Rahoto

Tinubu da Atiku sun yi musayar yawu kan taɓarɓarewar tattalin arziki

Tinubu da Atiku sun yi musayar yawu kan taɓarɓarewar tattalin arziki

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Fadar shugaban ƙasa da kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar sun yi ta cacar baki mai zafi game da manufofin tattalin arzikin gwamnatin tarayya, musamman faɗuwar darajar Naira. Tsohon mataimakin shugaban Nijeriyan ya yi doguwar magana a shafinsa na X a ranar Lahadi, inda ya zargi Bola Tinubu da jefa tattali a matsala. Atiku Abubakar yana ganin kura-kuren gwamnatin Tinubu sun gurgunta tattalin arzikin Nijeriya, wanda hakan ya jawo tashin da Dala ta ke yi. A jawabinsa, Atiku wanda ya zo na biyu a zaɓen 2023 ya ce, kyau a canja irin salon da ake…
Read More
Abubuwan da ya kamata a sani kan ƙudirin ƙirƙirar ’yan sandan jihohi

Abubuwan da ya kamata a sani kan ƙudirin ƙirƙirar ’yan sandan jihohi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ƙudirin da ke neman a yi wa Kundin Tsarin Mulki na 1999 kwaskwarima domin bai wa gwamnoni damar naɗa kwamishinonin ’yan sandan jihohi a Nijeriya ya tsalake karatu na biyu a zauren Majalisar Wakilai domin shawo kan matsalolin rashin tsaro da suka addabi ƙasar. Ƙudirin wanda 'yan majalisar 13 suka ɗauki gabatar, ya samu goyon bayan mafi rinjayen 'yan majalisar waɗanda suka yi imanin cewa gwamnonin jihohi ya kamata su mayar da hankalinsu ga halin da ake ciki na rashin tsaro a faɗin ƙasar. Da alamu dai an kama hanyar kawo ƙarshen tirje-tirje da ma tayar…
Read More
‘Yadda ‘yan bindiga suka yi awon gaba da ‘yan mata tara a Zamfara

‘Yadda ‘yan bindiga suka yi awon gaba da ‘yan mata tara a Zamfara

Daga SANUSI MUHAMMAD a Gusau Wasu gungun 'yan bindiga sun afka wa Unguwar Mareri dake cikin Gusau, babban Birnin Jihar Zamfara a daren ran Asabar inda suka yi awon gaba da 'yan mata tara tare da wani maƙwabcinsu . Rahotanni sun nuna cewar 'yan bindigar da ɗauke da muggan makamai sun yi dirar mikiya a Unguwar sunata harbe-harbe kafin su samu nasarar sace 'yan matan. Hakazalika, wakilinmu ya tattaro cewar 'yan matan da lamarin ya shafa 'yan asalin garin Anka ne cikin Ƙaramar Hukumar Anka a jihar ta Zamfara. Waɗanda abun ya rutsa da su sun haɗa da: Sanaratu Marafa,…
Read More
’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya

’Yan Majalisa Wakilai 60 sun buƙaci a sauya fasalin Nijeriya

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ’Yan Majalisar Wakilai sama da 60 ne ke neman a yi wa Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya kwaskwarima zuwa tsarin da ke ɗauke da Fira Minista kamar yadda aka faro a ƙasar.  A ƙarƙashin jagorancin Wale Raji, ɗan majalisar wakilai na jam’iyyar APC mai wakiltar Jihar Legas, sun nemi sauyi a Kundin Tsarin Mulkin ƙasar. Daga cikin hujjojinsu akwai rage yawan kashe kuɗaɗe wurin gudanar da mulki da samar da tsare-tsare. Har ila yau, masu goyon bayan ƙudurin sun tabbatar da cewa sabon tsarin ba zai fara aiki yanzu ba, zai iya kai wa zaɓen shekarar 2031.…
Read More
Tsohon soja mai kai wa ’yan ta’adda kayan sojoji ya shiga hannu

Tsohon soja mai kai wa ’yan ta’adda kayan sojoji ya shiga hannu

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar 'Yan Sandan Nijeriya ta kama wani tsohon jami’in sojan saman Nijeriya, bisa samunsa da hannu wajen samar da kakin soja ga ’yan bindiga da suka addabi Jihar Zamfara. An bayyana sunan sa da Ahmed Mohammed, jami’in da aka kora, wanda a baya yana aiki a sansanin sojin sama da ke Kaduna, ya aikata wannan ta’asa ne bayan kotu ta gurfanar da shi bayan wani laifin da sojoji suka aikata da ba a bayyana ba. Kakakin rundunar ’yan sandan ACP Muyiwa Adejobi ya bayyana cewa Mohammed ya haɗa kai da Mushiri Abubakar wajen raba kayan sojoji…
Read More
Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Na yi bankwana da gasar iyo a bikin ‘Rigata’, inji Rahana jarumar gasar

