Rahoto

Akwai buƙatar kowa ya sa hannu wajen farfaɗo da ilimin firamare a Zariya – Dr. Hassana

Akwai buƙatar kowa ya sa hannu wajen farfaɗo da ilimin firamare a Zariya – Dr. Hassana

Daga ISAH GIDAN ƁAKKO a Zariya Sakatariyar Ilimi ta Karamar Hukumar Zariya, Dokta Hassana Muhammad Lawal ta bayyana kudurinta na bin duk hanyoyin da su ka dace domin kawo karshen matsalolin da suke addabar makarantun firamare a karamar hukumar Zariya. Dr. Hassana Lawal ta bayyana haka ne a jawabin da ta yi a lokacin dora dambar makarantun firamare da suke qaramar hukumar Zariya, inda ta fara da makarantar firamare ta Zage-zagi a birnin Zariya. Dr. Hassana ta bankado matsalolin da su ke addabar makarantun firare a karamar hukumar Zariya da suka hada da gine-ginen gidaje da sauran gine-gine da al'umma…
Read More
Emefiele: EFCC ta kai wa Ɗangote sumame bayan rikitowarsa a matsayin attajirin Afirka

Emefiele: EFCC ta kai wa Ɗangote sumame bayan rikitowarsa a matsayin attajirin Afirka

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Jami’an Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, EFCC, a ranar Alhamis, sun kai samame babban ofishin Kamfanin Dangote dake Legas. Kamar yadda shafin jaridar TheCable ya rawaito, jami’an hukumar sun gudanar da bincike kan kudaden da aka ware wa kamfanin a zamanin Godwin Emefiele, tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya CBN. Amma Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya qi cewa komai kan batun. Sai dai wani ma’aikacin Kamfanin Dangote ya tabbatar da cewa, jami’an EFCC na nan a babban ofishin kamfanin. “Sun bukaci a ba su takardu kan hada-hadar kudi da CBN,” inji ma’aikacin.…
Read More
Sauyin yanayi: Ƙalubalen da wasu garuruwa ke fuskanta a Jihar Yobe

Sauyin yanayi: Ƙalubalen da wasu garuruwa ke fuskanta a Jihar Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Rahoton da Hukumar Kula da Yanayi ta Nijeriya ta fitar a 2019 ya bayyana cewa Nijeriya ta na asarar kimanin fili mai fadin murabba'in kadada 350,000 a duk shekara, sakamakon yadda hamada ke ci gaba da mamayewar yankuna, wanda hakan ya na faruwa ne ta musababbin sauyin yanayi, mai alaka da ayyukan yau da kullum da Dan Adam masu jawo dumamar yanayi. A nata bangaren, a wani sabon binciken da Hukumar Agora Policy ta gudanar a wannan shekara (2023), ta bayyana cewa, Nijeriya za ta iya yin hasarar Dalar Amurka kimanin biliyan 460 sakamakon sauyin…
Read More
Emefiele ya nesanta kansa daga zarge-zargen talauta Nijeriya

Emefiele ya nesanta kansa daga zarge-zargen talauta Nijeriya

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Tsohon Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele, ya karyata zargin da Mai Binciken CBN Na Musamman da Shugaba Bola Tinubu ya nada ya yi masa, wato Jim Obazee. Kwanan nan Obazee ya gabatar wa Tinubu rahoton harqallar da ya bankado Emefiele ya aikata a CBN, wadda aka yi zargin ya bindige biliyoyin nairori da biliyoyin daloli. Cikin harkallar da Obazee ya bankado har da badakalar sauya launin kudi, wadda Obazee ya ce damfara ce kawai sata Emefiele ya kantara. Da ya ke karyata zarge-zargen da Obazee ya yi masa Emefiele a ranar Lahadi…
Read More
Tarihi da siyasar rayuwar Ghali Umar Na’Abba

Tarihi da siyasar rayuwar Ghali Umar Na’Abba

Daga MAHDI M. MUHAMMAD An haife shi ne a gidan Umar Na’Abba, babban dan kasuwa a Tudun Wada, cikin birnin Kano, a ranar 27 ga Satumba, 1958. Mahaifinsa ya kasance mai karfin tarbiyya kuma malamin addinin Musulunci. Mahaifinsa ya koya masa kyawawan halaye na aiki tukuru, kasuwanci, sahihiyar magana, jajircewa, halin sassaucin ra'ayi, hankali, ladabi da son addini sosai. Ilimi: Ya yi makarantar firamare ta Jakara da ke Kano, inda ya samu shaidar kammala karatunsa na farko a shekarar 1969, sannan ya halarci Kwalejin Rumfa da ke Kano, inda ya samu shaidar kammala karatu ta Afirka ta Yamma. A tsakanin…
Read More
Harin Filato: Ku ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki – Sarkin Musulmi ga gwamnati

