Babban Labari

Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Za a fara allurar rigakafin korona a Nijeriya cikin Maris

Daga AISHA ASAS, Abuja Gwamnatin Tarayya ta ce, ana sa ran a soma allurar rigakafin cutar korona ya zuwa karshen Maris ko Afrilun 2021.Ministan Lafiya, Osagie Ehanire ne ya bayyana haka sa'ilin da Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da COVID-19 (PTF) ke gabatar da bayanin ayyukankasa, Litinin da ta gabata a Abuja. Ehanire ya ce, "Adadin maganin da Nijeriya ta yi odar sa ta AVATT na Hukumar Hada Kan Afirka, ya danganci daidai adadin da ake bukata ne don gundun barna." Ya ci gaba da cewa, Nijeriya na yin dukkan maiyiwuwa don tabbatar da an yi wa akalla kashi 70…
Read More
Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Cutar korona: NOA ta bukaci ‘yan Nijeriya su ba da hadin kai game da allurar riga-kafin korona

Daga FATUHU MUSTAPHA Hukumar Wayar da Kan 'Yan Kasa ta yi kira ga 'yan Nijeriya da su daina yarda da ra'ayoyi mara tushe da ake yadawa dangane da allurar riga-kafin cutar korona kan cewa maganin na tattare da wasu illoli.  Babban Daraktan hukumar, Garba Abari ne ya yi wannan kira a lokacin bayanin kore zargin da wasu ke yi cewa ana so a yi amfani da allurar ne wajen takaita yawan al'umma, lamarin da Abari ya ce ba gaskiya ba ne. Yana mai cewa, "Babu wata allurar riga-kafin da za a bari a shigo da ita Nijeriya ko a yi…
Read More
Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shari’ar El-Zakzaky zuwa 8 ga Maris

Kotu ta dage shri'ar El-Zakzaky zuwa 8 ga watan Maris Daga AISHA ASAS A Talatar da ta gabata babbar Kotun Jihar Kaduna da ke shari'ar jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya Ibrahim El-Zakzaky da matarsa  Zeenat, ta dage ci gaba da shari'ar ya zuwa ranar 8 da 9 ga watan Maris mai zuwa. Kotun ta dage shari'ar ne biyo bayan hukuncin da Alkali Gideon Kurada ya yanke dangane da neman kotu ta ba shi lokaci da lauyan El-Zakzaky Mr Femi Falana ya yi a bisa wakilcin Mr Eddie Inegedu, domin ba shi damar nazarin wani bidiyo da wasu shaidu biyu suka…
Read More
Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Tsaro: Shugaba Buhari ya nada sabbin hafsoshi

Daga Umar Gombe Bayanan da jaridar Manhaja ta samu daga Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, sun nuna Shugaba Muhammadu Buhari ya nada sabbin hafsoshin sojin Nijeriya. Wadanda nadin ya shafa su ne; Major General Leo Irabor a matsayin babban hafsan tsaron kasa da Maj. Gen. I Attairu a matsayin babban hafsan sojojin kasa, sai A Z Gambo a matsayin babban hafsan sojojin ruwa da kuma AVM IO Alao a msatsayin babban hafsan sojojin Sama. Kafin wannan lokaci, 'yan Nijeriya da dama sun yi ta bayyana ra'ayoyinsu kan bukatar da ke akwai na yi wa shugabannin sojoji garambawul don inganta…
Read More
“Filayen Nijeriya mallakar jihohi ne ba na Fulani ba” – Sanata Jibrin

“Filayen Nijeriya mallakar jihohi ne ba na Fulani ba” – Sanata Jibrin

Daga Fatuhu Mustapha An yi kira ga al'umar Fulani a fadin Nijeriya da su rungumi zaman lafiya da sauran kabilu tare da bai wa gwamnatocin jihohi hadin kai wajen yaki da ta'addanci. Sarkin Fulanin jihar Nasarawa kuma jigo a jam'iyyar PDP, Sanata Walid Jibrin ne ya yi wannan kira a wata sanarwa da ya fitar yau Talata. Jaridar Manhaja ta ruwaito Sanata Jibrin na cewa, "Ba na tare da duk wanda ke ra'ayin Fulani ne ke da mallakar filayen Nijeriya. Jihohi su ke da mallakar filaye." Sarkin Fulanin ya yi kira ga 'yan Nijeriya, musamman gwamnoin Ondo da Oyo da…
Read More
COVID-19: Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin saukaka dokar kulle

