Rahoto

Gina jami’o’i biyu a Kano ne ya sa muke son Kwankwaso — Hon. Sa’ad Darki

Gina jami’o’i biyu a Kano ne ya sa muke son Kwankwaso — Hon. Sa’ad Darki

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Tsohon gwamnan Jihar Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya samu yabo daga Hon. Sa’ad Ibrahim Darki, wanda aka fi sani da Janar, bisa irin gudummawar da ya bayar wajen bunkasa ilimi a jihar Kano. Hon. Sa’ad Janar ya bayyana cewa gina jami’ar Aliko Dangote University of Science and Technology (ADUSTECH) Wudil a tsakanin shekarun 1999 zuwa 2003, da kuma jami’ar Northwest University a lokacin wa’adin mulkinsa na biyu daga 2011 zuwa 2015, na daga cikin manyan dalilan da suka sa yake goyon bayan Kwankwaso. Ya ce Kwankwaso ya nuna kishin ilimi musamman ga ‘ya’yan talakawa,…
Read More
Yadda Hon. Abba Anas ya rasa ransa a hannun ’yan bindiga duk da karɓar kuɗin fansa

Yadda Hon. Abba Anas ya rasa ransa a hannun ’yan bindiga duk da karɓar kuɗin fansa

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD ’Yan bindiga sun sako gawar tsohon ɗan Majalisar Wakilai ta ƙasa kuma jigo a jam’iyyar ADC, Abba Anas Adamu, bayan da iyalansa suka biya kuɗin fansa har Naira miliyan 50. Rahotanni sun bayyana cewa an sace marigayin tare da wani ɗan siyasa daga jihar Jigawa, Ali Tukur Gantsa, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Abuja domin halartar taron jam’iyyar ADC. Majiyoyi kusa da iyalan sun shaida cewa masu garkuwar sun fara neman Naira miliyan 100 a matsayin kuɗin fansa, kafin daga bisani aka sasanta aka rage zuwa Naira miliyan 50. An ce kuɗin ne ya…
Read More
Oba Ewuare: Basaraken tagulla na birnin Benin

Oba Ewuare: Basaraken tagulla na birnin Benin

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAD Benin dai tana ɗaya daga ƙasashen yamma Afrika kuma ita ƙaramar ƙasa ce, da can ana kiranta da Dukome. A shekara ta 1894 ƙasar Faransa ta mamaye ƙasar, zuwa shekara ta 1960 ta samu ’yancin kanta. Benin tana da iyaka da ƙasashe huɗu, su ne, daga gabacinta Nijeriya, daga yammacinta Togo, daga arewacinta Nijar, daga arewa maso yammaci Burkina Faso. Benin ƙasa ce me tsuwo daga kudanci zuwa arewaci (650 )km, kuma tsawanta daga gabarce zuwa yammace ( 110 ) km, harshen Faransanci shi ne yaren ƙasar, tana kuma da yawan mutane kimanin (4,418,000 ). A…
Read More
Zuwa ga mata da maza: Faɗakarwa kan batun yadda ake yaɗa bidiyon tsiraici a zamanin yau

Zuwa ga mata da maza: Faɗakarwa kan batun yadda ake yaɗa bidiyon tsiraici a zamanin yau

A cikin wannan zamani da fasahar sadarwa ta zama ruwan dare, an shiga wani sabon yanayi da ke haifar da babbar matsala ga tarbiyya da mutuncin al’umma. Abin da a da ake ɓoye shi a cikin sirri da kunya, a yau ya koma ana ɗaukarsa a matsayin abin wasa ko soyayya ta zamani. Musamman yadda wasu ’yan mata ke tura wa samari bidiyon tsiraici, ko kuma hotunan da ba su dace ba, yana daga cikin abubuwan da ke rusa ginin tarbiyyar al’umma cikin gaggawa. Wannan wasiƙa tana da manufar yin kira na musamman ga ’yan mata da maza baki ɗaya,…
Read More
Kamar Neja kamar Filato: Yadda za a magance matsalar tsaro a jihohinmu

Kamar Neja kamar Filato: Yadda za a magance matsalar tsaro a jihohinmu

Daga ABBA ABUBAKAR YAKUBU A yayin da nake wannan rubutu, shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya amince da bayar da gudunmawar Naira Biliyan 2 da za a yi amfani da su wajen tallafawa waɗanda harin Anguwar Rukuba a Jos ya shafa, da ma rikicin da ya biyo baya. Shugaban ƙasa ya bayyana haka ne, a yayin taron masu ruwa da tsaki da ya kira zuwa fadarsa, domin tattauna hanyoyin magance rikicin da ya addabi Jihar Filato tsawon shekaru. Shugaban ƙasa ya shaidawa shugabannin al'umma da suka je ƙarƙashin jagorancin Gwamnan jihar Caleb Mutfwang, waɗanda suka haɗa da tsofaffin gwamnoni, tsofaffin ministoci,…
Read More
1999 zuwa 2026: Yadda manyan ’yan siyasa ke farfaɗo da ƙananan jam’iyyu