Harin Filato: Ku ɗauki ƙwaƙƙwaran mataki – Sarkin Musulmi ga gwamnati

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar, ya bayyana damuwarsa kan harin da aka kai jihar Filato, inda aka kashe sama da mutane 155 a jajibirin Kirsimeti. Ya yi kira ga gwamnati da ta wuce yin Allah wadai da hare-haren tare da inganta matakan tsaro. Ya yi wannan jawabin ne a wajen rufe taron koyar da sana’o’in addinin musulunci karo na 8 da aka gudanar a filin wasa na Abubakar Tafawa Balewa a ranar Larabar da ta gabata, wanda kungiyar dalibai musulmi ta Nijeriya, MSSN ta shirya. Da yake bayyana damuwarsa kan yawaitar tavarvarewar tsaro a…
Read More
‘Yan sanda sun cafke ɗalibar da ke kai wa ’yan bindiga rahoto

‘Yan sanda sun cafke ɗalibar da ke kai wa ’yan bindiga rahoto

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja An cafke wata dalibar Kwalejin Kiwon Lafiya da ke Kontagora, kan zarginta da kai wa ’yan bindiga bayanai a Jihar Neja. Kwamishinan ’yan sandan Jihar Neja, Shawulu Ebenezer Danmamman, ya ce an cafke dalibar da ke karatu a Kwalejin Kimiyyar Kiwon Lafiya da ke Kontagora ne bayan an kama wani dan bindiga mai shekara 37. A yayin binciken dan bindigan da aka kama a garin Kontagora ne aka gano lambar dalibar a cikin wayarsa. Ita kuma a wurin bincike aka gano sunan wani dan bindiga da ake nema ruwa a jallo, Shaibu Haruna a…
Read More
Ɗan majalisa ya tallafa wa makarantar Islamiyya a Funtuwa

Ɗan majalisa ya tallafa wa makarantar Islamiyya a Funtuwa

Daga DAUDA USMAN a Legas Dan malalisar dokokin Jihar Katsina mai wakiltar Karamar Hukumar Funtuwa a zauren majalisar jihar Katsina Hon, Abubakar Muhammed Total Funtuwa kuma Shugaban Kwamitin Lafiya a majalisar jihar Katsina ya bai wa wata makarantar Islamiyya a mazabarsa mai suna Anwaruddin Islamic Centre Funtuwa gudunmawar kudi har Naira dubu dari biyar a matsayin gudunmawar da makarantar take nema a hannuwan al'ummar Musulmi domin ara fadada ajijuwan makarantar baki daya. Dan majalisar dokokin na jihar Katsina Hon, Abubakar Muhammed Total Funtuwa ya bai wa makarantar wannan gudummawar ce a Funtuwa a lokacin da makarantar ta Anwaruddin Islamic Centre…
Read More
Rasuwar Ghali Na’abba babban rashi ne ga ƙasar nan – Ɗanpass

Rasuwar Ghali Na’abba babban rashi ne ga ƙasar nan – Ɗanpass

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Fitaccen dan kasuwa basarake Dan-Saran Kano, Alhaji Gambo Muhammad Danpass ya bayyana mutukar alhininsa bisa rasuwar tsohon kakakin majalisar wakilalai na Nijeriya, Rt. Hon. Ghali Umar Na'abba. Ya bayyana cewa rasuwar Ghali babban rashi ne ba ga jihar Kano kadai ba har ma da Arewa da kasa baki daya. Sannan fitaccen dan siyasa ne wanda ya yi gwagwarmaya domin tabbatar da adalci a tsarin tafiyar da dimukradiyyar kasar nan. Alhaji Gambo Muhammad Danpass ya ce a lokacin da yake kakakin majalisar wakilai kowa ya shaida a kasar nan, bai zama dan kanzagi ko dan amshin…
Read More
Tsofaffin ɗaliban makarantun kimiyya na Kano sun yi aniyar samar da jami’a

Tsofaffin ɗaliban makarantun kimiyya na Kano sun yi aniyar samar da jami’a

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Kungiyar tsofaffin dalibai na makarantun kimiyya na jihar Kano sun ci alwashin samar da jami'a ta kungiyar. Sabon Shugaban Kungiyar na Kasa, Alhaji Balarabe Jallah ne ya bayyana haka a jawabinsa na karbar jan ragamar kungiyar bayan rantsar da su a taron shekara da kungiyar ta gudanar a Jami'ar Bayero. Ya ce duba da yawan da suke da shi na 'yan kungiyar ya kamata a ce sun jawo hankalin masu ruwa da tsaki domin yara da suke fitowa daga makarantun kimiyyar da su rika fita waje suna karatu idan jami'ar ta samu za ta taimaka…
Read More