Rahoto

Azumi a kimiyance

Azumi a kimiyance

Daga ALI ABUBAKAR SADIƙ Allah masani, ya sanar da mu cewa: Q41:53 ““Za Mu nuna musu ayõyinMu a cikin sasanni da kuma cikin rayukansu, har ya bayyana a gare su cewa lalle (Alƙur´ani), shi ne gaskiya. Ashe, kuma Ubangijinka bai isa ba, ga cewa lalle Shĩ halartacce ne a kan kowane abu ne?" Wannan aya sama da shekaru 1400 da saukar da ita, kuma tsawon zamunna a kullum Allah na jaddada wa Dan Adam ta hanyoyin kimiyya yadda ikonsa ke wanzuwa a halittu duniyoyi da sammai da kuma a cikin jikinmu. Na kurkusan nan shine tsarin Autophagy wanda Allah ya…
Read More
Obi da ’yan ƙabilanci zalla

Obi da ’yan ƙabilanci zalla

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Wannan matsaya ta ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC ga zaɓen Nijeriya na 2027 Peter Obi ta ture amfani da makircin ƙabilanci, na nuna ya yi saurin ankara cewa ‘yan kwangilar bazata a soshiyal midiya ba za su iya sama ma sa mafita a zaɓen ba. Haƙiƙa a zaɓen 2023 ya samu ƙuri’u masu yawa a tutar LEBA daga mabiya add!nin Kirista don ba mamaki yadda ita kuma APC a ka jefe ta da tsayar da dukkan ‘yan takara Musulmi. A wancan zaɓen Obi ba kawai ya tsaya da ɗan takarar mataimaki dan arewa kadai…
Read More
Yadda marubuta ke ba da gudunmawa ga zaman lafiya

Yadda marubuta ke ba da gudunmawa ga zaman lafiya

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU  A ƙarshen watan da ya gabata, haɗakar ƙungiyoyin marubutan adabi na Jihar Filato da ake yi musu laƙabi da COPLIS, ƙarƙashin ƙungiyar Marubutan Nijeriya ta ANA Plateau, suka gudanar da babban taron shekara-shekara da suka saba yi, domin tattauna gudunmawar marubuta da ƙalubalensu, rubutattun waƙoƙi, raye-raye da bajekolin kasuwar littattafai. Baƙi daga ciki da wajen Jihar Filato har ma da ƙetaren Nijeriya sun samu halartar taron, wanda aka yi wa taken, "Yadda rubutun adabi zai inganta zaman lafiya a Filato da wajenta." Taron, wanda shi ne irinsa na uku da aka shirya da nufin haɗa kan…
Read More
’Yan kasuwar katako na fatan Abba zai inganta kasuwar Rijiyar Lemo – Aikawa

’Yan kasuwar katako na fatan Abba zai inganta kasuwar Rijiyar Lemo – Aikawa

Daga MUHAMMADU MUJITABA a Kano Kwamared Shehu Inuwa Aikawa ya yi kira ga Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, da ya kara mayar da hankali wajen inganta kasuwar katako ta Rijiyar Lemo domin ta zama daya daga cikin manyan kasuwannin katako mafi inganci a Nijeriya. Aikawa ya ce gwamnatin jihar na da kudurin tabbatar da cewa Kano ta ci gaba da zama abin koyi wajen gudanar da ayyukan raya kasa, musamman karkashin manufar “Kano First”. Ya bayyana cewa akwai bukatar a gyara hanyoyin shiga da fita, magudanan ruwa da sauran muhimman ababen more rayuwa a kasuwar domin saukaka harkokin…
Read More
Ranar Dimukraɗiyya: Tinubu yana gina ƙwaƙƙwarar Nijeriya ta kowa da kowa – Idris

Ranar Dimukraɗiyya: Tinubu yana gina ƙwaƙƙwarar Nijeriya ta kowa da kowa – Idris

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Shugaba Bola Tinubu ya ƙudiri aniyar gina Nijeriya mai ƙwari, wadda ta haɗa kowa da kowa, kuma mai wadata, inji Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris. Ya faɗi haka ne a ranar Talata a Abuja a wurin taron manema labarai da aka shirya a matsayin wani ɓangare na bukukuwan Ranar Dimokiraɗiyya ta 2026. Idris ya ce, “Bikin Ranar Dimokiraɗiyya na wannan shekarar yana da muhimmanci ta musamman domin ya zo daidai da cikar shekara uku na gwamnatin Sabunta Fata. Wannan dama ce ta yin bitar irin cigaban da ƙasa ta…
Read More
Tarihin Mada Garin Aliyu Babba Dan Malam Muhammadu Sambo

