Rahoto

Rasuwar Ghali Na’abba babban rashi ne ga ƙasar nan – Ɗanpass

Rasuwar Ghali Na’abba babban rashi ne ga ƙasar nan – Ɗanpass

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Fitaccen dan kasuwa basarake Dan-Saran Kano, Alhaji Gambo Muhammad Danpass ya bayyana mutukar alhininsa bisa rasuwar tsohon kakakin majalisar wakilalai na Nijeriya, Rt. Hon. Ghali Umar Na'abba. Ya bayyana cewa rasuwar Ghali babban rashi ne ba ga jihar Kano kadai ba har ma da Arewa da kasa baki daya. Sannan fitaccen dan siyasa ne wanda ya yi gwagwarmaya domin tabbatar da adalci a tsarin tafiyar da dimukradiyyar kasar nan. Alhaji Gambo Muhammad Danpass ya ce a lokacin da yake kakakin majalisar wakilai kowa ya shaida a kasar nan, bai zama dan kanzagi ko dan amshin…
Read More
Tsofaffin ɗaliban makarantun kimiyya na Kano sun yi aniyar samar da jami’a

Tsofaffin ɗaliban makarantun kimiyya na Kano sun yi aniyar samar da jami’a

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Kungiyar tsofaffin dalibai na makarantun kimiyya na jihar Kano sun ci alwashin samar da jami'a ta kungiyar. Sabon Shugaban Kungiyar na Kasa, Alhaji Balarabe Jallah ne ya bayyana haka a jawabinsa na karbar jan ragamar kungiyar bayan rantsar da su a taron shekara da kungiyar ta gudanar a Jami'ar Bayero. Ya ce duba da yawan da suke da shi na 'yan kungiyar ya kamata a ce sun jawo hankalin masu ruwa da tsaki domin yara da suke fitowa daga makarantun kimiyyar da su rika fita waje suna karatu idan jami'ar ta samu za ta taimaka…
Read More
Yadda sunayen manoman bogi suka mamaye shirin bunƙasa noman alkama a Yobe

Yadda sunayen manoman bogi suka mamaye shirin bunƙasa noman alkama a Yobe

Daga MUHAMMAD AL-AMEEN a Damaturu Gwamnatin Tarayya ta sha ɓullo da muhimman shirye-shirye da tsare-tsaren farfaɗo da harkokin noma, don inganta tattalin arziki, ayyukan yi tare da samar da isasshen abinci ga al'ummar ƙasa baki ɗaya. Wanda a zahiri, waɗannan muhimman shirye-shirye; idan an aiwatar da tsarin da yake a rubuce a takardun bayanai, hakan zai taimaka wajen kawo mafita ga wasu daga cikin wahalhalun da yan Nijeriya suke fuskanta na ƙarancin abinci da hauhawar farashinsa. Shirye-shiryen tallafa wa ayyukan da za su farfaɗo da aikin noma tare da manoma sun haɗa da amfani da ƙungiyoyin manoma na ƙasa, waɗanda…
Read More
Hukumar Abuja za ta rusa gidaje 200 don gina filin saukar jirgin shugaban ƙasa

Hukumar Abuja za ta rusa gidaje 200 don gina filin saukar jirgin shugaban ƙasa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya umurci daraktan sashen kula da cigaban ƙasa da ya tabbatar da cewa al'ummar Nuwalege da ke kan titin filin jirgin sama sun ba da fili don gina filin saukar jirgin shugaban ƙasa. Umarnin ya biyo bayan buqatar da rundunar sojin saman Nijeriya ta gabatar. Da ya ke magana ta bakin Daraktan, Mukhtar Galadima yayin wani taron al’umma da ’yan ƙasa a ranar Talata a Abuja, Ministan ya yi nuni da cewa, ya zama wajibi al’umma su ba da damar cigaba. A cewarsa, “Kimanin wata guda da ya gabata ne…
Read More
Kasafin 2024: Ba a ware wa ƙidayar 2024 ko sisi ba, inji Majalisar Dattawa

Kasafin 2024: Ba a ware wa ƙidayar 2024 ko sisi ba, inji Majalisar Dattawa

Daga MAHDI M. MUHAMMAD ’Yan kwamitin Majalisar Dattawa kan kasafin kuɗi sun kaɗu a ranar Talata bayan da aka sanar da su cewa babu wani tanadi da aka tsara na ƙidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2024 a cikin ƙudirin kasafin kuɗin hukumar ƙidaya ta ƙasa. Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da yawan al’umma ta ƙasa Sanata Abdul Ningi (PDP Bauchi ta tsakiya) ne ya sanar da ’yan majalisar halin da ake ciki a lokacin da yake gabatar da rahoton kasafin kuɗin NPC na 2024 ga kwamitin tattara bayanai. Ya shaida wa kwamitin cewa idan ba a samar…
Read More
Kotu ta haramta wa tsohuwar minista riƙe muƙami

