23
Feb
Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fadar shugaban ƙasa da kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar sun yi ta cacar baki mai zafi game da manufofin tattalin arzikin gwamnatin tarayya, musamman faɗuwar darajar Naira. Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyan ya yi doguwar magana a shafinsa na X a ranar Lahadi, inda ya zargi Bola Tinubu da jefa tattali a matsala. Atiku Abubakar yana ganin kura-kuren gwamnatin Tinubu sun gurgunta tattalin arzikin Nijeriya, wanda hakan ya jawo tashin da Dala ta ke yi. A jawabinsa, Atiku wanda ya zo na biyu a zaɓen 2023 ya ce, kyau a canja irin salon da ake…