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi Rahana Ibrahim Bunzawa wacce ta lashe gasar iyo (Linƙaya) wato tsere cikin ruwa ta ce ta yi bankwana da wannan wasa na ruwa har abada. Ta bayyana haka ne a lokacin da ta ke ganawa da wakilinmu a garin Yawuri jim kaɗan bayan kammala bikin 'Rigata' da aka gudanar kwanan nan. Ta ce wannan shi ne karo na biyu da ta ke lashe wannan gasar a jere kuma a duk lokacin da ta shiga ita ce samun nasara saboda haka ta yi bankwana da shiga gasar Rigata daga bana. "Na soma shiga gasar tun…
Read More
Yadda bikin ‘yar marubuciya Bilkisu Ali ya ƙayatar

Yadda bikin ‘yar marubuciya Bilkisu Ali ya ƙayatar

DAGA MUKHTAR YAKUBU An daura auren Sarra Tasi'u Ya'u Babura 'yar marubuciya 'yar Jarida kuma malama a Jami'ar Alqalam Hajiya Bilkisu Yusuf Ali tare da yin tarukan biki na kece raini. An daura auren Sarra Tasi'u Babura da angota Salihu Ibrahim Darma (Khalifa) ne dai a ranar Juma'a 9 ga Fabarairu 2024 ne a gidan Imam Sheikh Dr. Yusuf Ali da ke Unguwar Tudun Maliki ta Karamar Hukumar Kumbotso a cikin garin Kano da misalin 2-30 na rana inda dumbin jama'a suka halarci daurin auren. Bayan daurin auren ne kuma uwar amarya ta shirya taron wuni a wajen taro na…
Read More
Gwamna Idris ya yi wa yaran da ba sa zuwa makaranta rajista a Kebbi

Gwamna Idris ya yi wa yaran da ba sa zuwa makaranta rajista a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Birnin Kebbi  Gwamna Nasir Idris ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kira taron ilimi na dukkan masu ruwa da tsaki a fannin ilmi don karfafa dabarun bunqasa ilimi da cigaban ilimi a jihar Kebbi.  Ya bayyana haka ne a wajen bukin kaddamar da rabon kayayyakin ilimi ga yaran da ba su zuwa makaranta a garin Birnin Kebbi a ranar Talatar da ta gabata.  Ya bayyana cewa bayan rantsar da wannan gwamantin kawo yau ta kashe sama da Naira biliyan tara wajen samar da yanayi mai kyau a makarantu da suka hada da gyare-gyare da gina azuzuwa,…
Read More
Cin hanci da rashawa sun ragu a Nijeriya – CISLAC

Cin hanci da rashawa sun ragu a Nijeriya – CISLAC

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wata kididdiga da Kungiyar Transparency International ta fitar kan rashawa ta nuna cewa an samu ci gaba wajen yaki da matsalar a Nijeriya inda a yanzu jasar ke mataki na 145 cikin kasa 180 da aka yi nazari a kai. Kididdigar ta nuna cewa Nijeriya ta kara maki daya kan maki 24 da take da shi a baya inda a yanzu take da maki 25 cikin 100 baya ga matsawa daga matsayinta na 150. Kididdigar na duba yadda yanayin matsalar rashawa take a gwamnatin kasashen da aka yi nazarinsu. Tana bai wa kowace kasa…
Read More
Hukuncin Kotun Ƙoli: Ban ƙulla wata yarjejeniya da Tinubu ba – Gwamna Abba

Hukuncin Kotun Ƙoli: Ban ƙulla wata yarjejeniya da Tinubu ba – Gwamna Abba

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano a ranar Litinin ya karyata rade-radin dake yi na cewa ya kulla yarjejeniya da Fadar Shugaban Kasa gabanin hukuncin da Kotun Koli ta yanke ranar 12 ga watan Janairu wanda ya tabbatar da zabensa. Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da babban daraktansa na yada labarai da bayanai, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, ya fitar a Kano a ranar Litinin. Dawakin-Tofa ya bayyana wata takarda da tuni ta ke yawo tare da nuna wasu yarjejeniyoyi hudu tsakanin gwamna da fadar shugaban kasa a matsayin wata tatsuniyar da…
Read More