06
Jan
Daga ISAH GIDAN ƁAKKO a Zariya Sakatariyar Ilimi ta Karamar Hukumar Zariya, Dokta Hassana Muhammad Lawal ta bayyana kudurinta na bin duk hanyoyin da su ka dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar makarantun firamare a karamar hukumar Zariya. Dr. Hassana Lawal ta bayyana haka ne a jawabin da ta yi a lokacin dora dambar makarantun firamare da suke qaramar hukumar Zariya, inda ta fara da makarantar firamare ta Zage-zagi a birnin Zariya. Dr. Hassana ta bankado matsalolin da su ke addabar makarantun firare a karamar hukumar Zariya da suka hada da gine-ginen gidaje da sauran gine-gine da al'umma…