Rahoto

Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Waliyyan ango sun nemi a mayar musu da sadaki don su maida inda aka aro

Daga AISHA ASAS  Idan ba ka mutu ba, aka ce komai kana gani. Wani sabon salo, wai Bature da feƙe. A ranar Larabar da ta gabata a Jihar Sakkwato a wata unguwa da ake kira Zoramawa aka yi taro na ji da gani da ƙudirin neman auren wata yarinya da saurayinta da suka jima su na yin soyayya.  Taron da ya ɗauki ilahirin dangin yarinyar lokaci wajen shiri na  kwalliya da kuma kayan abincin da aka shirya don tarbon dangin ango, waɗanda suka haɗa da lafiyayyun kaji da makusantan uwar amarya suka tabbatar kowacce ɗaya daga ciki an siye ta…
Read More
UNESCO ta yi bikin ‘Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yaɗa Bayanai Ta Duniya’ a Abuja

UNESCO ta yi bikin ‘Ranar Amfani Da Kafofin Watsa Labarai Da Yaɗa Bayanai Ta Duniya’ a Abuja

Darakta Janar na Hukumar Bunƙasa Ilimi da Al’adu ta Duniya (UNESCO), Ms. Audrey Azoulay, ta ce a shekarar 2023, kashi 60% na al'ummar duniya mai jimlar mutane biliyan 4.75, sun rungumi amfani da shafukan sada zumunta wajen bayyana abubuwan da suka shafe su da neman amsoshin tambayoyi da sauran mu’amala. Ms. Audrey, wanda Darakta na Hukumar UNESCO ta Nijeriya, Mista Diallo Abdourahamane, ya wakilta, ta bayyana hakan a yayin bikin Ranar Amfani da Kafofin Yada Labarai da Yaɗa Bayanai ta bana, ranar Laraba, a Abuja. Ta yi bayani a kan alfanun hanyoyin sadarwa na zamani da kuma ƙalubalen da suke…
Read More
Shirin Bunƙasa Ilimi a Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida ta bi gida-gida ta kwashi ɗalibai 1001 zuwa karatu ƙasashen waje

Shirin Bunƙasa Ilimi a Kano: Yadda Gwamnatin Abba Gida-gida ta bi gida-gida ta kwashi ɗalibai 1001 zuwa karatu ƙasashen waje

Daga WAKILINMU A ƙoƙarin ta ta ɗabbaƙa darajar ilmi, Gwamnatin Jihar Kano ta zaɓi ɗalibai 1001 da ta fara ɗaukar nauyin karatun na digiri na biyu a ƙasashen waje. Premium Times Hausa ta ruwaito cewa, yayin da wasu za su yi na su karatun a Indiya, wasu kuma a Uganda za su yi na su kwasa-kwasan daban-daban. Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda ya rage kuɗin rajistar shiga jami'a da na zangon karatu da kashi 50 bisa 100 a kwanan baya, ya ƙaddamar da Shirin Bada Tallafin Karatu Ƙasashen Waje, wanda aka fara ranar Alhamis da jigilar ɗalibai 550 daga Kano.…
Read More
Matasa sun gudanar da zanga-zanga kan rashin wutar lantarki A Kebbi 

Matasa sun gudanar da zanga-zanga kan rashin wutar lantarki A Kebbi 

Daga JAMIL GULMA a Kebbi  Ranar Litinin ɗin da ta gabata wata ƙungiya mai rajin kare mutuncin al'ummar yankin Kamba da kewaye mai suna Concerned Citizen a garin Kamba dake jihar Kebbi ta gudanar da zanga-zangar lumana ta nuna ƙin jinin hukumar samar da wutar lantarki ta KAEDCO kan saɓa yarjejeniya da suka yi. Malam Musa Kamba ya bayyana wa jaridar Blueprint Manhaja da cewa zanga-zangar ta lumana ta biyo bayan saɓa yarjejeniya da suka yi tsakaninsu da ofishin Hukumar samar da wutar lantarki ta KAEDCO da ke kulawa da wannan yankin na cewa a kullum za su ba garin…
Read More
Abinda ya sa ba zan binciki gwamnatin Masari ba – Raɗɗa

Abinda ya sa ba zan binciki gwamnatin Masari ba – Raɗɗa

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Raɗɗa, ya ce, ba zai binciki gwamnatin tsohon gwamnan jihar da ya gada, Alhaji Aminu Masari, ba, saboda shi ma yana cikin gwamnati tasa. Malam Raɗɗa ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da sashen Hausa na BBC ranar Alhamis. Ya ce: “Babu wani shiri na bincikar wanda ya gabace ni. Kuma ina da dalilai guda biyu na faɗar haka. “Na farko ina cikin waɗanda suka kafa gwamnatin Aminu Bello Masari. Don haka ba ku tsammanin zan binciki gwamnati, wacce nake cikinta. “Kuma ko da ma…
Read More
Malamin Musulunci ya kwaɗaitar da attajirai falalar taimaka wa marayu