COVID-19: Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin saukaka dokar kulle

Daga jaridar Manjaha Gwamnatin Tarayya ta sanar da saukaka dokar kulle a karo na uku, inda ta kara wa'adin dokar da wata guda. Kwamitin Shugaban Kasa Kan Yaki da Cutar Korona (PTF) ne ya bayyana haka a Litinin da ta gabata a Abuja, yayin da yake gabatar da rahoton ayyukansa na mako-mako kamar yadda ya saba. Da yake jawabi, shugaban kwamitin Boss Mustapha ya ce, "PTF na nan na kokarin inganta sha'anin tafiye-tafiye zuwa ketare domin takaita kalubalen da matafiya kan fuskanta. “Haka nan, kwamitin na nazarin matakan sassauta dokar kulle karo na uku kasancewar wa'adin dokar da aka sanya…
Read More
Rikicin FCC: Kwamishinoni sun ja shugabar hukuma zuwa ICPC

Rikicin FCC: Kwamishinoni sun ja shugabar hukuma zuwa ICPC

Daga jaridar Manhaja Kwamishinoni masu wakiltar jihohi 36 na kasar nan hada da birnin tarayya Abuja, tare da Hukumar Kyautata Da'ar Ma'aikata ta Kasa (FCC) sun rubuta takardar korafi a kan shugabar hukumar FCC Dr. Muheeba Fraida Dankaka zuwa ga Hukumar Yaki da Rashawa da Laifuka Masu Alaka da Rashawa (ICPC) bisa zarginta da yin ba daidai ba da matsayinta. Takardar korafin mai dauke da kwanan wata 18/1/2021 wadda ta sami sa hannun Sir Augustine Wokocha da Abdul Wasiu Bawa-Allah, ta nuna yadda shugabar FCC ta mamaye komai na hukumar sannan ta karbe ayyukan kwamishinonin tana mika wa daraktocinta tare…
Read More
Tsaro: Arewa ta na kan bom, cewar Bafarawa

Tsaro: Arewa ta na kan bom, cewar Bafarawa

Daya daga cikin dattijan Arewa da suke kwana suna tashi cikin tunanin yadda za a shawo kan al’amarin shi ne tsohon Gwamnan Jihar  Sokoto, kuma tsohon xan takarar zama shugaban qasa, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa (Garkuwan Sokoto), wanda har qasida ya tava gabatarwa ga takwarorin sa manyan yankin kan yadda za a yi a tunkari matsalolin Arewa. Editocin jaridar Manhaja sun samu damar zantawa da shi domin ya yi mana qarin bayani kan yadda yake ganin za a tubnkari matsalar. A yayin hirar, Bafarawa ya bayyana dalilan da suka sa ya jagoranci tattara alqaluman asarar da aka yi wa arewacin…
Read More
Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin kisa ga Maryam Sanda

Kotun Daukaka Kara ta tabbatar da hukuncin kisa ga Maryam Sanda

Daga Umar Mohammed Gombe Kotun daukaka kara da ke zama a Abuja ta tabbatar da hukuncin kisan da aka yanke wa Maryam Sanda a kan kisan mijinta Bilyaminu Mohammed Bello da ta yi. A wani zama da kotun ta yi na mutum uku karkashin jagorancin Jastis Stephen Adah, a yau Juma'a da yamma, akan hukuncin da ta yanke, ya yi watsi da daukaka karar da Maryam Sanda ta shigar gaban kotun bisa rashin cancanta. A farkon wannan shekarar idan za a tuna, Mai Shari'a Yusuf Halliru na Babbar Kotu a Abuja da ke Maitama, ya yanke mata hukuncin kisa ta…
Read More