Rahoto

Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Ina farin ciki da matakan da gwamnatin Tinubu ke ɗauka – Buhari

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa yana farin ciki da irin salon mulkin gwamnati shugaba Tinubu duk da halin matsin rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya. Buhari ya bayyana haka ne a lokacin da mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya kai masa ziyarci a Daura, Jihar Katsina. Shettima ya ce, Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Tinubu ba za ta bar wani abu da zai kawo cikas a yunƙurinta na kare rayuka da dukiyoyin ’yan Nijeriya ba. Mataimakin shugaban Nijeriya ta cigaba da cewa, ya sha alwashin cewa gwamnati mai ci za…
Read More
Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Tsaro: Shugaban Jami’ar Bayero ya buƙaci a samar da kuɗin katange jami’ar

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Shugaban Jami’ar Bayero da ke Jihar Kano, Farfesa Sagir Abbas, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta saki kuɗaɗen da aka ware domin katange jami'ar saboda matsalolin tsaro da ake fama da su. Farfesa Abbas ya bayyana halan ne yayin taron taro karo na 38 da aka gudanar a Jami’ar Bayero a Kano. Abbas ya jaddada muhimmancin waɗannan kuɗaɗe, inda ya bayyana cewa, duk da cewa akwai kaso na farko a cikin kasafin kuɗin tarayya na shekarar 2023, daga baya kuma an cire shi a shekarar 2024, wanda hakan ya sa jami’ar ta shiga cikin mawuyacin hali.…
Read More
Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Ku dawo da kuɗin tallafi Korona – Majalisar Wakilai ga kamfanonin jiragen sama

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Kwamitin Kula da Harkokin Gwamnati na Majalisar Wakilai ya bayar da wa'adin mako guda ga dukkan kamfanonin jiragen sama masu zaman kansu a ƙasar nan da su yi lissafin yadda suka kashe zunzurutun kuɗi har Naira Biliyan 4 da Gwamnatin Tarayya ta ba su don magance cutar COVID-19 ko kuma su dawo da kuɗaɗen. Kwamitin wanda ɗan jam’iyyar PDP daga jihar Osun, Bamidele Salam ya jagoranta, ya bayar da wa’adin ne a ranar Juma’a a wajen ci gaba da zaman bincike kan zargin karkatar da kuɗaɗen shiga a tsakanin ma’aikatu da hukumomin gwamnatin tarayya. An ruwaito…
Read More
Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Yadda Kakakin majalisar Bauchi ya koma muƙaminsa bayan yin murabus  

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi Tsohon Kakakin Majalisar Dokoki Jihar Bauchi wanda a zaɓen gama-gari na ranar 18 ga watan Maris ta shekarar da ta gabata 2023 ya tsaya takarar zaɓen wa'adin wakilci zango na biyu, amma ya faɗi zaɓen, a ranar Laraba ya sake ɗare wa kujerar da ta shugabancin majalisar, sakamakon zaɓen cike gurbi da hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) ta yi a ranar 3 ga watan Fabrairu da ya gabata.  Ɗan takarar shiga majalisar dokoki na jam'iyyar APC daga mazaɓar Ningi ta Tsakiya, Malam Khalid Ningi, shine ya ƙalubalancin zaɓen na tsohon kakakin majalisa Abubakar Yakubu…
Read More
Abinda ya sa Sanusi fashewa da kuka a ta’aziyyar Shugaban bankin Access

Abinda ya sa Sanusi fashewa da kuka a ta’aziyyar Shugaban bankin Access

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II, ya bayyana yadda tsohon shugaban bankin Access, Herbert Wigwe ya ba shi gudunmawa a lokacin da aka sauke shi daga karagar mulki.  Yayin da yake jawabi a taron nuna alhinin rasuwar tsohon jami'an bankin da ya rasu a wani hatsarin jirgi tare da iyalinsa a Amurka, sarkin Kanon na 14 ya ce ya kaɗu matuƙa da jin labarin rasuwar mista Wigwe wanda ya taka rawar gani a rayuwarsa. “Na yi tunanin zan riga mista Herbert rasuwa. duka mun san irin kirkinsa, da biyayyarsa," inji Muhammadu Sanusi ll, lokacin da…
Read More
Tinubu ga ’yan Nijeriya: Ba zan yi gaggawa wajen sake fasalin ƙasa ba

