Rahoto

Cikakken jerin sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen Kungiyar Lauyoyin Nijeriya na 2026

Cikakken jerin sunayen waɗanda suka yi nasara a zaɓen Kungiyar Lauyoyin Nijeriya na 2026

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD An bayyana cikakken sakamakon zaɓen shugabannin ƙasa na ƙungiyar Lauyoyin Nijeriya (NBA) na shekarar 2026, bayan kammala zaɓe da kuma sanar da sakamakon da Kwamitin Gudanar da Zaɓen NBA (ECNBA) ya yi a ranar Lahadi. Kamar yadda aka ruwaito a baya, Babbar Lauya mai Matsayin SAN, Misis Oyinkansola Badejo-Okusanya, ta zama shugabar NBA ta 33 bayan ta doke sauran manyan lauyoyi biyu da suka fafata da ita a zaɓen shugaban ƙungiyar. Shugaban Kwamitin Gudanar da Zaɓen NBA (ECNBA), Aham Ejelam (SAN), ne ya sanar da sakamakon a hedikwatar ƙungiyar da ke Abuja. Badejo-Okusanya ta samu ƙuri'u…
Read More
Shehu bai ƙwace ƙasar kowa ba!

Shehu bai ƙwace ƙasar kowa ba!

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Sam Shehu Mujaddadi bai ƙwace ƙasar kowa ba, hasalima waɗanda su ka karɓi tuta ‘yan asalin yankin da su ke sarauta ne. Shehu Mujaddadi Bagobiri ne ko ɗan Gobir a matsayin mahaifarsa a ƙasarsa ta gado Wallahi akwai takaici da ban mamaki wani dan kwangilar AIFOB ko na makiya Arewa wanda ba shi ma da alaƙa ta kusa ko nesa da Hausawa; ya rubuta wai Shehu Mujaddadi ya ƙwace ƙasar Hausa ko ya yaƙi wani Sarki da sauran shirmen makirci da sai a soshiyal midiya dandalin bulus na Bello Badum a ke gani. In ka deɓe…
Read More
Duk da saukar hauhawar farashi, jihohi 19 da Abuja sun ci gaba da fuskantar tsaiko – NBS

Duk da saukar hauhawar farashi, jihohi 19 da Abuja sun ci gaba da fuskantar tsaiko – NBS

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Duk da cewa adadin hauhawar farashin kayayyaki a matakin ƙasa ya ɗan ragu a watan Yunin 2026, rahoton Hukumar ƙididdiga ta ƙasa (NBS) ya nuna cewa mazauna fiye da rabin jihohin Nijeriya na ci gaba da fama da matsanancin tashin farashi, inda jihohi 19 tare da Babban Birnin Tarayya Abuja, suka yi rajistar hauhawar farashi da ta zarce kashi 30 cikin ɗari. Sabon rahoton Ma’aunin Farashin Mabuƙaci (CPI) da hukumar ta fitar ya nuna cewa hauhawar farashin kayayyaki ta sauka kaɗan daga kashi 15.93 cikin ɗari da aka samu a watan Mayu zuwa kashi 15.91 cikin…
Read More
Trump ya jinjina wa Tinubu kan yaƙi da ta’addanci

Trump ya jinjina wa Tinubu kan yaƙi da ta’addanci

* Ya yi alƙawarin ƙarfafa haɗin gwiwa da Nijeriya Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu kan abin da ya bayyana a matsayin jajircewarsa wajen yaƙi da ta'addanci da magance matsalolin tsaro a Nijeriya, musamman hare-haren da ake kai wa al'ummomin Kiristoci. Yabon na ƙunshe ne cikin wata wasiƙa mai ɗauke da kwanan watan 6 ga Yulin 2026, wadda Trump ya aikewa Tinubu, kuma Fadar Shugaban ƙasa ta fitar da ita ga manema labarai ranar Laraba ta bakin Mai Bai wa Shugaban ƙasa Shawara na Musamman kan Yaɗa Labarai…
Read More
Majalisar Dattawa ta yi barazanar ladabtar da NNPCL, CBN, JAMB, NECO da sauran hukumomi kan ƙin amsa gayyatarta

Majalisar Dattawa ta yi barazanar ladabtar da NNPCL, CBN, JAMB, NECO da sauran hukumomi kan ƙin amsa gayyatarta

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Majalisar Dattawan Nijeriya ta yi barazanar amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba ta wajen ɗaukar mataki a kan wasu Ma’aikatu, Hukumomi da Cibiyoyin Gwamnati (MDAs) da suka ƙi amsa gayyatar Kwamitinta kan Harkokin Kuɗi domin gudanar da binciken sa ido. Barazanar ta fito ne bayan shugaban kwamitin, Sanata Sani Musa (Niger ta Gabas), ya gabatar da batu a zaman majalisar na ranar Laraba. Sanata Musa ya ce kwamitin na gudanar da bincike lokaci-lokaci bisa tanadin sashe na 88 da 89 na Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya domin tantance yadda hukumomin gwamnati ke…
Read More
Ku kama sana’a mata 

