Nijeriya," mataimakin shugaban marasa rinjaye Aliyu Madaki ya bayyana ƙalubalen da 'yan Nijeriya ke fuskanta sakamakon hauhawar farashin kayayyaki.…
Read More
Hukumar Kwastom za ta binciki sanadin turmutsitsi a wurin cinikin shinkafa

Hukumar Kwastom za ta binciki sanadin turmutsitsi a wurin cinikin shinkafa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Hukumar Hana Fasa-ƙwauri ta Nijeriya, NCS, ta kafa kwamitin da zai binciki al’amuran da suka janyo turmutsitsin da kuma asarar rayuka da aka samu a tsohon ofishinta da ke Yaba, Legas. Shugaban hukumar Bashir Adeniyi, ya umurci kwamitin ƙarƙashin jagorancin wani jami’in hukumar da ya zaƙulo waɗanda rikicin ya rutsa da su tare da tsara hanyoyin bada tallafi ga iyalansu. Haka zalika, shugaban ya dakatar da rabon ne domin jajanta wa iyalan waɗanda suka rasu yayin da hukumar da ƙoƙarin samar da dabarun yadda za a cigaba da rabon cikin kwanciyar hankali. Bugu da ƙari, jami’in…
Read More
Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana farin ciki da irin salon mulkin gwamnati shugaba Tinubu duk da halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya. Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya kai masa ziyarci a Daura, Jihar Katsina. Shettima ya ce, Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ba za ta bar wani abu da zai kawo cikas a yunƙurinta na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya ba. Mataimakin shugaban Nijeriya ta cigaba da cewa, ya sha alwashin cewa gwamnati mai ci za…
Read More
Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Jami’ar Bayero da ke Jihar Kano, Farfesa Sagir Abbas, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta saki kuɗaɗen da aka ware domin katange jami'ar saboda matsalolin tsaro da ake fama da su. Farfesa Abbas ya bayyana halan ne yayin taron taro karo na 38 da aka gudanar a Jami’ar Bayero a Kano. Abbas ya jaddada muhimmancin waɗannan kuɗaɗe, inda ya bayyana cewa, duk da cewa akwai kaso na farko a cikin kasafin kuɗin tarayya na shekarar 2023, daga baya kuma an cire shi a shekarar 2024, wanda hakan ya sa jami’ar ta shiga cikin mawuyacin hali.…
Read More
Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwamitin Kula da Harkokin Gwamnati na Majalisar Wakilai ya bayar da wa'adin mako guda ga dukkan kamfanonin jiragen sama masu zaman kansu a ƙasar nan da su yi lissafin yadda suka kashe zunzurutun kuɗi har Naira Biliyan 4 da Gwamnatin Tarayya ta ba su don magance cutar COVID-19 ko kuma su dawo da kuɗaɗen. Kwamitin wanda ɗan jam’iyyar PDP daga jihar Osun, Bamidele Salam ya jagoranta, ya bayar da wa’adin ne a ranar Juma’a a wajen ci gaba da zaman bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen shiga a tsakanin ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya. An ruwaito…
Read More
Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Tsohon Kakakin Majalisar Dokoki Jihar Bauchi wanda a zaɓen gama-gari na ranar 18 ga watan Maris ta shekarar da ta gabata 2023 ya tsaya takarar zaɓen wa'adin wakilci zango na biyu, amma ya faɗi zaɓen, a ranar Laraba ya sake ɗare wa kujerar da ta shugabancin majalisar, sakamakon zaɓen cike gurbi da hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta yi a ranar 3 ga watan Fabrairu da ya gabata.  Ɗan takarar shiga majalisar dokoki na jam'iyyar APC daga mazaɓar Ningi ta Tsakiya, Malam Khalid Ningi, shine ya ƙalubalancin zaɓen na tsohon kakakin majalisa Abubakar Yakubu…
Read More