Kotu ta haramta wa tsohuwar minista riƙe muƙami

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Wata babbar kotu a Babban Birnin Tarayya Abuja, a ranar Litinin, ta yanke hukuncin haramta wa tsohuwar ministar harkokin mata, Dame Tallen riƙe duk wani muƙamin gwamnati a cikin ƙara mai lamba CV/816/2016. Don haka, Kotun ta bayyana cewa furucin Tallen ya saɓa wa Kundin Tsarin Mulki, rashin ɗa'a ne, rashin kunya, kiraye-kirayen ƙin bin hukuncin kotun, don haka ta raina babbar kotun tarayya ta Nijeriya. Kotun ta kuma bayar da umarnin da ke hana tsohuwar ministar riƙe duk wani muƙami a Nijeriya, sai dai idan ta wanke kanta daga halin da ake ciki ta hanyar…
Read More
Ƙungiyar ‘yan jarida ta karrama Shekh Rigi-rigi Kusfa

Ƙungiyar ‘yan jarida ta karrama Shekh Rigi-rigi Kusfa

Daga ISA GIDAN BAKKO a Zaria A makon jiya ne Kungiyar Mawallafa Jaridu ta Arewa 'AREWA PUBLISHEUM' ta karrama fitaccen malamin addinin Musuluncin da ke Zariya mai suna Malam Usman Bini Shekh Idris Kusfa, saboda jajircewarsa wajen ilmantar da al'umma ilimin addinin Musulunci a ciki da kuma wasu kasashe da ke makotaka da Nijeriya. Taron karrama fitaccen malamin ya gudana ne a Zawiyyarsa da ke Unguwar Kusfa a Birnin da kuma ya sami halartar muridansa da kuma wasu fitattun malamai da suke Zariya. Dokta Sani Garba shi ne mataimakin shugaban kungiyar da ya jagoranci karrama wannan malami, ya ce kungiyarsu…
Read More
Rahoton Tattalin Arzikin Afirka na 2023 ya nuna buƙatar gyaran fuska a nahiyar don samun ci gaba mai ɗorewa

Rahoton Tattalin Arzikin Afirka na 2023 ya nuna buƙatar gyaran fuska a nahiyar don samun ci gaba mai ɗorewa

Rahoton Tattalin Arziki na Afirka 2023 (ERA 2023) ya bayyana cewa, akwai buƙatar yin ƙwarya-ƙwaryan gyaran fuska domin samun ci gaba mai ɗorewa da kuma jajircewa don cimma nasarar da ake fatan gani. Har ila yau, rahoton ya ce: "Manufofin masana'antun da suka bunƙasa na buƙatar mayar da hankali ga sassan biyu da kuma samun daidaitattun abubuwa na yau da kullum. Sannan yana da mahimmanci ƙasashen yankin su gano ingantattun hanyoyin haɗin kai da dabarun aiwatar da manufofin ci gaba don haɓaka harkokin masana'antu." Rahoton mai taken: “Gina gurbin Afirka da ya dace wajen bunkasa tattalin arzikin duniya”, wanda Darakta…
Read More
Gwamnatin Zamfara ta ƙwato motoci 50 daga hannun Matawalle

Gwamnatin Zamfara ta ƙwato motoci 50 daga hannun Matawalle

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Gwamnatin Jihar Zamfara ta ce, ta kwato motoci kusan 50 mallakin gwamnatin jiha da ake zargin tsohon gwamnan jihar, Bello Matawalle ya tafi da su. Da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Gusau, Sani Sambo, mai magana da yawun gwamna Dauda Lawal ya ce matakin ya biyo bayan hukuncin da wata babbar kotun tarayya da ke Sokoto ta yanke a ranar Juma’ar da ta gabata. Ya qara da cewa, an bi tsarin da ya dace domin kwato motocin daga gidajen Gusau da Maradun na tsohon gwamnan wanda a baya ya musanta cewa ya mallaki…
Read More
Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 9,000 daga 13,000 sun faɗi jarrabawar ƙarin girma

Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya 9,000 daga 13,000 sun faɗi jarrabawar ƙarin girma

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Aƙalla ma’aikatan gwamnati 9,000 da suka zana jarrabawar ƙarin girman ma’aikatan Gwamnatin Tarayya na shekarar 2022 sun faɗi. An samu wannan adadi ne daga Hukumar Ɗa’ar Ma’aikata ta Tarayya.An ce aƙalla ma’aikatan gwamnati 13,000 ne suka zana jarrabawar ta shekarar 2022, wadda aka gudanar a kusan cibiyoyin gwajin kwamfuta 69. An zaɓo ma'aikatan ne daga manyan ma’aikatan gwamnati, ’yan sandan Nijeriya, da sauran jami’an soji da sauran hukumomin tsaro. Wasiƙar mai ɗauke da jerin sunayen ma’aikatan da suka yi nasara ta kasance a ranar 30 ga Nuwamba, 2023 kuma an aiko ta daga Hukumar Kula da…
Read More