1999 zuwa 2026: Yadda manyan ’yan siyasa ke farfaɗo da ƙananan jam’iyyu

Daga MAHDI MUSA MUHAMMAMD Tun bayan dawowar Nijeriya kan tafarkin mulkin dimukraɗiyyar Nijeriya a shekarar 1999 zuwa sauye-sauyen siyasa da ake gani a 2026, ƙananan jam’iyyun siyasa da ba su da ƙarfi sun riƙa samun karɓuwa, kuɗaɗen shiga da kuma fitowa fili ne ta hanyar shigowar manyan ’yan siyasa da ke sauya sheƙa daga manyan jam’iyyu sakamakon rikice-rikicen cikin gida, rashin nasara a zaɓen fidda gwani ko kuma dabarun sake tsarawa. Duk da cewa Nijeriya na bin tsarin jam’iyyu da dama, gasa ta fi karkata ne ga manyan jam’iyyu irin su PDP, APC da kuma LP. A ƙasa da wannan…
Read More
Ya kamata Gwamna Abba ya fahimci manufar Shugaba Tinubu akan Farouk Lawan

Ya kamata Gwamna Abba ya fahimci manufar Shugaba Tinubu akan Farouk Lawan

Daga NASIR S. GWANGWAZO Daga dukkan alamu Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ɗauki matsaya kan wanda zai tsaya wa Jam’iyyar APC takarar ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Ɓagwai da Shanono a babban zaɓen 2026, inda yake ƙoƙarin mika takarar ga wanda ba shine akasarin al’ummar yankin suke so ba, duk da cewa, mazaɓar tana da mai neman takarar wanda duk Nijeriya an yarda da tasirinsa a majlisar dokoki ta ƙasa, wato tsohon ɗan majalisa, Hon. Farouk Lawan. Sunan Hon. Farouk Lawan ba baƙon abu ba ne a siyasar Nijeriya, ballantana ta Jihar Kano, mahaifarsa, saboda…
Read More
Yadda mutumin da ya mutu ya bayyana kwana guda bayan binne shi

Yadda mutumin da ya mutu ya bayyana kwana guda bayan binne shi

Al’ummar garin Masindi da ke ƙasar Uganda sun wayi gari cikin ɗimuwa da al’ajabi bayan da wani mutum da aka bayyana cewa ya mutu ya sake bayyana a garin ’yan awanni kacal bayan an riga an binne gawarsa. Lamarin ya haifar da ruɗani mai tsanani a tsakanin iyalansa da mazauna yankin, inda aka kasa fahimtar yadda abin ya faru. Rahotanni daga mujallar Daily Monitor ta intanet sun bayyana cewa mutumin mai suna Godwin Baguma, wanda ke zaune a yankin Kijura a tsakiyar Uganda, an ce ya yi ɓatan dabo na makonni da dama kafin daga bisani a gano wata gawa…
Read More
Cikar AKCILS shekaru 50: Abba Bichi da Farfesa Ibrahim sun samu lambar yabo kan tallafin ilimi

Cikar AKCILS shekaru 50: Abba Bichi da Farfesa Ibrahim sun samu lambar yabo kan tallafin ilimi

Daga MUHAMMADU MUJITTABA a Kano Kwalejin Shari’a da Addinin Musulunci da ke Kano, wato Aminu Kano College of Islamic and Legal Studies (AKCILS), ƙarƙashin jagorancin Farfesa Balarabe Jakada, ta ba Hon. Abba Bichi, ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar ƙaramar hukumar Bichi a Abuja, kyautar lambar yabo tare da wasu mutane bisa tallafin ilimi da suke bayarwa. An bayar da lambar yabon ne a yayin bikin cikar kwalejin shekaru 50 da kafuwa, wanda aka gudanar a harabar makarantar a makon da ya gabata. A jawabinsa, wanda ya karɓi kyautar a madadin Hon. Abba Bichi, mai ba shi shawara kan harkokin ilimi,…
Read More
Jihohin Jigawa, Kano, Katsina na kan gaba wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta – UNICEF

Jihohin Jigawa, Kano, Katsina na kan gaba wajen yawan yaran da ba sa zuwa makaranta – UNICEF

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja  An ayyana jihohin Jigawa, Kano da Katsina a matsayin waɗanda suka fi yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a yayin da asusun tallafa wa ƙananan yara (UNICEF) ke jaddada buƙatar tallafa wa ilimin yara daga tushe. A cewar UNICEF, Nijeriya na da yara miliyan 18.3 da ba sa zuwa makaranta a faɗin duniya. Jami’ar tuntuɓa na UNICEF a Kano, Aisha Abdullahi, ce ta bayyana hakan a yayin wata ganawa ta kwana biyu na ‘yan jaridu daga jihohin Jigawa da Kano da Katsina. A yayin da take gabatar da jawabinta jan ginshiƙin koyo da…
Read More