Babban Labari

An nemi a ciyar da malaman firamaren Kano gaba akai-akai

An nemi a ciyar da malaman firamaren Kano gaba akai-akai

Daga IBRAHIM MUHAMMAD a Kano Ƙungiyar Malamai ta Ƙasa reshen Jihar Kano ta yi kira ga gwamnatin jihar akan ta yi ƙarin matsayin aiki, musamman ga malaman makarantun firamare, domin rabon da a yi musu an daɗe. Shugaban ƙungiyar, Kwamred Abubakar Hambali, shine ya yi kiran a wajen bikin Ranar Malamai ta Duniya da aka gudanar a rufaffen ɗakin wasa na Sani Abacha da ke Ƙofar Mata a Kano ranar Talata. Ya yi nuni da cewa, rabon da a yi wa malaman ƙarin girma tun a shekara ta 2017 lokacin da aka ciyar da malamai 50,000 gaba, inda hakan ya…
Read More
Shekaru 61 da ‘yancin kan Nijeriya: Na ji daɗin tuƙa Sardauna – inji direbansa, Aliyu Shehu Maradun

Shekaru 61 da ‘yancin kan Nijeriya: Na ji daɗin tuƙa Sardauna – inji direbansa, Aliyu Shehu Maradun

Daga IBRAHEEM HAMZA MUHAMMAD Alhaji Aliyu Shehu Maradun ɗan uwa kuma direban Marigayi Alhaji Ahmadu Bello (Sardaunan Sokoto), ya zanta da Manhaja dangane da gwagwarmayar neman 'yancin kan Nijeriya. Alhaji Aliyu Shehu Maradun yana daga cikin Direbobin Sardauna kuma shi ma jinin Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodio ne. Amma sunan mahaifinsa shi ne Ahmadu Marafa Makwashe ya yi hakimcin Maradun tsohuwa. Don hake me yake yin amfani da sunn mariƙinsa, kuma kawunsa. Ya yi makaranta a Maradun da kuma Ƙwatarkwashi. Sarkin Musulmi Abubakar Atiku ne ya tura ɗansa Sarkin ‘Kayan-Maradun Muhammadu Mu’alaidi don ya yi sarkin garin. Sarauta ce mai daraja…
Read More
Don ’yan baya Buhari ke cin bashi, inji Gwamnatin Tarayya

Don ’yan baya Buhari ke cin bashi, inji Gwamnatin Tarayya

*Masu sukar shugaban ba su yi masa adalci ba, cewar Lai Mohammed*Yar’Adua, Obasanjo da Jonathan suka jefa Najeriya a ƙangin basussuka – Kwamitin Majalisa Daga AMINA YUSUF ALI Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kare kanta game da sukar da ta ke fuskanta daga wasu ’yan Nijeriya kan yawan bashin da gwamnatin ke ciyowa a ƙarƙashin jagorancin Shugaba Muhammadu Buhari, musamman ma na baya-bayan nan da Shugaban Ƙasar ya aike wa Majalisar Dokoki ta Ƙasa yana neman sahalewarta, don amso rancen zunzurutun kuɗi Dala Biliyan Hu]u da kuma Yuro Miliyan 710 daga ƙasar waje, gwamnatin tana mai cewa, domin gina ’yan baya…
Read More
Janar Yahaya kan hare-haren cibiyoyin soji: Kwamandoji zan kama da laifin sake kai hari

Janar Yahaya kan hare-haren cibiyoyin soji: Kwamandoji zan kama da laifin sake kai hari

*Rundunar Sojin Saman ta yi amai ta lashe kan harin Jihar Yobe*Lallai za a gudanar da bincike – Gwamna Buni Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Babban Hafsan Sojojin Ƙasa na Nijeriya, Laftanar Janar Faruk Yahaya, a jiya Laraba a Abuja ya sha alwashin cewa, daga yanzu zai kama kwamandoji a dukkan matakai da alhakin kai hare-hare kan cibiyoyin soji da suka haɗa da sansanonin soji, barikai da sauransu. Babban Hafsan Sojojin, wanda ya faɗi haka a yayin rufe taron Manyan Hafsoshin Sojojin da aka yi a Abuja, ya kuma bayyana cewa, halin sanyin jiki da wasu kwamandoji ke nunawa,…
Read More
Harin NDA ya tayar da hazo

Harin NDA ya tayar da hazo

*'Yan bindiga sun kashe da sace jami’an soja a Kaduna*Za a farauto 'yan ta'addar – Makarantar NDA*Ina zargin ’yan cikin gida – Babban Hafsan Tsaro*Ya kamata wannan ya zama silar gamawa da 'yan bindiga – Janar Kuka-sheka*An tsara harin ne don a kunyata Buhari – Garba Shehu*Tsaron Nijeriya ya rikice – ACF*Buhari ya mayar da martani mai zafi*Masu lura da CCTV ba bacci suke ba – Hedikwatar Tsaro Daga MAHDI M. MUHAMMAD a Abuja Abin mamaki da baƙin ciki mai kamar almara ya afku a ranar Talatar da ta gabata a wani harin da 'yan bindiga suka kai a Makarantar…
Read More
APC a 2023: Guguwar siyasa ta soma ruri a Kebbi

