Rahoto

Abu-Bilal Al-Minuki: Wane ne jagoran ISIS wanda Nijeriya da Amurka suka murƙushe?

Abu-Bilal Al-Minuki: Wane ne jagoran ISIS wanda Nijeriya da Amurka suka murƙushe?

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban ƙasar Amurka, Donald Trump, ya tabbatar da cewa dakarun Amurka da na Nijeriya sun yi nasarar halaka Abu-Bilal al-Minuki, wanda aka bayyana a matsayin mataimakin shugaban ƙungiyar ISIL a matakin duniya, a wani farmakin haɗin gwiwa na yaƙi da ta’addanci da aka gudanar a Nijeriya. Trump, a wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, ya bayyana cewa an shirya aikin cikin tsari mai inganci, tare da yabawa haɗin gwiwar dakarun Amurka da rundunar sojin Nijeriya wajen bin diddigin tare da kawar da jagoran ’yan ta’addan. Haka kuma, Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu…
Read More
’Yan uwantakar addini ta fi ƙarfin ta ƙabila

’Yan uwantakar addini ta fi ƙarfin ta ƙabila

Daga NASIRU ADAMU EL-HIKAYA Tun ’yan bazata na nanata kalmomin batanci da a ka lakkana mu su na jifar waɗanda a ke son su tunzura don kyasta ashana ga Arewa amma yayyafi daga Allah ya kwantar da ƙurar, yanzu mutanen sun shiga babin murde wuyan tarihin tushen Musulunci don mabiya su koma harkar fifita ƙabilanci kan addinin. Da zarar Musulmi sun jingine girman darajar mika wuya 100% ga umurnin Allah sun koma son zuciya ta ƙabilanci to sun gama yawo don ƙarshe a ka iya shigo da addinin nan na BA ALLAH a dakatar da mutane daga sallah, azumi da…
Read More
Hattara dai iyaye!

Hattara dai iyaye!

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Wani rahoto da kafar watsa labarai ta Arewa Updates ta wallafa game da wani malamin Islamiyya da aka kama kuma ake zargi da lalata da wasu ƙananan yara mata su huɗu, dake karatu a makarantar da yake koyarwa a garin Inusawa, a Karamar Hukumar Ungogo ta Jihar Kano, ya yi matuƙar tayar min da hankali. Sakamakon irin takaici da abin tausayi da ke cikin wannan labari. Kodayake kawo lokacin rubuta wannan rahoto, rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun kama wannan baragurbin malami, ana bincike kan anin da ake zarginsa a kai. Ba tun yanzu ba…
Read More
Wata na’urar ATM ta watso kuɗi ba tare da kati ba a Amurka

Wata na’urar ATM ta watso kuɗi ba tare da kati ba a Amurka

An shiga ruɗani a wani gari a Amurka bayan wata na’urar cire kuɗi ta ATM ta fara bayar da kuɗi ba tare da amfani da kati ko lambar sirri ba. Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne bayan na’urar ta samu matsalar fasaha, inda take ci gaba da fitar da daloli ga duk wanda ya danna maɓallin cire kuɗi. Da fari mutane sun ɗauka wata talla ce ko gwaji daga banki, amma bayan wasu sun samu kuɗi cikin sauƙi, sai labari ya bazu cikin gaggawa. Cikin ƙanƙanin lokaci mutane suka fara taruwa suna yin layi domin cire kuɗin, yayin da…
Read More
Boko Haram ta sace yara 42 a matsayin ganimar yaƙi

Boko Haram ta sace yara 42 a matsayin ganimar yaƙi

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  Iyayen ƙananan yara 42 ’yan ajin raino da ’yan ta’adda suka sace daga makaranta a yankin Mussa da ke ƙaramar Hukumar Askira-Uab a Jihar Borno, sun koma ga yin addu’o’i domin neman kuɓutar ’ya’yansu. A ranar Juma’a da misalin ƙarfe 9 na safe ne mayaƙan Boko Haram suka kutsa a wata Makarantar Firamare da ƙaramar Sakandaren Gwamnati da ke ya koma Mussa, suka yi abin gaba da ƙananan yara 42, yawancinsu ’yan shekara 2 zuwa 5. Bayan kimanin kwana biyar da sace yaran ba tare da jin ɗuriyarsu ba, iyayensu da malamai sun duƙufa…
Read More
Tirela ta halaka ‘yar sanda da wani mutum a Gombe