Tinubu ga ’yan Nijeriya: Ba zan yi gaggawa wajen sake fasalin ƙasa ba

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaba Bola Tinubu ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya cewa gwamnatinsa za ta sake fasalin ƙasar kamar yadda ya yi alƙawari tun da farko, amma ya lura cewa dole ne a aza harsashi mai kyau. Tinubu ya bayar da wannan tabbacin ne a wata ziyarar da ya kai wa jagoran ƙungiyar siyasa da zamantakewar al’ummar Yarabawa ta ƙasa, Afenifere, Pa Reuben Fasoranti, a Akure, Jihar Ondo ranar Laraba. Bayan ganawar sirri da wasu zaɓaɓɓun shugabannin ƙungiyar, sakataren yaɗa labaran ƙungiyar na kasa, Mista Jare Ajayi, ya ruwaito shugaban qasar na tabbatarwa ‘yan Nijeriya cewa zai…
Read More
Sojojin Nijeriya na iya murƙushe ‘yan ta’adda – Gwamna Sule

Sojojin Nijeriya na iya murƙushe ‘yan ta’adda – Gwamna Sule

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce sojojin Nijeriya na da ƙarfin da za su iya lalata duk wasu masu ɗauke da makamai da ke dagula zaman lafiyar al’umma. Ya bayyana hakan ne a ranar Lahadin da ta gabata a yayin gudanar da ayyukan jin daɗin jama’a na Afirka ta Yamma na 2023 na rundunar sojojin Nijeriya ta IV a ƙaramar hukumar Doma ta jihar. Gwamnan ya yaba da kokarin sojoji da sauran jami’an tsaro a yaƙin da suke yi da garkuwa da mutane, ‘yan fashi da sauran matsalolin tsaro a ƙasar nan.…
Read More
An kashe mai juna biyu a turmutsutsun sayen shinkafar Kwastom

An kashe mai juna biyu a turmutsutsun sayen shinkafar Kwastom

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Mutane bakwai, ciki har da mace mai juna biyu sun rasu a yayin turereniyar sayen shinkafar da Hukumar Kwastam ta yi gwanjo a kan N10,000 kowane ƙaramin buhu a Jihar Legas. Wasu da dama kuma sun jikkata a turereniyar da ta barke a lokacin da wasu bata-gari suka yi yunƙurin shiga ofishin hukumar da ke gwanjon shinkafar da ƙarfin tuwo. Lamarin ya faru ne ranar Juma’a da hukumar ta fara gwanjon shinkafar a ofisinta da ke yankin Yaba. Gwanjon shinkafar da hukumar ke yi wani ɓangare na yunƙurinta rage wa ’yan Nijeriya raɗaɗin tsadar…
Read More
Yadda dillalin jarida ya rikiɗe zuwa shehin malamin jami’a

Yadda dillalin jarida ya rikiɗe zuwa shehin malamin jami’a

Daga BAKURA MUHAMMAD a Bauchi  An shawarci manema labarai da suke kan ganiyarsu a fagen fama, mazauna Jihar Bauchi da cewar, kowane ɗaya daga cikinsu zai iya ko za ta iya murjewa daga masomi ko tale-tale, cikin sana'arsa/ta ta yaɗa labarai, har ya/ta kai ga cimma muradun sa/ta na rayuwa, walau kan wannan sana'a da yake/take kai, ko wata makamanciya da za ta kai shi/ta ga tudun mun tsira. Wannan shawara ma'abuciyar ƙarfafa zuciya ta fito ne daga bakin wani jigon gwamnatin jihar Kaduna, kuma babba sakatare na sirri wa Gwamnan jihar ta Kaduna, Farfesa Bello Ayuba a kwanakin baya…
Read More
’Yan sanda sun musanta sace matafiya 26 a hanyar Gusau zuwa Sakkwato

’Yan sanda sun musanta sace matafiya 26 a hanyar Gusau zuwa Sakkwato

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar 'yan sandan Jihar Zamfara ta musanta ikirarin sace fasinjoji 26 da aka yi a kan hanyar Gusau zuwa Sakkwato. Rahotanni sun bayyana cewa, wasu gungun 'yan bindiga sun tare hanya tare da garkuwa da masu ababen hawa. Sai dai ’yan sandan sun yi gaggawar mayar da martani tare da fatattakar ’yan bindigar, lamarin da ya maido da zaman lafiya a yankin. Kakakin 'yan sandan Yazid Abubakar ya bayyana cewa yayin da ‘yan bindigar suka tare hanyar, babu wani fasinja da aka sace. Ya kuma jaddada cewa ’yan sanda sun yi nasarar tarwatsa ’yan bindigar, tare…
Read More