APC a 2023: Guguwar siyasa ta soma ruri a Kebbi

Daga JAMIL GULMA a Kebbi Daga dukkan alamu, guguwar babban zaɓen gama-gari ta 2023 ta soma kaɗawa a ilahirin Nijeriya, saboda haka kowane ɗan siyasa, kama daga masu neman muƙaman jam'iyya ya zuwa masu neman a zaɓe su, don su jagoranci ko wakilci a matakai daban-daban sun soma neman hanyoyin samun cimma burinsu. Jihar Kebbi ita ma ba a bar ta a baya ba, inda a can ma jam'iyyar APC mai mulki ta bi sawun sauran jihohin da APC ɗin ke mulki wajen zaƙulo mutanen da za su jagoranci jam'iyyar tun daga matakin mazaɓu, ƙananan hukumomi, jiha zuwa tarayya, inda…
Read More
El-Zakzaky: Aikin gama ya gama, cewar lauya

El-Zakzaky: Aikin gama ya gama, cewar lauya

*Sarƙaƙiyar da ke cikin shari’ar*Za mu ɗaukaka ƙara, inji Gwamnatin Kaduna*Mu diyya za mu nema, cewar ’yan Shi’a*Bulandar da ta sa kotu sakin malamin Daga NASIR S. GWANGWAZO a Abuja An bayyana cewa, hukuncin da Babbar Kotun Jihar Kaduna ta yanke game da shari’ar da aka gudanar kan jagoran ƙungiyar ’yan uwa Musulmi ta IMN, wacce a ke kira da ’yan Shi’a, wato Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, ba za a iya sake ta ba. Don haka aikin gama ya gama. Bayanin hakan ya fito ne daga bakin wani }wararren lauya mazaunin Kano, Barista Nazir Adam, wanda ya ce, bisa la’akari da…
Read More
Ƙarin girma: Hukumar ’Yan Sanda ta yi wancakali da Magu

Ƙarin girma: Hukumar ’Yan Sanda ta yi wancakali da Magu

…Biyo bayan rahoton Ayo Salami, an ciyar da ’yan sanda da dama gaba Daga NASIR S. GWANGWAZO, a Abuja Hukumar Kula da Aikin ’Yan Sanda a Nijeriya (PSC) ta yi wancakali da batun ƙara wa tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Ta’annatin Kuɗi da Tattalin Arziki ta Ƙasa (EFCC), Ibrahim Magu, biyo bayan rahoton Kwamitin Mai Shari’a Ayo Salami, wanda ya zargi Magun da aikata ba daidai ba a lokacin da ya ke shugabantar hukumar ta EFCC. Kazalika, Hukumar PSC ta yi ƙarin girma ga manyan 'yan sanda guda uku zuwa muƙamin Muƙaddashin Babban Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa (DIGs), yayin…
Read More
Ina sane da halin da ku ke ciki – Buhari ga sojoji

Ina sane da halin da ku ke ciki – Buhari ga sojoji

Daga SANI AHMAD GIWA a Abuja Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari ya bayyana bikin Ranar Sojoji a matsayin wani abin da ke ci gaba da bai wa 'yan ƙasa kyakkyawar fata da ƙwarin gwiwa a hanƙoron su na rayuwa cikin zaman lafiya irin na al'ummar da ke rayuwa ƙarƙashin tsari na dimokraɗiyya. Rundunar Sojin Nijeriya wacce ke da dogon tarihi na shekaru 185 da ta somo daga Turawan mulkin mallaka, ta taka rawa na musamman a yaƙin duniya na farko da na biyu da kuma yaƙin basasar haɗa kan Nijeriya. Shugaba Buhari wanda Ministan Tsaro Bashir Magashi ya wakilce shi, ya…
Read More
Yadda aka shirya bikin bai wa Sarkin Kano sanda gobe Asabar

Yadda aka shirya bikin bai wa Sarkin Kano sanda gobe Asabar

Daga MUKHTAR YAKUBU a Kano Idan Allah ya kai mu gobe Asabar, 3 ga Yuli, 2021, a ke sa ran za a gudanar da babban taro na bai wa Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, sandar sarauta Sarkin Kano, wadda Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, zai yi. Taron dai kamar yadda iyalan Marigayi Sarkin Kano, Alhaji Ado Bayero, kuma mahaifin sarkin na yanzu, suka sanar, wani muhimmin taro ne da aka shirya shi. Don haka ne ma aka fara hidimar bikin tun daga jiya Alhamis da shirya taro lakca, wanda haɗin gwiwa ne tsakanin Masarautar da Jami'ar…
Read More