09
Mar
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana farin ciki da irin salon mulkin gwamnati shugaba Tinubu duk da halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya. Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya kai masa ziyarci a Daura, Jihar Katsina. Shettima ya ce, Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ba za ta bar wani abu da zai kawo cikas a yunƙurinta na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya ba. Mataimakin shugaban Nijeriya ta cigaba da cewa, ya sha alwashin cewa gwamnati mai ci za…