22
Oct
Daga JAMIL GULMA a Kebbi Rahotanni daga Jihar Kebbi na bayyana cewa, ɗalibai 30 da kuma malamai biyu da aka sace daga makarantar Kwalejin Tarayya ta Birnin Yauri sun samu kansu. Kamar yadda wata takarda mai ɗauke da sa hannun Alhaji Yahaya Sarki, Mataimaki na Musamman kan Harkar Yaɗa Labarai ga Gwamna Atiku Bagudu na jihar, ta bayyana cewa, “Yau Alhamis 21 (jiya) ga watan Oktoba, ɗalibai 30 daga makarantar FGC Birnin Yauri sun iso nan babban birnin jiha bayan da aka sako su. Yanzu haka ana cigaba da duba lafiyarsu kafin a sada su da iyayensu. Haka-zalika yanzu haka gwamnati tana…
