21
Jul
Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD An rantsar da matashi, Nehemiah Danjuma a matsayin lauya a Nijeriya, inda ya kafa tarihi a matsayin mutum na farko mai matsalar ji, wato kurma, daga Arewacin ƙasar da aka rantsar domin fara aikin lauya. Matashi Danjuma, ɗan asalin Jihar Kaduna daga ƙaramar Hukumar Jaba, ya kammala karatun digirin farko na fannin Shari'a da sakamako na Second Class Upper a Jami'ar Ilorin. Daga bisani ya kammala shirin Bar Part II a harabar Abuja ta Makarantar Koyon Aikin Lauya ta Nijeriya. Da yake sanar da wannan gagarumar nasara a shafinsa na ɗ, Danjuma ya rubuta cewa: "Kurma…
