Rahoto

Ba takardar digiri kaɗai ake buƙata a jami’a ba – Shettima

Ba takardar digiri kaɗai ake buƙata a jami’a ba – Shettima

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Mataimakin Shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima, ya ce lokaci ya yi da jami'o'in Nijeriya za su sauya salon aikinsu ta hanyar zama cibiyoyin ƙirƙire-ƙirƙire, kasuwanci da bunƙasa masana'antu, maimakon mayar da hankali kan fitar da masu takardun shaida kawai. Shettima ya bayyana hakan ne yayin ƙaddamar da cibiyar Manufacturing Technology Uniɓersity Innoɓation Pod (Manu-Tech UniPod) a Jami'ar Noma ta Michael Okpara da ke Umudike, ƙaramar hukumar Ikwuano a Jihar Abia. An kafa cibiyar ne domin haɓaka ƙirƙire-ƙirƙire a fannin fasaha da kuma bunƙasa harkokin kasuwanci. Shirin haɗin gwiwa ne tsakanin Shirin Raya ƙasashe na Majalisar ɗinkin…
Read More
Dangote zai gina babbar matatar mai a Kenya

Dangote zai gina babbar matatar mai a Kenya

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Rukunin Kamfanonin Dangote ya bayyana shirinsa na samar da kuɗaɗen gina sabuwar matatar mai mai ƙarfin tace ganga 700,000 a kowace rana a ƙasar Kenya, ta hanyar haɗa kuɗaɗen shiga na cikin gida, fitar da takardun bashin gwamnati da kuma kuɗaɗen da ake sa ran samu daga sayar da hannayen jari ga jama'a (IPO). Sabuwar matatar, wadda za a gina a Tsibirin Lamu da ke gabar tekun Kenya, ana sa ran za ta kasance mafi girma a Gabashin Afirka, tare da taimakawa wajen ƙarfafa tsaron makamashi a yankin ta hanyar rage dogaro da shigo da tataccen…
Read More
Akanza ya yabi Tinubu da Gwamna Sule kan ayyukan hanyoyi

Akanza ya yabi Tinubu da Gwamna Sule kan ayyukan hanyoyi

Daga JOHN D WADA a Lafia Shugaban yankin raya Lafia ta Arewa Hon. Nasiru Kasimu Akanza ya yaba wa shugaba Bola Ahmed Tinubu da gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa bisa ayyukan hanyoyi da ake cigaba da yi, yana mai cewa ayyuka ne na tarihi da za su inganta cigaban tattalin arziki da sauƙaƙe zirga-zirga a faɗin ƙasa. Da yake tattaunawa da manema labarai a ofishinsa da ke Shabu na ƙaramar hukumar Lafia, Akanza ya yaba da ƙaddamar da aikin babbar hanyar Akwanga zuwa Jos da Gombe da Maiduguri da kuma buɗe hanyar kilomita 3 mai layi biyu da aka…
Read More
Kadarori: An ɗage yanke hukuncin shari’ar Malami da EFCC

Kadarori: An ɗage yanke hukuncin shari’ar Malami da EFCC

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Babbar kotun tarayya da ke zama a birnin Abuja ta amince da ɗage ranar yanke hukunci na ƙarshe dangane da ƙarar da hukumar yaƙi da yi wa tattalin arzikin ƙasa ta'annati (EFCC) ta shigar, tana neman a ba ta damar ƙwace wasu manyan ƙadarori guda hamsin da bakwai (57) na tsohon ministan shari’a kuma babban lauyan ƙasa (AGF), Abubakar Chika Malami (SAN).Alƙalin kotun, mai shari’a Emeka Nwite, ne ya sanar da ɗage zaman bayan da lauyoyin ɓangarorin biyu suka kammala gabatar da hujjojinsu na ƙarshe a gaban kotun. Hukumar EFCC tana neman babban hukunci na…
Read More
Gwamnatin Nasarawa ta amince da ɗaukar malaman firamare 1000 aiki

Gwamnatin Nasarawa ta amince da ɗaukar malaman firamare 1000 aiki

Daga JOHN D WADA a Lafia Kimanin masu neman aiki 10,000 ne suka fafata domin samun guraben aikin malaman makarantar firamare 1,000 da gwamnatin jihar Nasarawa ta amince da su ƙarƙashin wani tsari na musamman na ƙauyuka kamar yadda jami’in gwamnatin ya bayyana a ranar Litinin na mako da ake ciki a Lafia. Mataimaki na musamman ga gwamna Abdullahi Sule kan harkokin jama’a hon. Peter Ahemba wanda ya wakilci gwamnan a wani taron manema labarai na kowanne watanni biyu da aka gudanar a sakatareiyar ƙungiyar ‘yan jaridu ta ƙasa, NUJ ta jihar Nasarawa dake Lafia babban birnin jihar ne ya…
Read More
An garzaya da wata uwargida asibiti bayan samun labarin mijinta ya ƙara aure a ɓoye