Malamin Musulunci ya kwaɗaitar da attajirai falalar taimaka wa marayu

Daga MOH'D BELLO HABIB a Zariya Wani malamin addinin Islama dake Zariya, Malam Umar Magaji ya buƙaci attajirai da 'yan siyasa da su taimaka wa marayu da zawarawa da miskinai da faƙara'u da masu buƙata ta musamman da abinda za su ci. Malamin ya yi wannan kiran ne lokacin da yake zantawa da wakilin Manhaja a Zariya kan halin ƙunci da mutanen ƙasar nan musamman masu ƙaramin ƙarfi suke ciki. Ya ce tabbas talakawa na cikin ƙuncin rayuwa saboda tsadar kayan abinci da dukkan kayan masarufi da kuma matsin tattalin arziki.  Malam Umar ya ce yakamata attajirai da 'yan siyasa…
Read More
Majalisar Ɗinkin Duniya za ta samar da sabon tsarin zaman lafiya a Kaduna da Katsina

Majalisar Ɗinkin Duniya za ta samar da sabon tsarin zaman lafiya a Kaduna da Katsina

Sakatare Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, Antonio Gutteres ya ɗauki nauyin samar da wani tsari mai suna "Ƙarfafa Zaman Lafiya a Kananan Hukumomi da Jihohin Katsina da Kaduna da ke Arewa maso Yammacin Nijeriya". Yankin Arewa maso Yamma, musamman Jihohin Kaduna da Katsina, na fama da matsalolin da suka shafi rikicin manoma da makiyaya da rikicin ƙabilanci da ta’addanci da sauransu. Domin samun nasarar tsarin, an gudanar da wani taro na musamman a ofishin Majalisar Ɗinkin Duniya da ke Abuja, ranar Alhamis, don neman goyon baya da tabbatar da zaman lafiya da yaki da ‘yan bindiga musamman a Jihohin Kaduna…
Read More
An ɗauki tubabbun ’yan daba aikin ɗan sanda a Kano

An ɗauki tubabbun ’yan daba aikin ɗan sanda a Kano

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rundunar ’Yan Sandan Nijeriya, reshen Jihar Kano ta ƙaddamar da tubabbun 'yan daba 50 waɗanda ta ɗauka aikin ɗan sanda a jihar bayan kammala horo na wata biyu. Wata sanarwa daga kakakin rundunar, Abdullahi Kiyawa, ta ce an zaɓo mutanen ne daga ƙananan hukumomin Municipal, da Dala, da Ungoggo, da Gwale, da Fagge, inda aka ɗauki mutum 10 kowaccensu. Da yake jawabi ranar Litinin a birnin Kano, Kwamishinan 'Yan Sanda Mohammed Usaini Gumel ya ce 'yan daba 222 ne suka tuba tare da miƙa makamansu a birnin. Birnin Kano ya fuskanci hauhawar faɗan daba da kuma…
Read More
Yadda rikicin Isra’ila da Falastinawa ya samu asali a tarihi

Yadda rikicin Isra’ila da Falastinawa ya samu asali a tarihi

Daga MAHDI M. MUHAMMAD Rikici tsakanin Isra'ila da Falastinu ya na da dogon tarihi, amma za mu ɗauko shi daga ƙarni na 19 a lokacin da Yahudawa bisa jagoranci wani ɗan jarida Bayahude ɗan asalin ƙasar Sweeden mai suna Theodore Herzl, suka shirya wani muhimman taron a birnin Bale na ƙasar Sweezerland, wanda sakamakon shi suka ƙirƙiro abinda suka kira 'Sionisme', wato ƙungiyar ƙwatar 'yanci Yahudawa da kuma komawarsu a tsaunin Sion, wanda suka ce nan ne ƙasar ta asali. Sun ƙaddamar da wannan shiri dalili da azabar da kuma wariyar da Yahudawan su ka ce su na fama da…
Read More
Ranar Yaƙi da Talauci ta Duniya: Sama da mutum biliyan ɗaya na fama da talauci – Sakataren MƊD

Ranar Yaƙi da Talauci ta Duniya: Sama da mutum biliyan ɗaya na fama da talauci – Sakataren MƊD

Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, MƊD, Antonio Gutteres, a cikin jawabinsa na ranar kawar da talauci ta duniya, ya yi iƙirarin cewa, a wannan duniyar tamu mai cike da ɗimbin arziki, bai kamata Talauci ya yi ma ta katutu ba. Gutteres ya ce, duk da ɗimbin arzikin cikin duniyarmu amma kusan mutane miliyan 700 ke fama da ƙalubalen rayuwa, inda suke rayuwa a ƙasa da dala 2.15 daidai da naira N2,000 a duk rana. Sama da mutane biliyan ɗaya ne ke fama da matsananciyar rayuwa daga ƙarancin abinci, ruwa, lafiya da ilimi. Akwai biliyoyin mutane da ba su da tsaftataccen…
Read More