Ku kama sana’a mata 

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A cikin zamani da rayuwa ke ƙara saurin sauyawa, inda farashin kayan masarufi ke tashi ba kakkautawa, kuma buƙatun gida ke ƙaruwa a kowace rana, mata da dama a cikin al’umma suna tsintar kansu cikin wani sabon yanayi na tunani da neman mafita. Wannan yanayi ya sa batun sana’a ga mata ya zama ba kawai magana ta ci gaban kai ba, har ma da wani ginshiƙi na rayuwar iyali da zaman lafiya a gida. A baya, wasu al’adu sun kan ɗauki sana’ar mace a matsayin abin da ba ya da muhimmanci ko…
Read More
Ko akwai amfanin da garin shinkafa ke yi wa fata?

Ko akwai amfanin da garin shinkafa ke yi wa fata?

Daga AISHA ASAS  Kafin komai bari mu fahimci ita kanta garin shinkafa wadda za mu shimfiɗa darasin namu kai. Menene garin shinkafa? Garin shinkafa ana yin sa ne ta hanyar niƙa ƙwayar shinkafa ta zama gari. Amma ba dukkan garin shinkafa ne iri ɗaya ba. Yadda aka sarrafa shi na iya shafar amfaninsa. Shinkafa na da sassa uku: Fatar waje mai ƙarfi. Tsakiyar wadda wasu ke kira da tsakiyar rai Farin ɓangaren ciki. A duk waɗannan da na lissafa sashen waje shi ne mafi ɗauke da sinadarai masu kariya ga fata tare da kawar da wasu matsaloli kamar na rage…
Read More
Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (I)

Tarihin Muhammadu Kanta, wanda ya assasa Daular Kabi (I)

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Muhammadu Kanta na daga cikin fitattun jaruman da suka taka muhimmiyar rawa a tarihin Arewacin Nijeriya da yankin Yammacin Afirka. Shi ne ya assasa Daular Kabi, wadda ta zama ɗaya daga cikin manyan daulolin Hausa kafin zuwan Turawan mulkin mallaka. Har zuwa yau, zuriyarsa ce ke ci gaba da riƙe sarautar Kabi mai hedikwata a Argungu, Jihar Kebbi. Asalinsa: Riwayoyi sun nuna cewa Muhammadu Kanta ya fito ne daga zuriyar Usman ɗan Mas'ud, wanda ake cewa yana cikin mutanen da suke hidima a Haramin Ka'aba tun kafin bayyanar addinin Musulunci. Bayan Musulunci ya bunƙasa, kakanninsa…
Read More
Rayuwa bayan ritaya: Tsarin shirye-shirye a ilimance don samun ingantacciyar rayuwa

Rayuwa bayan ritaya: Tsarin shirye-shirye a ilimance don samun ingantacciyar rayuwa

Tare da BILKISU YUSUF ALI, P.hD Gabatarwa Ritaya wani mataki ne na rayuwa da kowane ma'aikaci zai iya fuskanta idan Allah Ya ba shi tsawon rai. A mafi yawan lokuta, mutane suna shiryawa ne domin samun aiki, samun albashi da gina iyali, amma ba sa bai wa rayuwa bayan ritaya muhimmancin da ta dace. Wannan rashin shiri kan haifar da matsalolin tattalin arziƙi, damuwa ta tunani, matsalolin lafiya da kuma rashin walwala. Masana ilimin zamantakewa da tattalin arziƙi sun nuna cewa shiryawa tun kafin ritaya yana taimakawa mutum ya ci gaba da rayuwa cikin mutunci, kwanciyar hankali da walwala. Ma'anar…
Read More
Shehu Mujaddadi bai ƙwace ƙasar kowa ba

Shehu Mujaddadi bai ƙwace ƙasar kowa ba

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Wallahi akwai takaici da ban mamaki wani ɗan kwangilar AIFOB ko na makiya Arewa wanda ba shi ma da alaka ta kusa ko nesa da Hausawa; ya rubuta wai Shehu Mujaddadi ya ƙwace ƙasar Hausa ko ya yaƙi wani Sarki da sauran shirmen makirci da sai a soshiyal midiya dandalin bulus na Bello Badum a ke gani. In ka deɓe ƙasar Gobir inda shi ma Shehu ɗan yankin ne, ba wasu wajaje da ya taka da kafarsa. Allah cikin ikonsa da’awarsa ta kai nisan inda ƙafarsa ba ta taɓa takawa ba. Hatta Gobir ɗin ma Wallahi…
Read More