Tirela ta halaka ‘yar sanda da wani mutum a Gombe

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Wani mummunan hatsarin mota da ya faru a yankin Sabuwar Mile 3 da ke kan hanyar Gombe zuwa Yola ya yi sanadin mutuwar mutane biyu, ciki har da wata jami’ar ’yan sanda, tare da jikkatar wasu da dama. Lamarin ya faru ne a ranar Laraba, lokacin da wata babbar mota ƙirar DAF wadda ke ɗauke da buhunan hatsi, ta yi hatsari ta kuma kutsa cikin babura uku, masu tafiya a ƙasa da kuma wasu shaguna da ke gefen hanya. Binciken farko da rundunar ’yan sanda ta gudanar ya nuna cewa direban motar ya yi…
Read More
Waɗanne hanyoyi ne ake iya sarrafa man jojoba?

Waɗanne hanyoyi ne ake iya sarrafa man jojoba?

Daga AISHA ASAS  Mai karatu barkanmu da sake kasancewa da shafin Kwalliya na jaridar Blueprint Manhaja. Sannunku da jimirin bibiyarmu.  Kamar yadda muka shafe makonni biyu muna tattaunawa kan wannan darasi mai muhimmanci. A wannan makon ma za mu sake ɗibo wani ɓangare ne daga wannan tsiro mai tarin albarka.  Ana iya amfani da man jojoba ta hanyoyi da dama, waɗanda ke iya taimaka wa wajen inganta fata tare da bata lafiya kan matsalolin ta da dama. Jojoba oil na da matuƙar amfani a fannoni da dama: 1. A matsayin mai cire kayan kwalliya (makeup remover): Masana fata sun sha…
Read More
Masarautar Katsina ta bayar da lambobin yabo ga hakimai da su ka yi zarra a hawan ƙaramar sallah

Masarautar Katsina ta bayar da lambobin yabo ga hakimai da su ka yi zarra a hawan ƙaramar sallah

Daga ABDULLAHI MUHAMMAD a Katsina Sarkin Katsina Alhaji Abdulmumini Kabir Usman ya gabatar da kofin da lambobin yabo ga hakimai da su kayi zarra a hawan ƙaramar sallah da ta gabata. Magajin Garin Katsina, Alh. Aminu Abdulmumini Kabir Usman shine ya zamo na ɗaya a hawan sallah ƙarama da ta gabata, inda Ƙauran Katsina Alh. Aminu Nuhu Abdulƙadir ya zamo na biyu sai Ɗan Galadiman Katsina Hakimin Ƙafur yazo na uku. Kurayen Katsina Alhaji Darda'u shine yazo na huɗu sannan daga na huɗu zuwa na goma an basu lambar yabo sannan sauran hakiman su 28 su ma an basu takardar…
Read More
A kiyaye martabar aure da mutuncin iyalinmu

A kiyaye martabar aure da mutuncin iyalinmu

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU Mai karatu, nasan ba za ka kasa jin labarin nan da ya karaɗe kafafen watsa labarai da zaurukan sada zumunta ba, wanda aka ce wasu mutane bakwai a garin Azare da ke cikin ƙaramar Hukumar Karagum suna musanyar matansu na aure a tsakanin su. Mutumin da ya ɓullo da wannan sabon tsarin ya ce a mafarki ya gani ana umartarsa da su fara musanyar matansu a tsakaninsa da abokanensa su bakwai, waɗanda suka yi imani da wannan aƙida mai suna "Huddadu". Binciken rundunar Hisba ta garin Azare ya gano cewa, an kwana biyu ana wannan musanyen…
Read More
Nijeriya za ta iya zama cibiyar samar da magunguna a Afirka — Shugaban NAIP

Nijeriya za ta iya zama cibiyar samar da magunguna a Afirka — Shugaban NAIP

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Shugaban ƙungiyar Masana Haɗa Magunguna ta Masana’antu ta Nijeriya (NAIP), Pharm. (Sir) Bankole Ezebuilo, ya buƙaci Gwamnatin Tarayya da ta gaggauta ƙarfafa tallafi ga masana’antun haɗa magunguna na cikin gida domin rage dogaro da shigo da magunguna daga ƙasashen waje tare da mayar da Nijeriya cibiyar samar da magunguna a nahiyar Afirka. Ezebuilo ya bayyana hakan ne yayin taron ƙasa karo na 29 na shekara-shekara da horaswar ƙungiyar NAIP da aka gudanar a Ilorin, babban birnin jihar Kwara. Da yake jawabi a taron mai taken: “Haɗin Gwiwa da ƙirƙire-ƙirƙire Domin Gina Mafita Ta Cikin Gida Don…
Read More