Tarihin Mada Garin Aliyu Babba Dan Malam Muhammadu Sambo

Daga IBRAHIM MUHAMMAD Asalin su Fulani ne da suka fito daga yankin Ningi ta Jihar Bauchi da zummar za su kai caffa a wajen Mujaddadi Shehu Usman ɗanfodiyo Tagammadahullahu birahamatihi a Sakkwato domin shiga dumu-dumu a cikin jihadin jaddada addinin Musulunci wanda Mujaddadi Shehu Usman ɗanfodiyo ya jagoranta. Sun zauna a wurare da dama kamar ƙiru da Gwarzo (da ke Jihar Kano ta yau) da Matazu da Fawwa ( dake Jihar Katsina a halin yanzu) da kuma Wonaka da ke Jihar Zamfara ta yanzu, kafin daga bisani Malam Muhammadu Sambo ya jagorance su ya zuwa inda suke a halin yanzu.…
Read More
Hukumar REMASAB ta ƙaryata zargin rashin biyan ’yan shara albashinsu a Kano 

Hukumar REMASAB ta ƙaryata zargin rashin biyan ’yan shara albashinsu a Kano 

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Hukumar Kula da tsaftar muhalli da kwashe shara ta Jihar Kano (REMASAB) ta ƙaryata rahotannin da ke ikirarin cewa ba ta biyan ma’aikatanta albashi, tare da zargin cewa wasu ma’aikatan na karɓar Naira 10,000 kacal a kowane wata. A cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na hukumar, Abubakar Ahmad, ya fitar ranar 2 ga Yuni, 2026, REMASAB ta ce zarge-zargen da aka wallafa a wani flyer na shafin Facebook na gidan rediyon Dala FM ƙarya ne kuma ba su da alaƙa da ainihin halin da ake ciki a hukumar. Hukumar ta bayyana…
Read More
Sojoji sun halaka ‘yan bindiga 10, sun ceto mutane 31 a Zamfara da Katsina

Sojoji sun halaka ‘yan bindiga 10, sun ceto mutane 31 a Zamfara da Katsina

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Rundunar Sojoji a ƙarƙashin Atisayen FANSAN YAMMA, ta yi nasarar ceto mutane 31 da aka yi garkuwa da su, tare da halaka ’yan ta’adda guda biyar yayin wasu atisaye a Jihar Zamfara da Katsina. Haka kuma, sun ceto mutane 31 a yankin Bagega zuwa Kawaye da ke ƙaramar Hukumar Anka ta Zamfara bayan harbin bom daga jiragen yaƙi a maɓoyar ’yan ta’addan a Dajin Bagega. Rahotanni sun bayyana cewa, waɗanda aka ceton, sun shafe tsawon makonni da dama a tsare kuma ’yan asalin ƙananan hukumomin Maga, Gummi, Zuru, Wasugu, Bukuyyum, da Anka ne da…
Read More
Cutar Ebola: Me ya kamata mu sani

Cutar Ebola: Me ya kamata mu sani

Daga USMAN KAROFI Ebola Virus Disease (EVD)cuta ce mai tsanani da ƙwayar cuta ta Ebola ke haifarwa. Tana daga cikin cututtukan da idan aka kamu da ita, mafi yawa ana rasa rai, inda tsakanin kashi 25% zuwa 90% na masu kamuwa da ita kan rasa rayukansu idan ba a gano ta da wuri ba. Masana sun yi imanin cewa jemagu masu cin 'ya'yan itatuwa (fruit bats) su ne manyan ma'ajiyar wannan ƙwayar cuta. Yadda Ebola ke yaɗuwa Ana iya kamuwa da cutar ta hanyar hulɗa da jemagu ko wasu dabbobin da suka kamu da ita kamar birrai, ɓeraye da sauransu.…
Read More
Gwajin jini kafin aure: Ba iya kanjamau da genotype ya kamata a tsaya ba

Gwajin jini kafin aure: Ba iya kanjamau da genotype ya kamata a tsaya ba

Daga AISHA ASAS  (Ci gaba daga makon jiya) Baya ga wannan, akwai wasu gwaje-gwaje da suka shafi lafiyar jiki gaba ɗaya waɗanda ya kamata a kula da su kafin aure.  Cutar hanta irin su hepatitis, alal misali, na iya wucewa daga mutum zuwa mutum ko daga uwa zuwa jariri. Haka kuma akwai cututtukan da ake ɗauka a matsayin “ƙanana” amma suke da babbar illa ga jarirai, kamar wasu cututtukan da mace za ta iya kamuwa da su ba tare da ta sani ba, amma su shafi jaririn da take ɗauke da shi. Haka kuma batun gwaje-gwajen hormones yana da muhimmanci,…
Read More