09
Oct
Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi kira ga gwamnatin jihar akan ta yi ƙarin matsayin aiki, musamman ga malaman makarantun firamare, domin rabon da a yi musu an daɗe. Shugaban ƙungiyar, Kwamred Abubakar Hambali, shine ya yi kiran a wajen bikin Ranar Malamai ta Duniya da aka gudanar a rufaffen ɗakin wasa na Sani Abacha da ke Ƙofar Mata a Kano ranar Talata. Ya yi nuni da cewa, rabon da a yi wa malaman ƙarin girma tun a shekara ta 2017 lokacin da aka ciyar da malamai 50,000 gaba, inda hakan ya…