An garzaya da wata uwargida asibiti bayan samun labarin mijinta ya ƙara aure a ɓoye

Wata mata mazauniyar garin Ashaiman da ke ƙasar Ghana ta kwanta jinya a asibiti bayan ta suma sakamakon gano cewa mijinta ya auri wata mata a matsayin mata ta biyu ba tare da sanar da ita ba. Rahotanni sun bayyana cewa yayin da ake gudanar da bikin auren matar ta biyu a wani wuri daban, mijin ya shafe ranar yana gida tare da matarsa ta farko kamar yadda suka saba yi, ba tare da ya nuna wata alamar cewa yana shirin ƙara aure ba. An ce matar ta farko ta samu labarin auren ne bayan an kammala komai, lamarin da…
Read More
Sabon cece-kuce ya ɓarke kan mutuwar jarumi Alex Ekubo 

Sabon cece-kuce ya ɓarke kan mutuwar jarumi Alex Ekubo 

Ya wofantar da mahaifiyarsa, ba mai mutunci a idonsa sai matar ubansa, inji ɗan uwan jarumin  Daga AISHA ASAS  Watanni kaɗan bayan rasuwar fitaccen jarumin Nollywood Alex Ekubo, sabon rikici ya ɓarke cikin iyalansa bayan wani mutum da ya bayyana kansa a matsayin ɗan uwansa, Clinton Ekubo, ya fito da jerin zarge-zarge da suka sake ɗaga hankalin jama'a kan yadda rayuwar marigayin ta kasance kafin mutuwarsa da kuma yadda aka gudanar da jana'izarsa. A cikin wani dogon saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Clinton ya yi ikirarin cewa matar mahaifin Alexx ta taka muhimmiyar rawa wajen yanke muhimman…
Read More
Kotu ta ba da belin Sowore kan miliyan N200

Kotu ta ba da belin Sowore kan miliyan N200

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa fitaccen mai fafutukar kare haƙƙin al’umma kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Omoyele Sowore, belin Naira miliyan 200 a shari’ar da ake da shi inda ake zargin sa da aikata laifin da ya shafi intanet. Hukumar ‘yan sandan farin kaya (SSS) ce ta gurfanar da editan jaridar Sahara Reporters bisa zargin cewa ya aikata laifin da ya saɓa da dokokin amfani da intanet bayan kiran shugaba Tinubu da “mai laifi” a wasu rubuce-rubucensa da ya wallafa a shafukan sada zumunta a bara. Mai shari’a Mohammed…
Read More
Ku kama sana’a mata 

Ku kama sana’a mata 

(Ci gaba daga makon jiya) Daga AISHA ASAS A cikin zamani da rayuwa ke ƙara saurin sauyawa, inda farashin kayan masarufi ke tashi ba kakkautawa, kuma buƙatun gida ke ƙaruwa a kowace rana, mata da dama a cikin al’umma suna tsintar kansu cikin wani sabon yanayi na tunani da neman mafita. Wannan yanayi ya sa batun sana’a ga mata ya zama ba kawai magana ta ci gaban kai ba, har ma da wani ginshiƙi na rayuwar iyali da zaman lafiya a gida. A baya, wasu al’adu sun kan ɗauki sana’ar mace a matsayin abin da ba ya da muhimmanci ko…
Read More
Kifi ya faɗo daga sama ya kashe tsuntsu

Kifi ya faɗo daga sama ya kashe tsuntsu

Wani lamari mai ban mamaki ya faru a ƙasar Kanada inda wani mutum ya tarar da wani tsuntsu matacce a harabar gidansa tare da wani kifi a gefensa. Da farko dai mutumin ya kasa fahimtar abin da ya faru, domin babu ruwa ko kogi a kusa da wurin. Bayan masana sun gudanar da bincike, sun bayyana cewa wataƙila wani babban tsuntsu mai farauta ne ya kama kifin daga ruwa domin ya ci. Sai dai yayin da yake shawagi a sama, kifin ya kuɓuce daga bakinsa ya faɗo ƙasa da ƙarfi. Ana zargin cewa kifin ya bugi wani tsuntsu da ke…
Read More